Author : Zainab Idris Makawa Category : Read Hausa Novels
kinsan ta da,kwashe kwashe, wani dan Arne ta samu yake kashe mata kudi haka,
Arne fa inji mama Asabe mai dinki, Amina tace wallahi ke dai,
Niko bayerabe ne musullumi ai ban iya zama da shi balle iyamuri kirsta,
Mama Asabe tace ke ko indai musullumi ne ai ba matsala, tunda Allah bai hana aure a tsakani ba
Amma ace kirsta gaskiya abin baiyi ba,
Amina tai wani irin turo baki tana mai daga kafada da watsar da hannayen ta alamar nuna oho ba ruwan ta,
Mama Asabe tace amma dai Amina nagane zancen ki har da kushi a ciki
Nan gardama ya kaule masu tsakanin ita da mama Asabe
Daidai lokacin da mama tagama hada dinki tana kokarin nikewa tasa a cikin leda ta miko ma maryan, din,
Tamike tana mai ce madu sai anjimar ku, mama tace ku rage min tsarabar Lagos in ankawo maku
Dariya maryam tayi kawai ta ce to mama zan fada mata in naje,
Ganin motar Ya Iliyasu a kofar gida ya tabbatar mata da isowan shi, gari,
Cikin nuna farin ciki da jin dadi ya iso duk daxtasan cewa ba wai wani abu zaizo masu da shi na marmari ba,
Amma dai tana murna Allah yakawo masu shi lafiya
Yana zaune saman kujera rungumay da yaran shi ta shigo dan matsakaicin falon nasu,
Har kasata kai tana mai sannu da zuwa yai yar dariya yace little mummy ance min an aike ki ,
Tai mai anzo lafiya da murnan ta shima a cikin fara,a yake ansa mata,
Iyalin iliyasu sun cewa ko ba komai indai har yana gari suna cikin farin ciki a ko yaushe
Don gidan su yacika da baki masu zuwa da yan bukatun su akai akai,
Kasan cewar zukatan mutane ya mutu yanzu don ba,a maida roko bakin komai ba,
Sai kaga mutum magidanci bai aikin komai sai bin gida,jen masu dan abin hannu ana rokon su, na cefane,
Yau kwansn iliyasu biyu da dawo wagarin don kusan sati guda yake yi idan ya zo garin,
Zaune suke suna hira shida Anty Dije bayan fitan wasu mata yan uwan shi da suka shigo
Wani almajiri ne yai, sallama a kofar gida ya ce ana kiran Assalam wai a waje ,
Daga Anty Dije har mai gidan ta, saida suka kara tambaya cikin mamaki,
Maryan wace ke kitchen tana kokarin gyara kitchen din
Zuwa tayi tadan leka don taga kowaye ya aiko kiran Assalam haka,
Tsaye suke jingine da wata mota mai kamar ruwan kakin soja,
Dan lekawa,tayi kadan daidai yadda basu ganinta tadawo cikin sauri ,
A,kofar shiga falo ta hadu da ya iliyasu, da ke kokarin fita waje don yadiba,
Duk kan su maryam suke kallo don jin ko waye a wajen,
Inda Anty Dije take tsaye ta nufa tace cikin murya kasakasa wanan mutumin ne fa wanda Assalam yake lakewa,
Iliyasu da ke tsaye ke tambayar maryam waye ne a wajen wai,
Murya cikin taushi anty Dije tace wanan abokin jibrin din gidan baba bala dana fadama,
Kasancewa duk wani abu mai muhinmanci sai anty ta fadawa mijn ta don gudun zargi,
Dan shiru yayi can kuma sai yakama hanyar wajen
Basufi minti koda uku ba sai gasu sun shigo cikin gidan duk kan su,
Shi maigidan shi ne gaba, sai su biyu a bayan shi,,
Ya iliyasu nacewa jibrin nadauka ma ko wani bako ne da naga ka tsaya a waje kana cewa wai akira ma Assalam,
Bayan sun zauna a falo ne suka dan taba hira a tsakanin su inda aka gabatar masu da abinci,
Duk da Joseph baiso cin abincin ba am a saida ya illiyasu yasa shi ci
Sannu sanu daga hiran su yafara sake jiki har zuwa lojacin da Assalam suka dawo daga gidan kakan nin su,
Dagudu Assalam ya fada jikin Joseph yana murna,
Batare da yai magana da kowa ba ya mike tsam rike da hannun Assalam zuwa gurin motar shi waje,
Sai a lokacin Ya Illiyasu yake tambayan jibrin ko waye Joseph din,
Nai yai mai kwatance da mahaifin shi da kuma mahaifiyar, shi,
Saidai bai fada mai ko waye Joseph din ba ayanzu
Yadai bashi labarin haduwar su da Assalam har yadda jinin su ya hadu,
Lokaci guda don yace ma ya illiyasu kusan ko yaushe su kayi waya sai yatambaye shi labarin sturbonboy,
Abinda da da mahaifi, duk mai son mutun akace yaso dan shi,
Hakan yasa ya illisu jin dadi har a cikin zuciyar shi,
Ganin su mukayi Assalam da kaya nike nike sun shigo harda keken yara,
Gaba daya muma fito waje muna kallon wanan irin shakuwar
Bayan sun aje kayan ne yaya yagaiyace su cin abin cin dare a gidan shi,
Joseph din yaso ya doje yaki zuwa saboda yana son ya shiga evening services yau,
Amma ba yadda ya iya kawai sai ya amsa gaiyatar yaya din,
Saidai su uku suka zo tare da KB akazo wanan karon,
Abincin hausawa mukayi yau tuwon shinkafa fara da miyar Alaihu da yakuwa, sai yar kabewa da mukasa da busashen kifi,
Mundauka cewa baza suci abincin ba sai gadhi duk an cinye sai kwano kawai,
Duk kan su sunyi mamakin ganin anyi girkin mutanen da a gidan matashi kamar ya iliyasu,
Saboda sanin da sukayi yanzu kiuyya bai bari mata suyi girki mai kama ciki, da dare,
Saidai kawai aima namiji taliya ko indomie da dare ko dafa duka,
Saboda kiuyyuya kawai, don kada a motsa jiki,
Hira sosai sukeyi yan sungama cin abincin kamar sun dade da sabawa da junar su,
Shiko Assalam yana manne a jikin Joseph har yai barci,zuwan wanan lokacin,
Ganin haka ya iliyasu yaba Joseph bakin cewa duk lokacin da yazo kuma yana son ganin Assalam yashigo kawai gurin anty Dije,
Kuma miyar da yace yana so na hausawa yadinga fada mata ai mai, irin da yake so,
Wanan shine silar kara shakuwar yan gidan su Anty Dije da Joseph,
ZEEE MAKAW
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
1⃣1⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Why why mutane suke da gulma haka, may ye aibun taimaka ma KB dayayi da har za,a fada ma Dad din shi,
Wai may yasa mutane basu kaunar suga cigaban yan uwan su ne musan man hausawa,
Don dai yasan cewa wanan maganar daga bakin hausa yafito zuwa kunen mahaifin shi,
Zubur ya mike tsaye daga inda yake daga shi sai dogon wando da singlet a jikin shi,
Gurin window dake facin din titin da ke unguwar su ya nufa,
Fitinlo ne karara suka haske ko ina sai kuma duhun dare da ya gauraye gari lif,
Ya kai wani dan lokaci a gurin tsaye yana kallon sararin samaniya kawai,
Daga karshe bayan yasamu mafita yai wani dan ajiyar zuviya mai nauyi,
Fridge ya bude alcoholic ke ciki kala kala duk sunyi rabar sanyi yadda yake so,
Hannu ya mika da niyar yadauko wani mai berry a ciki,
Caka hannu shi ya tsaya daidai wuyar kwalbar
Muryan Jibrin ne ke mai yawo a kwakwawa duk addinin mu bai yarda da shan giya ba,
Duk wanda ya ganka a lokacin kana cikin maye baya kara kallon ka da dara a idon shi,
Don duk sanda ya gan ka wanan yanayin mayen dayagan ka aciko zai fado mai zuciyar shi
Kaga kimar ka da mutuncin ka yazube a idon shi,
Idan kuma ka samu iyali za,a dinga goranta masu cewa uban su dan giya ne, ai,
Cikin sauri kamar wanda akai ma tsawa ya dauke hannun shi saman kwalban,
Marfin fridge din ya buga da karfi kamar zai balla ,shi,
Da karfi ya fada kan gadon ta baya yana mai rike goshin shi da hannayen ,,
A haka wani irin barci mai nauyi ya kwashe shi bai farka ba sai misalin karfe tara saura na safe ,
Dan hasken ranar da hudu ta cikin labulen window dakin ya haska mai idon shi,,,
Mika yayi ya gyara kwanciyar shi don ya cigaba da barci amma sai kuma ya kasa ci gaba da barcin,
Mikewa yayi yashiga bayi yai wanka bayan fitowan wanshi ya na daure da towel
Yazo bakin gado ya rusun na kan shi saman gado
Nan yafara jero addua, our father whose as at heaven ,
Hello be there name,,,,,,,,,,,,,
Bai tsaya ba saida yakai karshen addu,an shi kamar kullun yadda ya saba yi duk safe kafin yafita,
Saida ya kintsa tsab ya sauko inda yasamu break fast din shi an shirya mai komai tsab
Jin gidan shiru yasa shi daga murya yana kiran Uchee, da karfi,
Uchee da ke can yana gyara cikin gida yazo cikin ladabi,
Cikin muryan nan tashi mai nuna sanyin hali a koda yaushe yace ma Ucheen ya na duk bear dake cikin gidan shi a kwashe su a zubar da su,
Jin maganar Ucheen yayi kamar a mafarki cikin sauri yadago kanshi ya kai wa ogan kallo,
Joseph da kanshi ke duke yana dan kada ruwan zafin da ya zuba a cup,
Batare da ya daga kai ya kalli Uchee ba yace
Yes I Mean it,,,,
Uchee zuciyar shi fam da farin ciki yasamu gara basa, yau,
Duk yawan giyar gidan oga a ce wai ya kwashe ya zubar,
Ba bata lokaci ya kwaso su jiki na rawa yafita dasu gidan,,
Saidai a kasan zuciyan shi yana mamakin ko may yasa ogan nashi ya ce ya fita mai da su gaba daya,,
KB ne ya kira Joseph din wanda duk yinin yau bai fita ko ina ba yana zaune a cikin gidan shi da ke cikin birnin Lagos,,,
Cikin kasala yadauki wayar don bai son yin wani dogon motsi yau,
Hello, KB ya kake ne yau ya, Abuja,?
Yace a lokaci guda sai KB ya amsa mai da cewa lafiya kalau gashi ma zai tafi suleja dibo wasu motocin da suka samu matsala,
Kuma suna dauke da mai a cikin su,
Duk da Joseph din yai kokari wurin bashi amsa sama sama,
Hakan bai hana KB gane cewa Joseph din yana cikin wani irin yanayi yau din,
What's wrong with u, today,,,?
KB ke tambayar shi a karshen maganar su da Joseph din,
Nothing ma,,
Inji Joseph din yaba KB amsa a takaice, kawai, daga haka suka kashe wayan,
KB din ne yadan shiga tunane don saboda dan zaman da sukayi da Joseph yakai kowa na iya gane mood din wanin su,,,
Duk abinda KB keyi hankalin shi na gurin Joseph don shi a zaton shi ko baida lafiya ne
Don yasan cewa ciwon Joseph kamae fitina ce ga duk na kusa dashi,
Saboda irin mutanen da basa ciro ne da wuri ranan da duk zasuyi sai duk wanda ke tare da su hankalinshi ya tashi,
A hanyar shi ta komawa cikin garin Abuja yakara kiran wayar Joseph din saidai wanan karon muryan da dan sauki sosai a saman da zu,
Ejoma, yarinya ce matashiya yar kabilar IBO mazauna cikin garin kwantagora,
Tana zaune tare da yayanta da mijin yayanta wa yanda suka kawo ta garin kwantagora da zama,
Tun bayan gama karatun secondary din ta ta shaku da wani yaron hausawa,
Dan cikin gari shakuwar su ta samo asaline ta yawan zuwa sayen abu da Aminu Aliyu ke yawan zuwa yi a,shagon su Ejoma Ibire,
Har takai sun kulla, soyayya da Aminu din batare da kowa yasani ba,
Sai da abokan mijin yayan Ejoma suka gan su tare shine suka fada ma mijin yar nata,
Ranan tasha fada har d a duka agurin yayyen nata so sai hakan bai masu ba saida suka fada ma pastor don yai mata preach
Duk wanan abin bai raba Ejoma da Aminu ba illa ma kara shakuwar da sukayi so sai ,
Har ta kai Aminu yai mata alkawarin cewa zai aureta
Hakan yasa har ta yarda dashi har suka kai ga kara aikata masha,a a tsakanin su hakan yasa Ejoma ta fara bijirewa yayanta da mijin yar nata,
A karshe saiga ciki, shiko Aminu Aliyu yana jin ta ce ciki gare sai yace ai sam bashi yai mata ciki ba,
Duk yadda yayanta suka so a sulhuta maganar sam Aminu yaki yarda da zancen cewa ai cikin sane,
Hankali duk wani IBO dake zaune ya tashi da jin wanan labarin na zance Ejoma ,,
Ganin haka yasa mijin yarta ya koreta gidan nasu yace saidai ta koma can gurin Aminu,
Wayan shi yake kokarin ajewa bayan ya gama waya da wani Abokin shi da ke zaune a janhoriyar Benin republic,
Inda yake kwadaita mai yadda sana,ar motoci da shimkafar kasar wane ke da riba so sai a harkan,,,
Kiran Samuel ce ta hana shi aje wayan dai yai niya,
Inda Samuel ke sheda mai cewa mahaifin su yana fama da ciwon kafa sosai duk kwanakin nan,
Don har takai ko shago da gidan mai bai iya fita yanzun nan,
Hankalin Joseph din ya tashi sosai don yasan yadda yakanyi fama da ciwon kafar na shi
Sanadin ciwon kafar ya samo asaline tun wani hatsari da yasa mu a saman mashin,
Joseph yakira mahaifin nashi inda yake tambayar shi lafiyan jikin nashi
Amma sai Mr Ema din yace mai a meke ,you, no worry my child,
Na small problem ,
I go manager amm,,,
Yasan cewa zai shigo kaduna sati mai zuwa don akwai wani wanda yake son gani a kaduna din,
Hakan yasa bai cewa mahaifin komai, ba,
Musalin biyar na na yamma ya shigo garin kwantagira bayan dan banzan gudun da ya dinga shararawa shi kadai acikin mota,
Tun kwanar shiga gidan su yafara ganin abin hawan su duk ya cika kifar gidan su,
Hankali shi ya tashi matuka daga ganin taron IBO haka,
Hon yayi mai karfi wanda dole suka bude mai get,
Da kyat yasamu inda yadan parker motar shi a can gefen cikin gida,
Tun bai fito daga cikin motan ba ya hango wata yarinya a tsugune gaban elders nasu,
Yana ganin haka ya san cewa wani case sukeyi mai karfi,
A hankali ya fito daga ccikin motar saidai ganin mutane a gidan ya hana shi bude bayan motar don ya fitar da tsaraban da yazo da shi,,,
Tun daga nesa yake jin yadda yarinyar ke gumza ta na ihu da kuka mai ban tausayi,
Tana, mai ba da hakkuri sai kawai yaji wani iri a zuciyar shi
Don komadai may tayi yakamata,su yi considering din ta a mace ce fa,
Ko kallon su baiti ba ya wuce ta gefen su batare da ya tsaya gaishe su yadda ya saba ba,
Wanan ya kalli wanan wancan ya kalli wan can,
Su na mamakin shi don basu san shi da halin rashin mutunci ba,
Samuel wanda ke labe tunda aka fara case din shine ya ke taron dan uwan shi cikin mutunci,
Nan yake washe baki babu ko ga ruwa ya fara labarta ma Joseph cewa
Na, Ejoma Ebere one hausa boy givern bele,,,
D hausa boy now say no b him do amm,
Na yin d elders wan punish har,,,
Y ,she, give her self to musulim boy,
Me ,I know ask u ooo,
Joseph ya ce ma Samuel wanda da har zai ci gaba da zubawa,
Roban ruwa yadauko ma kan shi daga cikin fridge din,
Ganin cewa Samuel baida niyar kawo mai komai
Eanka yafada don ya sauke gajiyar shi,
Daga cikin bayin yakre jin karar motocin su da mashunar su suna watsewa
Saida ya shirya tsab yafito cikin wasu kananan kaya,
Abin mamaki wanan yarinyar Ejoma yagani rakube bayan kujera a falon su, har yanzu tana dan sheshekan kuka,
Sai a lokacin yake gaisawa da mahaifin shi wanda ke zaune ya mike kafar dake mai ciwo saman wani tsohon tebur,
Joseph y u know greet my people,?
Baba me i don't have problem with dem woo,,
Waiting dis girl do here Dad ?
Yace mai zata zauna har asan yadda za,ayi da ita ne,
Don ta je tana bin yaran hausawa ga irin hawalan da wo mata, nan,
Wayan Joseph din ce tai kara a lokacin wanda hakan ne yasa shi samun sararin guda daga fadan baban,
Motar shi ya shiga ya bar gidan nasu don yasan cewa fadan sai ya kawo kan shi a karshe,,,,
Tafiya yake yi kawai don yasan cewa KB bai gari kuma ,
Don haka zuciyar shi ta raya mai cewa yaje wurin little friend kawai ya ganshi,,
Anty