Furen Juji Book Compelet Zainab Makawa

Author :  Zainab Idris Makawa Category :  Read Hausa Novels

Chapter   55 / 84

162K to 165K   out of 251.8K words

addinin Christian,
Da wanan tunanen suka risketa a zaune, duk sallama da maganar da Jibrin kewa maryam hankalin ta ya zurfafa a cikin tunanen wanan matar da taji labarin ta dazun,
Gaba dayan su mamaki yadda yar karamar yarinya take irin wanan zurfafan tunanen da kurciyar ta,
Jibrin ne yasa keys din motar shi kusan fuskan ta ya dan kada mata shi a fuska,
Firgigit tadawo a cikin hankalin ta yayin da ta sauke idon ta a kan su su uku,
Suna tsaye suna mata wani irin kallon mamaki cikin sauri ta dukar da kanta kasa tana mai gaishe su da shigowa a lokacin,
Kara tambayar ta Jibrin din yayi a cikin tsigar wasa,
Ko dai A, A din ta dan masuga take tunane ya kira mata shi,
Murmushi mai kama da harara tai mai tana cewa ai ba sai kakira min shi ba,
An fada ma, ni banda wayan kiran shi ne a guri na,
Ke dai gaskiya barin kira maki shi kawai,
Wani wawan tsuki Yusuf yaja daga bayan Jibrin din yace
Ke Maryam Anty tace zaki fitar muna da kulolin abinci ko ?
Sai a lokacin maryam ta farga da su a tsaye bayan jibrin
Yusuf din wanda tun fara wasan ba,an su yake faman dan,nan wayar shi, kawai,
Irin yadda yai magana ta mayar mai da ansa ita ma,
Ta mike suka shiga fito masu da yawan kololin abincin da a ka dafa masu don jama,an su,
Gaskiya duk sun yaba da irin kalar girkn da anty dije ta tayi ita da sisters din nata,
Maryam ce ta dangware wasu set din plates masu yawa a gaban kololin,
Yusuf wanda ke can daga bayan su don yaki karaso kusa yadaga wayan shi yana kira,
A daidai lokacin da wata daga cikin matan tazo tana mai wani kirari a cikin harshen yaren su,
Sai wata yar boyayyar murmushi yake yi a hankali tankar wanda bai son asan may take cewa,
Matar ta juya da harshe hausan wanda ke da,surkin yare aciki tana mai cewa wasu jibrin,
Wanan da kuna ganin shi a nan,
Shan gerin mu shune manya, manya sosai don de baba nashi bai jauna a gida bane
Da yan junan yazama serki a gerin na su ko,
Kudi masu yawa yafito dasu ya mika mata sai ga sauran matan dake saye da zanin su na IBO
Anyi fanti, fatin sama da kasa sai farar bluewers, da gwagwaro a kai,
Nan suka shiga raira mai wani waka acikin yaren su suna mai yi mai kirari,
Tsatsaye su maryam sukayi suna mai kallon su gwanin ban sha,a wa,
KB da Jibrin su ma suka basu kyautan kudi masu yawan gaske,
Safiya ce ta dan muntsili maryam din tana mai mata nuni da Yusuf din,
Wani irin wawan duka takai ma Safiya din wace ta kauce tana dariya keta,
Caraf sai a idon Yusuf wanda, idon shi yakai gare su tun fara wasan nasu,
Daure fuskan shi yayi yana mai masu wani kallon ku daina haka man,
Duk kan su, suka sun,kuyar da kan su a cikin lokaci guda,cikin jin kunya,
Still, uncle inji Safiya ka bari mu ji kirarin ka mana ko zamu iya muma muyi ma, irin shi,
Duk daure fuskan shi da yayi sai da maganar safiya ta sa shi yin yar murmushin,
Ya dan kada kai yace kai,safiya baki da dama fa,
Dariya ta saka mai tana mai jawo maryam, wai zasuyi wa Yusuf din kirari,
Kanta ta koma sadawa kasa saboda irin kallon da Yusuf ke mata,
Mayar da hankalin shi gurin da kololin abincin suke ya yi
Juyawa kawai maryam tayi zuwa dakin, abin ta batare da takara wani abin ba agurin,
Ko da ya juyo bai ganta a gurin ba ta wutsiyar idon shi, ya dan hango ta, zata shige daki,
Daga cikin daki taji dirin motocin su, sun kwashi kayan abincin zuwa gurin da za ai recipetion,
Wanka maryam tayi bayan shigan ta daki inda ta fito cikin wani Dakkaken dinkin shadda din da yusuf ai,kowa Sadiyar, ce daka karshe kuma yace abar ma,maryam din,,,
Sune Anty Dije ta bayar akai mata wanan dinkin mai wani hannu shara,shara,
Sai lece, da aka darza mai bayan anyi mai aikin wuta, da kuma stone a jikin shi,
Kayan light green, sunyi mugun karban jikin ta takai wani lokaci a gaban miro tana gyara jikin ta tsab,
Itama dai safiya irin shaddan ta sa sai dai gurin dinki ne kawai suka sha banban dana maryam,
Sun kai wani lokaci a cikin daki suna yar hiran su ,saidai muryan mutane da suke ji sama sama a,waje,
Da sauri ta mike zuwa waje don tunawa da tayi cewa Anty fa bata gida suna gurin gyarawa Naimat gidan da zasu zauna,
Zaune yake shi kadai a cikin falon su, ya dan zauna rigingine.
Ya dafe kai da hannu shi guda idon shi a rufe ya lumshe su,
Ganin da tai mai haka yasa ta kudirawa barci yake yi a hankan,
Juyawa tayi da niyar ta koma cikin daki inda suke ta zabga hiran su,
Maryam, yace cikin wata irin nishadaddiyar murya,
Cak ta tsaya don jin mai zaice, mata,
Still bai kalle ta ba hannun shi ya na dafe da kan shi,
Jikin ta taji yai sanyi don irin yadda yai mata,
Kan ka ke ciwo ne yaya ta samu kanta da tambayar shi,
Shiru nadan lokaci tukun kafin ya cire hannun shi yadan kalle ta da idon shi da su ka kada mai sukai jajir kamar yaci kuka,
A hankali ya ce mata may kika gani ne haka ?
Cikin dakewa tace idon ka sunyi ja da yawa uncle,
Kan sa ya girgiza mata, yace babu wani ciwon kai dake damu na maryam,
Illa magana da ke kokarin tarwatsa min zuciya ta,
Maryam bana son in na fadawa mutum gaskiya,yana dauka ta tankar banda daraja agurin mutum,
Baki ta dan murgada mai kadan tace nidai ya Yusuf na dai kusa aure in huta da duk wanan sa idon da kuke min,
Don dai ni banga abin da nake yi ba har kake cewa hakan,
Niyar barin gurin tayi tana kun,ku ni, tana cewa wallahi shi yasa bana son shigowar ku KG sam, saboda takura da sa ido,
Tajuya kawai abinta,
Saidai batai nisa ba ta jiyo muryan shi yana cewa,
To aiko nai maki murna da kika fada min cewa, kina son aure kwanan nan
Don haka zan je in samu baba da Anty in sheda masu, abinda ki ka ce,,
Da sauri ta juyo tana fuskan tar shi batare da wani jin dariri ba ko kunyan shi,
Sai dai, kuma wanan karon kamar bashi ke kwance da zu ba,
Yanzu a zaune ya kyam,kamar ba shi ba, ya na mata wani kallon cikin zaki gane kuren ki,
Ba kunya ta, kama yar hararan shi, tace, ban san may yasa kake yawan samin ido yanzu ba wallahi,
Kawai ta juya ta shige abin ta zuwa inda ta hango Naimat zaune tare da bakin ta,,,
Bayan ta yabi da kallo a daidai lokacin da kiran sadiyar shi ya shigo mai,
Tana mai sheda mai cewa ga ta a kofar gidan Ànty tazo mai buki,
Tashi yayi daga inda yake yadan leka inda yaga maryam tabi,
Tsaye take sina diban waya ita da Naimat da Safiya,
Ganin shi ya leko daga kofan falon yasa su mai da hankali gurin shi banda maryam wace kanta yake duke tana kallon waya,
Sunan ta yakira yace tafita waje ta shigo mai da baki pls,
Lokacin da ta fita, ta samu su Sadiya ne bakin da yake nufi tai bakin ciki sosai don ita tana ganin cewa yai mata rashin mutunci sosai,
Ita Sadiya din bata san kofar shiga gidan bane da zai tura ta taron su,
Kallo guda Sadiya tai wa Maryam sai taji wani irin tsanar yarinyar ya kara shiganta,
Ita dai sam bata ra,ayin wanan yarinyar a rayuwar ta bata san mo may ya sa ba,
Rai a dan bace maryam ta dan tare su inda tai masu iso zuwa cikin gidan,
A falo kamar yadda tabar shi su ka samay shi a zaune hankalin shi kwance,,,,

SEENABU ZEEE MAKAWA
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
6⃣6⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA,

IYAKA, NA,ABBUDU WA,IYAKKA, NAS,TA,INN,,,

Ina mai baku hakkurin rashin jina da bakuyi ba kwana biyu, da fatan zakuyi hakkuri dani dan Allah,

Sanya suke cikin dogayen rigunar shadda mai ruwan powder, wanda dinkin shi ya,kai har kasa kamar yana jan kasa,
Hannun dinkin shara,shara, dashi har ya dan zarta hannun su,
Takalman su masu tsinin duduge, da su da kuma tsawo,
Sai chewing gun dake a bakin su suna taunawa kas,kas, kas,
Duk karan chewing gun din ya damu maryam wace ke gaba tana masu jagora zuwa ciki,
Idon su kem a kanta, yanayin ta da kuma yanayin shigar ta ya sasu yin hassada da ita a cikin zukatan su,
Kayan da ke a jikin ta da nai bayani baya din kin yan Senegal yakarbi jikin ta yai mata dan karen kyau, a jiki,
Yana zaune kamar yadda ta bar shi kafin ta fita,
Sai dai wanan karon waya ce a hannun shi yake yi,
Takon su takalman su da ya cika gidan duk ya ruda ko ina,
Wanda hakan ya jawo hankalin mutanen dake ta wajen tsakar gidan zaune,
Inda suka zubo masu ido caaaa, suko sai wani ran gwada sukeyi abin su
Gurin zama maryam din ta nuna masu saboda samun shi da sukayi yana waya a lokacin,
Fita tayi zuwa dauko tire inda ta jero masu abin sha da cups saman ture din,
Duk wanda da Yusuf ke yi idon shi sometimes suna gittaiyya akan maryam wace ke sintirin taron baki,
A hankali ta dire mazu shi a gaban su inda ya yunkura zuwa dayan kujeran da ke gefen,
A lokacin shi ma yusuf din yai sallama da wanda yake waya dashi din,
A cikkin wani irin kashe murya Sadiya kewa Yusuf din magana ,
Ganin haka yasa maryam yunkurin tashi don barin gurin,
Shigowan Anty Dije tare da sallama sai yan rakiyan da suka raka ta gurin gyaran gidan suka shigo a gajiye,
Yun,kurawa, yayi don ya gyara zaman shi da kyau don gani shigowar su anty gidan,
Kallo daya Anty tai masu kawai sai ta wani dan fuske fuskan ta tankar bata ji dadin ganin su ba,
Su ma dai ba wai sun sake jiki da ita ba ce a irin yadda su ka gan su,
Gaisawa sukayi sama , sama da su anty dije din tankar ba su so ganin ta ba,
Yusuf ne ke gaida anty a cikkin kulawa da girmamawa inda yake ta faman yi masu sannu da zuwa,
Gaba daya hankalin shi, ya baya gurin da anty dije ke mai bayanin yadda aikin nasu ya kaya,
So sai yaji dadin baya nin da Anty Dije ke mai akan irin yadda aikin ya kaya,
Sadiya ce cikin wani irin sallon murya ta ce D, Yusuf din wanda ke, magana da Anty yadan juyo gurin ta kadan,
Maryam ce tsaye a gefe dauke da ruwan leda tana kokarin rarabawa mutane don su biyar ne suka shigo
Cikin wani marairai ce murya take ce mai muna son mu tafi fa,
Anty ce tai magana wanan karon da cewa haba ku dan dakata in baku, abin buki pls,
Maryam ce tace cikin dan sake fuska tun yanzun nan da shigowar ku har zaku tafi,
Sadiya wace tai tankar bata ji ko may maryam din ke fada ba, ta wani share,kawai,
Saida ya gaji don kanshi ya mike tsaye yana mai cewa Anty Dije sai an jima idan yadawo,
Sai anjima ma da kyat sukewa mutane shi ida suka bi bayan Yusuf din,
Su na shiga mota yadan wuce gidan su Anty batare da ya waigo inda Sadiya take zaune ba yace,
Sadiya may wanan yarinyar ta tare maki ki ke wani share ta haka,
Pls bana son irin haka, Sadiya yace a cikin dakewa,
Caraf Sadiya tace Nafa san ko may wanan yarinyar da yar ta muna fuka suke kullawa a kai na,
Da wani irin karfi ya faka motar shi wanda har yasa karan motar yajawo hankalin mutane,
Ita kan ta sadiyar sai da ta ji tsoron wanan karar amma sai kawai ya dake ya wani matse fuskan shi,ya ce,
Kufita min mota, bata motsaba a inda take sai ma ci gaba da taunar chewing gun da tayi,
Wani irin tsawa yadaka mata saida ta firgita wanan karon yace ku fita, min nace,
Yadda su ka ga fuskan shi ya canza tankar na wani katon zaki yasa su jin tsoron shi,
Murya na rawa ka fara cewa, don Allah yayi hakuri ya karasa da su saboda Allah,
Sai da yai kamar ya dukar da kan shi saboda yadda yake ji a zuciyar shi,
Tankar wani zaki da ya kwana bakwai baici komai ba,
Sunan Allah da kawar sadiya ke ta hada su da shi yasa shi tayar da mota ya hau saman titin a hankali,
Sai da suka danyi nisa ya sauke wani irin ajiyar zuciya batare da yakalle ta ba yace,
Sadiya kinyi babban kuskure na ai,banta Ànty Dije da kikayi a gabana
Tun ban aure ki ba kina kokarin rabani da mutanen dake sona da zuciya daya,
Mutane da nake jin su tankar yan uwana na ji,ni wa yan da muka fito ciki daya,
Matar da itace tasa ni gaba a kan ki wai yau itace kike wa, wanan bakar maganar haka,
Cikin rawan murya tace Yusuf don Allah dai kayi hakkuri pls,
Yusuf batare da yai magana ba ya kau da kan shi gefe ya na mai fesar da iskan mai huci da zafi, daga bakin shi,
Bai karasa kofar gidan su ba ya aje ta tana mai magana ya fisgi motar shi ya bar gurin,,,,,,

Kwance take makale da waya a kunen ta daga ita sai wani dan rigar shimi fara mai yar hude, hude,
Zani shaddan da ta sa ne daure a jikin ta sai wani dan yalalon gyale da ta rufe fuskan ta da shi, a lokacin,
NA,IMAT ce zaune daga gyafe tare da Isslam suna kallo a wayar ta.
Ga kuma tv dake cikin falon shima aiki yajeyi a lokacin
Sam maryam bataji shigowar Yusuf ba a lokacin saboda hankalin ta da ke gurin wayar tana kokari karkada kafar ta,
Kamshin turaren shine ya daki hancin ta ida ta bude idon ta dake a lumshe ta sauke su a cikin idon shi,
Saye yake da jallabiya mai ruwan toka, a jikin shi,
Sai yar karamar tasbaha da yake dan ja a hannun shi, a hankali,
Cikin yare Naimat ta ke gaishe she shi inda ya ansa mta da kada kai alamar ansawa,
Muryan maryam yaji tana cewa ai ko ba,a gaiyace, kaba kai nagida ne zaka iya zuwa,,
Kanta ta kwantar saman hannun kujerar da take zaune a kai, tana mai ci gaba da wayan ta,
Sam ta manta cewa yar shimi ce kawai a jikin ta a lokacin,
Kujerar da yake facing din ta ne ya zauna fuska babu walwala, a tare da shi,
Fitowar Anty Dije ne daga cikin daki yasa shi dan sake fuska,
Sun gaisa take cewa, ya komawar baki dazun da suka shigo,,
Sai da ya idar da abinda yake karan tawa ya shafa sanan ya cewa anty dije,
Anty wanan yarinyar taban mamaki so sai wallahi,
Baidai fada mata ko may ye ba don bazai iya yin magana ba a lokacin irin yadda yake ji a ran shi,
Dariya maryam ke yi a lokacin don abin da A,A ya fada mata har tana wani dan kyarkyatawa,
Ido ya zuba mata daga inda yake zaune yana mai jefa mata harara,
Da sauri maryam ta kauda kan ta daga gare shi don irin yadda yai mata,
Kanta na kasa cike da jin nauyin shi don tunawa da tayi cewa,, daga ita sai, yar base a jikin ta,
Ta rasa yadda zata mike zuwa cikin dakin su a lokacin,
Duk da ya fahinci cewa tana son tashi zuwa ciki sai ya kawar da kan shi gefe tankar bai ganta ba ma agurin,
Cikin dabara ta mike zuwa cikin dakin su inda ta karasa yin wayan ta,
Har ya gama hiran shi da anty ya bar gidan maryam bata leko wajen falon ba,,,,

Bayan ta gama komai tana kokarin kwantawa barci ne taji wayan tana kara,
A sanin ta dai sunyi waya dazun sosai da A, A din ta sai kuma dan bankin ta da ya kirata around four na marance,
Hannu ta mika ta jawo wayan ta, zuwa fuskanta don ganin kowa ke kiran ta a wanan lokacin,
Uncle Yusuf,

55 / 84