Furen Juji Book Compelet Zainab Makawa

Author :  Zainab Idris Makawa Category :  Read Hausa Novels

Chapter   58 / 84

171K to 174K   out of 251.8K words

yake, ?
Tsuki Yusuf yayi baiko gama jin bayanin ba ya kashe wayan ,
Komawa yayi bakin gado yazauna ya mai harde hannayen shi a cikin juna,
Maganganun da,wanan guy din yayi a lokacin ne suke dawo mashi a rai,
Abubuwan da yace a gamay da Naimat din a wancan lokacin sune abinda ke mai yawo akai tankar yanzu akayi su,
Mikewa yayi zuwa downstairs dakin da Pipkin ke kwance ya turo a hankali,
Inda ya hango yaron a kwance cikin sleeping dress din shi fare masu dan adon pink colour,
Tsayawa ya yi daga kofan daki kafan shi a harde yana ma yaron wani kallon cikin tausayi,
Yasan dama something wrong zai faru da yaro din shi yasa duk kwanan na yake yawan tunanen al,amarin yaron,
Yadade gurin yana kallon dan yaron dake kwance dunkule a saman gadon shi yana barci,,,,,

Maryam wace ke jin cewa duk duniya ba mai son ta a wanan lokacin saboda babu mai kaunar farin cikin ta ashe,
Ba wanda yafi bata mamaki ga wanan al,amarin kamar Anty Dije wace, taki aiwatar da komai akan zancen,
Don a zaton ta Anty Dije zata iya shawo kan mahaifin ya yi hakkuri da zance hada ta da Yusuf da baba ke kokarin yi,
Idan har suna ganin cewa baba ya zai hada tane da Yusuf don wani ra,ayin kan shi to lalai sunyi kuskure sosai, da yin hakan,
Ita dai sam zuciyar ta yaki amincewa da zance Yusuf din akanta,
Mutumin da tun tsawon sanin shi da tayi babu wani zancen so ko makamanci soyayya a tsakanin su,
Shine yanzu za,a ce wai ta aura a matsayin mijin auren ta,
Yusuf din nada abubuwan da mata da yawa ke so a gurin namiji a rayuwar su,
Amma ita sam wa yan nan abubuwan basu burgeta haka kawai take jin tsanar sa,
Yanzune ma da suke dan sabawa a hankali tarage jin wanan tsanar da take mai,
Wanda tun farko ya samo asaline tun lokacin da yake dan mabiyi addinin Christian,
Tun alokacin take jin batason al,amarin shi a rayuwar ta,
Wasu hawayen ne masu zafi suka kara zo mata wanan karon, bata damu da wai ta goge su ba,daga fuskan ta ba,,
Jin alamar shigowar mutum a dakin baisa maryam wace ke kwance tana sharban kuka, dagowa ba,
Gefen gadon ta samu ta zauna takai wani lokaci ta kurawa kaunar nata ido sosai,
Tawani ramae acikin dan kankanin lokaci, tayi baki ga kukan da tasawa kanta duk ya wani kumbura mata ido,
Duk da farko tausayi take bata yanzun ganin da tai mata yasa ta jin tausayin ta sosai,,,,

SEENABU MAKAWA,
[4/6, 23:06] Anty Lantana: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
6⃣9⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

MA, LLIKI,YU,MMIDEEN,,,,,

BARKAN MU DA JUMMA,A YAN UWA MUSULMAI,,,ALLAH YA SADA MU ALHERIN DAKE A CIKIN WANAN RANAN
ALLAHUMA AMEEN👏


Hannun ta takai a hankali tadafa yar uwan nata dake a kwance tankar wace bata a cikin hankalin ta,
Sautin kukan na, ta ne tasake gaba daya a lokaci guda,,
Jawota Anty Dije tayi zuwa jikin ta itama hawaye takeyi saboda tausayin yar uwar ta,
Murya irin ta mai kuka Anty Dije tace, Maryam ki daina wanan kukan haka kada ki jawa kanki matsala,
Don dai kin san halin baba ko waye, mutun ne wanda bai magana biyu,
Kamar yadda ta fada maki cewa ke din tausayin ki ne yake ji har yasa kika samu fagen mai musu,
Ina son ki kwantar da hankalin ki kin sai dai cewa aure na Allah ne ai,
Kika sani cewa ko wani matsala yazo ya hana ayi auren,
Kamata yayi ki barwa Allah zabi akan al,amari ba wai ki kama butulce mashi ba, irin haka da kike yi,
Maryam sam banso tun farko har ki bari Yusuf yagane cewa ba kya son shi ba, haka,
Shima da ba wai baba ne ya haife shi ba ya daure ya nuna boyewar zuciyar shi,
Don may ke da baba ya haifa zaki kasa daurewa ki nuna biyayyan mahaifin ki,
Sai a lokacin ne maryam ta dago idon ta dake face face da hawaye ta kai kallon ta ga Anty nata,
Anty yakike son in yi da abin da raina baiso Anty ban taba jin cewa ina son uncle da soyayya ba arayuwata, tun farko,
Daukar shi nayi a cikin mu tankar wani dan uwar mu,
Amma Anty taya za, ace wai ni dangin mijina duk kafirai ne,
Da sauri Anty Dije ta dafe mata baki kafin ta karasa zancen ta,
Da cewa Assha maryam kin san abinda yasa Allah yai wanan hadin a tsakanin ku,
Kin sani ko shigar ki cikin su zai kawo sanadiyar musluntar wasun su,
Maryam Yusuf mutum ne wanda ke bukatar mace wace zata ba shi kulawa,
Saboda yana cikin maraicin rashin yan uwa na sahihi a tare da shi,
Yana son mace mai mutunci da sanin ya kama tane bawau irin wa ancan matan da suka laje mai don kwadayin dukiyar shi ba kawai,
Wani irin kallon tuhuma maryam ke aikawa Anty ta don jin wanan maganar da ta,jera a lokaci guda watau ke nan Anty ce ta ke son wanan hadin ko ?
Saboda son Yusuf din da takeyi tan,kar wani jinin ta can,
Wai may yasa Anty Dije take son al,amarin wanan bawan Allah haka ne,?
Muryan Anty ne ke cewa maryam kinfi kowa sanin cewa bawai don abin hannun Yusuf nake ra,ayin shi ba, ko ke da shi,
Tadan girgiza kanta cikin ban tausayi ta ce kawai don kyawawan halaiyan shi ne na alheri,
Wanda tun farko na hango su daga gareshi amma baida mataimaki,
Kanta takawar daga kallon yar nata, a lokacin da taji haka din,
Wani irin bakin ciki ne ya tokare mata zuciyar ta ta rasa yadda,zatayi da,shi,
Komawa tayi da kanta saman filo tana mai kallin silin din dakin a hankali ta lumshe idon ta saboda tuno wasu abubuwa da dama a zuciyar ta da tayi,,,,,

Kusan kwana nawa Yusuf bai kira yan dattijan da suka maye mai gurbin mahaifin shi ba gurin sa ma albarka da fatan gamawa da duniya lafiya,
Mahaifin jibrin ne ya fara kira inda suka gaisa a cikin ladabi da biyayya,
Sun dan kai wani lokaci yana mai bashi hakkuri da duniya, da mutanen cikin ta,
Sai kuma malam Abdulsamad da yakira shima kusan irin yadda sukayi da mahaifin jibrin ne sukayi da shi,
Sai kuma yai niyar kiran mahaifin Anty Dije wanda dattijon ke burge shi saboda irin halaiyar shi na sanin mutuncin mutane,
Da gaisuwa ne suka fara magana da mahaifin na su Anty Dije,
Inda yake mai magana kamar nasiha akoda yaushe,
Anan yake sheda mai cewa ya yi kokari ya shigo ya duba mahaifin shi,
Ya daina dadewa baizo gurin shi ba saboda hakkin mahaifa ya na a kan shi,
Sosai Yusuf yaji dadin wanan nasihan na baba shi yasa shi har kullun yake sun al,amarin wannan tsohon,
Ya kai wani lokaci, azaune gurin da su ka gama waya da mahaifin su anty dije din,
Hannun shi bibiyu ya tallabo haban shi da su yana mai tuna nen yadda zasu kwashe da mahaifin shi,
Murmushi yayi shi kadai don sanin cewa sai sun kwasa da mahaifin nashi,
Wanda har zuwa yanzu bawai ya hakkura da zancen shi bane,
Amma ya zai yi dole ne ya bi zancen dattijon nan don neman albarkan,mahaifa,

Ta gama shirya duk wani abin dazata bukata acikin yar jakar ta mai kama da handbag,
Kaya kala ukune tsab ta tura ciki sai yan abubuwan bukata kamar su, kayan shafawa, irin na mata da unders,
Wani katon hijab fari ta zunduma a jikin ta ta yadda ba mai iya gane cewa ta na dauke da wani abu a jikinta
Tafiyan ta a cikin natsuwa tare da dan jan aji kamar kullun,
Kokai waye ka ganta sai ka kara wai,gawa don ganin ta,
Can hanyar fita gari maimashin ya kai ta don ta tare motar da zai kai ta garin Bobi
Ana Sallah Azahar ta isa garin bobi inda ta samu jama,an gidan nasu mahaifiyar ta lafiya kamar kullun,
Duk sunyi farin cikin a ganin maryam din saboda jimawan da tayi bata zo garin ba,
Mahaifiyar dai kallon ta kawai take yi batare da tace mata komai ba,
Amma dai rayuwan ta ya bata cewa ba tafiyan lafiya yar diyar nata tayo ba,
Su biyune adakin yanzu tana zaune daga gefe ta na kallon yar diyar nata,
Daketa wasa da spoon a cikin abincin da kishiyar ta tasa asayo mata, abakin kasuwa,
Sunan ta, ta, takira har sai,da maryam din ta dan zabura sabboda nisan da tayi a cikn tunane,
Yar baba mai ke tafe dake ne haka a wanan lokacin,
Maimakon tai magana sai kawai tasa kuka kamar zata suke,
Bata cewa yar nata komai ba illa fita da tayi zuwa, dakin kishiyar ta,
Can sai gasu tare su biyu sun shigo dakin,hankali a tashe,sai kallon ta sukeyi,
Da kyat kishiyar ta tasamu Maryam ta tsakaita da kukan nata,,
Nan dai cikin hikima suka samu har maryam din ta dan labarta masu irin abinda ke tafe da ita da ,
Salati suka sa a lokaci guda suna mai, tafa hannyen su don mamaki,
Mahaifiyar ta ce ke cewa yar baba ina maki daukan yarinya mai hankali ashe ke ba haka kike ba sam,
Hankalin ki bai kai ba sam to yanzu mai kikazo gurina in maki,
In goya maki baya ki bijirewa mahaifin ki ko may,?
Kirufawa kan ki asiri tun muna mu biyu ki koma inda kika fito,
Kishiyar mahaifiyar ta ce ta dakatar da mahaifiyar na tada cewa ya isa haka ki bari abi a hankali,
Haba yaya zuwa tayi don ta ja min magana ga dangi, mu kawai ta barna min suna,
Kishiyar mama ce tace barin kira malam ina ga zaifi sauki,
A tare suka,shigo da malam mijin mama wanda fuskan shi kawai zai nuna ma cewa baiji dafin abin da tayi ba,
Maryam wace sai kuka takeyi a lokacin bata iya cewa komai don gaba daya yanzu tagane ba,a son ta kowa sai Yusuf,
Daga karshe dai shawara ya yanke akan cewa ta koma ita kadai batare da,wani ya rakata ba don kada agane cewa guduwa tayi,
Mijin mama yai mata nasiha sosai akan cewa tayi hakkuri da zabin mahaifin ta insha Allah bazata tabe ba,
Maryam tana share hawaye da gefen hannun ta ta mike jiki ba kwari don bin umurnin mahaifan ta,

Anty dije bayan tadawo ne ta laika ko ina bata ga maryam ba ,
Sai abin yabata mamaki saboda sanin cewa maryam dun ba ma,abociyar fita bane duk sanda taga dama,
Har gidan makwabciyar su ta leka da taji shiru amma sai matar tace aiba ta, shigo ba,
Hankali ta yakara tashi sosai amma sai bata kawo komai ba a ran ta,
Don haka tamike da, kan ta don yi masu girkin abin da za suci a ranan,
Har zuwa yamma ba maryam don haka hankalin ta ya kara tashi sosai,
Jin ana kiran sallah magarib ko ina yasa ta kara tsinkewa,
Alwala tayi da niyar yin sallah idan ta idar sai ta shiga gidan su gurin baba, ta sheda mai,
Da sallamar ta tashigo gidan ta wuce dakin ta direct ta kwabe hijab din ta da sauri kamar yadda kishiyar mama ta ce mata tai saurin mayar da kayan ta gurin da suke,
Buta ta sura zuwa gurin alwala, sallah magrib ba, din kada ta makara,
Tana zaune bayan ta idar fa sallah tana lazimi taji shigowar yar nata,
Daga kofa ta tsaya tana mai tambayar ta da cewa ina ta tafi tun da safe, haka,?
School muka,shiga don yin submit din wani takarda, dake a hannun mu,
Amma maryam shine baza ki fada min ba sai ki bari ina yawon neman ki,
Kiyi hakkuri tace kawai sai anty dije ta juya batare da takara cewa komai ba,,,,,

Sosai wanan karon yai shirin shigowa don yasan cewa lokacin tafiyan Alhazai ya yi Insha Allah,
Shigan dare yaiwa garin a lokacin don haka bawai kowa ne yasan da zuwan shi garin ba,,
Gidan mahaifin shi ne ya nufa kamar yadda baba ya bashi shawara,
Zaune Mr Ema yake yana shan hantsi, safe dake karawa,jiki karfi,
Cikin mamaki yake kallon dan nashi ganin irin yadadda ya kara zama big man
Da gani abin duniya akwai su a gurin sun zaunu dam,
Duk irin yadda ya sha cewa zai dake aduk inda suka hadu da yaron nashi ya gwada mai cewa ya fita batun shi sam,
Zaune yake amma Yusuf din yana zuwa yadan rakwafo zuwa jikin mahaifin nashi kadan,
Bayan shi yadan bubuga yana mai baya yana ce mai welcome my Son,
Ba karamin mamaki Yusuf din yaji ba don jin abinda Dad ya ce mai yau,
Yaushe rabon shi da samun haka daga gare shi har ya manta da lokacin gaskiya,
Hamdala yayi azuciyar shi na samun wanan sassaucin da yayi gurin mahaifin nashi,
Bayan sun gaisa ne yakoma mota ya,dauko mai tsaraban da yazo mai da su,
Daga gidan nasu yakama hanyar zuwa gidan anty dije,
Gittawan motar shi da suka gani ne yasa su gane cewa ya shigo gari a lokacin,
Aminu wanda ke tsaye a kofan wani shago ya ji ana cea cewa
Dan iyamurin nan yashigo kenan kwanan nan akwai harka ke nan,
Cikin sauri Aminu din ya juya don yagan shi wani irin yai mai acikin mota yake zaune,
Binshi yayi da kallon mamaki har ya bace mai da gani, don yasan cewa tunkar shi akan a kan yaron nashi zaiyi wuya sosai,,
Gidan Anty ya yaron nashi daniyar zuwa ya karya zancen dan shi yanzu yana da wuya sosaiduk da yasan cewa bawai ansan da zuwan, n shi bane don haka ba,a yi komai dashi ba, sai dai yasan cewa bazai rasa mutumin shi ba ai watau ,kunu,
Duk da safiyane, Wasu Swiss pure cotton ne saye a ajikin ta masu saukin kudi, ne amma sun karbe ta sun kara fitar mata da kyaunta
Kunnun gyada yau suka dama saboda yaran sunce shi suke son sha, wannan lokacin,
Sallamar shi ce yasa yaran kurma wani irin ihun murna, a lokacin, a
Wanda ya jawo hankalin iyayyen nasu gare su, kowan su sai da yai mamakn ganin shi
Maryam wace tafito daga kitchen dauke da cups a hannun ta ganin Yusuf a tsaye tare da yaran yasa ta tai kamar ta koma baya
Sai kuma tadake takaraso tana mai sannu da zuwa,
Sau guda ya dan kalli gefen da take ya kau da kan shi cikin sauri,
Amma sai yaji gaban shi yai wani irin faduwa saboda ganin yadda ta koma takara yi mai wani fes a fuska,



ZEEE. MAKAWA
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
7⃣0⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI

Dan girman Allah ku tayani addu,a pls ina a cikin damuwa, 👏👏👏

IYYA,KA NA, ABBUD,DU WA, I YYAKA NAS,TA,INN,



Kusan maryam ce ta karshe gurin yi mashi sannu da zuwa,
A lokacin tana dauke da cups din kunun yaran guda biyu a hannun ta,
Mikawa ko wani yaro nashi cup din tayi ta juya da niyar komawa kitchen din,
Muryan Yusuf ne wanda ta dade bata ji ba yake cewa,
Maryam da akwai sauran kunnun dan Allah a san min,
Guri guda ta tsaya cak don sauraren a binda yake cewa,
Tana kokarin juyawa ne don ta debo mai, sai, taji muryan Anty Dije a bayan ta tana cewa,
Haba Yusuf azubo maka dai ko badai a san makaba,
Dariya yadan yi mai kama da yake yana cewa to ba, a dama shi da ni ba aikin ga zan rage maku quantity ko?
Zama Anty Dije tayi suka fara gaisawa yayin da maryam ta nufi kitchen kawai,
Tafe take dauke da tire da jug din kunu sai kuma wani giran ruwa mara sanyi da ta azo a sama,
Saboda shi da kan,shi ne yai mata bayanin cewa
Idan mutun yasha kunu mai zafi ko tea baya shan ruwan masu sanyi don gudun kamuw da cancer ciki,
Hakan yasa indai abu mai zafi zata kawo mai sai dai ta dauko ruwan da ba, sa a fridge ba,
A gaban shi ta aje tire din wanda dukawar ta yai daidai da juyowan shi, da sauri ya kau da kan shi gefe guda,
Saboda shakan numfashin juna da sukayi, inda turaren ta yadaki hancin shi,
Itama dai maryam daurewa tayi saboda mayattacen turaren shi mai dafe wa mutun a hanci idan ya shaka,
Duk taji kamahi shi har yabar gari da kusan yan kwanaki zakaji falon gidan su yana wanan kamshin nashi,
Jiki ba lakka ta juya da niya barin

58 / 84