Author : Zainab Idris Makawa Category : Read Hausa Novels
sallama a cikin hausa,
Cire wayar yayi yadaga yana kallo don shi a bin ya bashi mamaki so sai wallahi,
Sai kuma yace kila wrong noba ce,
Karakara wayar yayi a kunen shi don yace is wrong noba,
Saida abin mamaki daidai lokacin da ya kara wayar akunen shi a lokacin ne, yaji mai maganar tana cewa
Yakake Joseph ?
Mamaki karara a fuskan shi ya ansa mata da lafiya,
Wake magana ya ke tambaya cikin mamaki, saida tai yar murmushi har yana jinta daga inda yake
Tace kana magana da Aisha Sanda ce,
Aisha Sanda ?
Joseph ya kara nanata sunan cikin mamaki a fili
Tace mai eh
Wace kuka hadu a wurin dinner din hamza har ka kaini gida,
Ok ok yace nagane ya kuke ta amsa mai da lafiya lau,
Yau nake tambayar KB kai yace min ka wuce sai tadan shake muryan ta kamar mai shirin kuka,
Tace shine bakazo munyi sallama ba katafi, ?
Maganar ta ba shi mamaki sosai don dai ya san cewa bawai wani sanin juna sukayi ba ko sabawa,
Amma sai kawai yadake duk da cikin mamakinta yake , ya ce , mata just sorry,
Kamar ta na ganin shi kai kawai ta gyada mai kamar yana ganin ta a fili,,
Wani irin ajiyar zuciya yayi yana mamakin maganar ta acikin zuciyar shi,,,
Ita ko Aisha wani irin shu,umin murmushi tayi bayan sun aje wayan azuciyar ta tana kiyasta abinda, take planing akai,,,,
Tsaye yake a cikin wani ma,aikatar tatan man petroleum, da ke kudu, yana son idon shi ya tabbatar mai da ko mota nawa daga con n motocin su , suka shigo,
Wayar shi tai kara noba ce ya gani babu suna don haka bai san mai wanan nobar ba,
Yadauka yana mai cewa hello,
Aka ansa mai adayar bangaren, jin muryan mace kuma ba hausa tana cewa
Hello mun wuni lafiya ya kwana biyu ?
Hello wake magana yace
Mamaki ne ya kama Aisha jin cewa har yanzu ashe bata shiga ba,
Ansa mai tayi da cewa Aisha ce daga KG,
Dan shiru ya biyo baya kadan sai can yake ce mata ok nagane
Pls ki bani dan lokaci zan kira ina aiki yanzu pls
Ba matsala race tana mai aje wayar cikin jin takai ci,
Amina wace ke kwance gefen ta har tagama wayar ta numfasa tace wallahi Aisha kina bani mamaki
Cikin dan jingina bayan ta da bangon dakin da suke zaune tace agani ki ko,
Amina tace a ganin kowa ma,
Kin fasan cewa ba musulmi bane wanan guy din don may zaki nace a kan shi dole sai kinyi halak da shi,
Daidai lokacin ta dauko wani abin gyara kumba daga cikin jakar ta,
Tafara dan kankare kumbar hannunta da abin sai can kamar bazatai magana ba tace
Kina nufin don ba musullumi bane bazan yagi rabo na ba ke nan,
Cikin mamaki kawar nata ke kallon ta don Aishan ta ba ta mamaki kwarai ta ya zatai mu,amula da wanda ba musullumi ba,
Gaskiya ita bazata iya ba, iyakar harkan ta ga musulumai yan uwanta,,,
Saboda yawan matsin da take mai dole yafara dan sakin jikin shi da ita har suna dan hira jefi jefi a waya,
Tafe take ciki uniform din su na girls day secondary school, sauri takeyi don ta isa gida, saboda ta samu ta shirya da wuri zuwa islamiya,
Don a kwaita da tsoron bugu bata son abinda ya tabi lafiyan jikin ta sam
Wasu "yan matane mutum biyu cikin shiga ta isa da nuna lokaci ke tafiya,
Tafiyar ta takeyi cikin sauri yasa sukayi kusan yin karo da daya daga cikin yan matan ne tai karfin halin cewa haba malam wani irin tafiya ne kikeyi babu ko tsari balle ki nuna ajin cewa ke ma mace ce,
Maryam wace duk saurin da takeyi bai hana ta tsaya wa guri guda ba cak,,,,
A hankali ta juya inda suke tadan kalle su murya a raunane tana mai cewa kuyi hakuri pls ban san cewa gurin ba zai muna bane,
Daga haka ta juya batare da ta kara cewa uffan bata ci gaba da tafiya sai dai maganar na kona mata zuciya,
Don may zasu ce ita bata da aji kodon batasa bujen da ya manne mata jiki bane, shine rashin wayewar da suke hange a gareta,
ZEEE MAKAW
ZEEE MAKAWA
[🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
ZAINAB IDRIS MAKAWA,
Zaune suke a majalisar su,inda suke hira duk marance ( yamma ) akantitin B C G titin da ya mike zuwa kaduna , minna Abuja tare da,wasu yan kauyu kar dake hanyar,
Duk marance a nan su KB ke yada zangon su, suyi ta hira ko aita shan matar juna a tsakanin su,
Wanan abin ko yaushe yana kara burge Joseph don saman yan yaren su basu da lokacin hakan ,
Ko yaushe ana cikin kasu ko bakin titi gurin bidan kudi,
Yan zun kuma sai dai in har yaso shiga taro saidai ya yaje koda clubs ko kuma wani park ire iren wuraren sheke aya amma ba irin haka ba da hausawa ke yi,
Shiyasa shi har gobe yana sha,awar tarbiyan bahaushe,
Joseph jin shi yakeyi kamar bai da wani harkan komai a gaban shi,
Zuciyar shi na mashi fes a duk lokacin da yake cikin irin wanan yanayin,
Wani matashi mai suna sulaiman ne yazo sama wata mashin rober,rober yanata,washe baki,
Ya sayo sabuwar abin hawa, sai sam barka kowa ke mai a lokacin saboda ya huta da yawo a kasa ko saman kabukabu,
Kowa sai zuwa yakeyi yana duban man shin din cikin kulawa, da yiwa Suleiman fatan alheri,
Joseph dake waya a lokacin kuma yana kallon su sai abin ya daure mai kai so sai
Don saboda mashin kawai da ko gabadayan su zai iya sai masu wanda ma yafi wanan tsada suke ta ma suleiman murna haka,
Sai kawai yaji tausayin su yakara kamashi duk da sunan wai suna aiki gwaunati ke nan amma gashi yar mashin kawai na basu sha,awa,
Jesus crisis yace a zuciyar shi don ba karamin sa,a ya taka ba shi da Allah ya maishe shi haka cikin su,
Don ai a da duk tare suka taso kuma yan zun ne yasamu wanan ci gabar duk da dai basu san ko shi waye ba to amma dai sun san yana da shi,
Muryan Nasir ce tadawo da shi inda yaji Nasir na fadin cewa
Allah yasa ko yar Suzuki yasamu ya saye shima, hakadai duk sukayi ta hira a tsakanin su inda kowa ke fadin albarkacin bakin shi,
Har zuwa goma na dare suka kai agurin suna hira sannan KB yadauke shi sama wata rubaban mashin din shi zuwa gida,
Tun da safe yabar gari ya ko gurin harkokin shi don ci gaban shi,,
Tunda yadawo yadawo da kudin tallafawa mutane da dama aran shi,
Din shi a ganin shi duk wanda kuka wahala tare har Allah yabaka samu daga cikin ku to bai kamata ka manta da yan uwa ba,
Sanar,ar da suka fara shigo da dan yar Gas dama ainihin pure Gas din,
Gani harkan ta karbu yasa shi yin kokarin gani sun gyara system din business din yadda ya kamata,
Shigowa da mai din kasar arewa yasa shi kawo KB daga cikin wa yanda za,aiwa interview din zama members nan gaba,
Waya yai ma KB yace su hadu Abuja next week Wednesday, don su dan tatauna, akai,
KB duk da bai sam komaiba bai yi kasa a gwaiwa ba ya shirya zuwa Abuja din, don ansa kiran da joe ya mashi,,
Cikin lokaci ya samu isa Abuja inda yasamu, har Joseph ya cika mai duk wani form da ya kamata,.
Briefly Joseph yai mai bayani sai gashi kawai, ankira shi don yashi ga ciki duk da bawasu tambayoyi bane masu tsauri amma dai Joseph din yana darrr kada kb ya kasa amsawa duk da baida shakku akan shi, don yasan cewa yana da kokari,,
A cikin ikon Allah KB yai nasaran lashe interview din ,,,a cikin masu yi harda Joseph a cikin su,
Murna da farin ciki a gurin su baa musalintawa, duk da har yanzu bawai KB ya gamsu da kowace irin aiki bane,
Amma dai gani masu taron ya tabbatar mai da ba karamin aiki bane,,
Wanan abin ya jawo ma Joseph surutu acin abokan harkan shi,
Don sai cewa suke yi ya dauk hausa ya sa acikin harkan shi ya bar yan uwan su sun fadi,
Wanan damar a cikin sune ya kamata wani ya samu ba,a cikin northern side ba,
Suko hausawan dake cikin su sun yi mamaki kwarai daganin Joseph ya kawao candidate din shi bahaushe,
Tun a wurin akaba KB sabuwar mota da kuma gida inda zai dinga besing a Abuja
Sai sabuwar office da aka bude masu washegari,
Kabiru gani al,amarin yakeyi kamar a mafarki wai yau shine da wanan abin da bai taba tunane samu ba,
Sai gashi Allah ya bashi cikin dan lokaci guda, don haka bakaramin nasiha Joseph yai mai ba don ya fada mai cewa sai yasa ido ga harkan so sai kuma ya rike gaskiya don akwai bata gari wa yanda zasu iya batasgi cikin dan lokaci,
Don zasu iya hada mai tracks kalakala don kawai ama wani hanya,shi a kore shi,
Kwantagora ta dauki zance kwaaaaa cewa KB yadawo da sabuwar mota, ya samu aiki,
Amma ba,a san kowace irin aiki bane haka da har ya samu wanan cigaban cikin lokaci guda,
Wasu suka fara cewa ai yafara irin harkan Joe ne Joe din ya jefa shu cikin kungiya,
Wanan zancen har ya fada a kunen KB da yan uwan shi,
Inda mahaifin shi yakira yin mitin tare da duk wani dan uwanshi tare dashi KB din,,,,
Anan KB ya fada masu cewa wallahi har ka ce ta sanar man Gas wanda duk wani Gas da zai shigo nan arewa saida sa hannun su a ciki,
Nan dai yai masu bayani har suka fahinta suka kuma yi mashi fatan alheri a harkan,,,
Saodai cikin gari kan wasu sun yarda wasu ko ba su yarda ba har yanzu,,,
Sadiya Mohammad jodi wata sabuwar matashiya ce mai tashen budurci a cikin gari
Tun ranan da taga Joseph tare da su Aisha Allah yasa mata son shi a rai saidai kawai matsalar ta da akace mata ba musullumi bane shi,
Don har ta kasa boyewa a zuciyar ta saida ta samu jibrin tai mai magana akai,
Dayake akwai wasa a tsakanin su yasa Jibrin duk inda ya ganta sai yace mata ta Joseph ita kuma sai tace aa, saidai Yusuf,
Wanan wasa ko yaushe jibrin kewa sadiya, indan sun hadu ita ko bata gajiya da bashi ansa kamar kullun,
Maryam ce zaune tana wanki a bakin famfo gidan su.
Wayan Anty Dije yai kara alamar kira ya shigo mata, a lokacin
Maryam tamike cikin tafiyar ta maikama da rangwada kasan cewa ba wani jiki gareta ba,
Daukar wayan tayi don ganin bakon noba ke kira, cikin yar siririyar murya tace Assalamu Alaikum,
Hello Anty kuna lafiya ya yara da gida,
Wayan ta dan daga ta kalla,sai kuma ta kara manna wayar a kunen ta,
Wake magana ne tace ?
Anty Hadiza nake nema pls aka bada ansa,
Bata nan ta,shiga makwabta yanzu, dan shiru yayi sai kuma yace Assalam na kusa pls,?
Baya nan shima tare suka tafi, ok in tazo ki fada mata Joseph ya bugo mata,
Joseph kuma ? Joseph fa, kai is wrong noba pls
Kada ka kara bugowa nobar matar aure ce pls
Dan murshi yayi har tana iya jin shi, alokacin yace ba nobar maman Assalam bane?
Tsuki tayi tana fadin mukan ina muke da wani arne wai Joseph da zai kira Anty
Daidai lokacin da ta gama fadi ta kashe layin,
Tana ta faman fada wai kawai don suyi magana da matan mutane suke kiran wrong noba,,,
Shiko joseph dake zaune a saman wani leda cushion ya rike wuyan shi da hannu bibiyu ya furzar da iska, daga bakin shi,
In akwai abinda yafi mai munin ji shine ace mai arne, ko kafiri,,,,
Tun yana yaro yai hating din wana kalman a rayuwan shi,
Don in mutane suka ga su jibrin ko kabiru tarrme dashi lokacin sai yaji sun ce baku barin yawo tare da dan kafirai ko ko dan arna ko,
Wani bukin Christmas daya kawo masu abinci kamar yadda su ma suke bashi abinci sai cewa wasu mata sukayi
Ku fita mu na da abincin kafirai a cikin gida kada muyi amai
Wa zai ci abincin arna jagwagwalen banza kawai babu ko tsarki,
Shikuma yadai san cewa duk wani tsabta a lokacin mamanshi tanayi,
Kuma shi har gobe idan ya kewaya yana tsarki kamar yadda ya ga kowa nayi,
Amma sai ake ce mai wai baida tsarki haba mutane ne,????
Anty Dije tana shigowa tare da su Assalam daga makwabta ko daki bata shiga ba,,,
Maryam ke fada mata cikin fada cewa wani kafiri ya bugo mata waya wai sunan shi Joseph nikan nace wrong noba ne
Dan rainin wayo kawai Anty Dije dake tsaye sororo tana kallon yadda maryam ke ta faman halako fada,
Tace kafirin banza kafirin wofi don ma bakiji hausan shi ba wallahi kamar fa hausan mutum kwarai,
Anty Dije tace maryam ina fatan duk wanan zancen baki fada a waya ba dai ko,
To may ye Anty in ma na fada mai kawai ina aikina kafirin banza ya kirani, ya bata min lokaci,
Saida Anty ta zauna take cewa maryam mutumin nan ne fa abokin Assalam,kike ta surfa ma masifa,
Barin wankin tayi tana kallon Anty Dije tace Anty ce min fa maishi yayi sunan shi Joseph fa,
Shine mana Anty takara ce mata da dan karfi wai anty shi kafiri ne dama ba musulumi ba,
Ke baki sani bane dama
Hmmmm lalai mishon bat da musulumi,
Wallahi anty ni na dauka cewa musullumi ne shi duk ganin da nake msi,
Dan guntun kara dake gefe anty tadan duka ta dauko tana cewa wallahi ke dai kamar ace mai musulumi
Don dai gaskiya ya duk halin shi na kwarai ne, wallahi,
Daga inda maryam take tsaye tace furen juji kenan shi,
Ga halin kwarai amma ba alkiblan kwarai,
Dama malamin mu na islamiya ya fada muna ce wa akwai irin wa yan nan mutane acikin yan Ahal,kitab,
Saidai basu da yawa so sai daga cikin su, masu halin rayuwa irin na mumunai
Daga haka ta tabe baki taci gaba da wankinta tana cewa Assalam abokin Christian, shiko sai dariya yake mata don bai san ma,anar maganar ta ba,,,
Yinin ranan sai maganar ta dan tsaya mata a rai kawai tausayi yabata mutum kamar wanan ace baya sallah Allah ya kyauta kawai take cewa aranta
Sai ma daga karshe takama jin haushin shi, da takaicin kawai,,
Mr Emanuel yanzu girma ya fara kama shi don haka yanzu iyakar shi zama gixan man su ya daina yawan harkoki kamar da
Kamar su saida manja, saida robobin aiki irin na mata duk suna da shagunar su acikin garin kwantagora,
Yau ma kamar kullun zaune yake saman wata far kujera kamar kulun da yamma haka yakeyi sai zuwa shidda yake wuce wa church wani lokaci,,
Wani musa mai aski ne yazo inda yake don sun saba da musa,wanzami tun tuni
Saboda zaman uguwa guda, da suka taba yi ada,
Shine sabon su yai karko har zuwa yan zu
Musa yakan dan biyo ya samu dan abin ihisani akai akai
Bayan sun gaisa ne yake kokarin zama gefen da Ema mai manja yake, daidai lokacin yake cewa
Ashe taimakon da yaron ka yayi wa dan gidan Tanimu kafinta ke nan
Mr Ema ya ce taimakon may ke nan fa, acikin hausar su irin ta IBO,,,
A, ba ance ya samo mai babban aiki a Abuja ba har ma yai kudi lokaci guda,
Wani yar Mr Ema yaji kamar an datsa mai mashe a zuciyar shi,
Sai da yai kokarin boye ma musa wanzan da halin da ya shiga tukun sanan yace har ya fara aikin ne ko,
Musa wanzan yace kai tun yaushe aiki kan har mun fara cin moritar ta,
Don nafito zan wuce kauye nagan shi yana magana da wasu masu aikin gina wai yana son ai masu katangar gidan su,,
Wani iri mr Ema yakaraji a ran shi watau ke nan har maishi yadan fara karfi da tai makon Joseph din,
Alhalin ga yaran su cikin gari birjit da suka gama karatu suna ta bin shi yasamo masu aikin yi yana cewa ba aiki yanzu,,,