Author : Zainab Idris Makawa Category : Read Hausa Novels
kwanciyar shi,
Yusuf ya matso gab da tson inda suka sa mai kujera ya zauna suna fuskantar juna da tsohon,
Alokacin Yusuf yaji a zuciyar shi dama ace wanan tsohon shine mahaifin shi
Dayafi kowa morewa, mahaifi a rayuwa da ba zai iya gusawa nan da can ba a wanan halin da zai tsaya ya kula da,duk wani motsi na shi,
Yana zaunawa wanan tsohon yafara zuka mai albarka ya na mai fatan gamawa da duniya lafiya,
Wani abu ne yazo mai a makoshin shi ya tokare mai yakama jin wani irin tukuki a zuciyar shi,
Da kyat ya samu,ya hade wasu miyau masu daci, da yauki
Sai yar dariyar yake yake yi a fuskan shi tankar ya kai mai ciki,
Kai mutumin wani gari ne ?
Tambayar da tsohon yajefo shi da ita ke nan a lokacin da yake cikin tunanen shi,
Forgigit ya tuna cewa ko shi waye,
Inda har za,a tambaye shi ba zai gushe da fada masu gaskiyan ba kamar yadda ya saba fada cewa Asalin shi FUREN KAN JUJI NE,
Dayan yaron tsohon ne ke cewa ana tambayar ka ko kai mutumin wani gari ne wai,?
Kwantagora ya ba da, ansa, a ta kaice ,,,,
Wai, wai, akwai nisa gaskiya a cikin wani jaha garin yake dayan mutumin ke tambaya,,
A can cikin jahar Niger garin yake, yankin yamma,
Allahu akbar inji tsohon ya fadi lokacin da yake dan gyara kwanciyar shi,
Saida muma zamane yakai mu can asali mu yan jahar,Benue ne,
Gaba dayan su suka juyo da kallon su inda yake cikin mamaki,
Yace musulunta nayi bada dadewan nan ba saboda fahintar musulunci itace hanyar gaskiya,,
Gaba dayan su a lokaci guda sukace Allahu Akbar,
Kan shi ya sunkuya kasa don abinda yake ji, a jikin shi tun jiya,
Babu abin dake a zuciyar shi duk yinin yau kamar yadda zai furta hukunci da ya yanke a kan su,
Dan tsohon nan na kwace cikin cijewa irin ta mai jin jiki,
Tsohon yai ta bashi labarin ko shi waye da kuma yadda ciwon ya samay shi ,
Nan ne Yusuf gane cewa dan tsohon irin malaman nan na zaure ne masu tara almajirai da yawa agidan su,
Zaune take cikin wani yellow material dinkin buje da riga masu kyau,
Dan kwanlishi ba daurawa tayi ba just ta aza shi saman kan tane,
Wayan ta yana a hannun ta tana dan yin game da shi,,
Kirane ya shigo mata sai dai bata gane ko waye mai nombar ba,
Da sallama ta dauki wayan muryan mace ce ke magana a layin,
Maryam taji an anbaci sunan ta, batare da ta ansa ba taci gaba da sauraren mai maganan,
Sai kuma mai maganar bata kara cewa komai ba dan shiru ne ya biyo baya,
Tace baki sanni ba amma dai da zaki gan ni zaki sanni,
Kiran da nai maki shine akan nasaban ki da Yusuf watau Joseph dan gidan Ema mai manja,
Gaban maryam ne a lokacin yabada wani dam haka kawai batare da tasan ko may ye za,a fada mata, ba a lokacin,
Wani,tsoro ne ya lullube ta da sauri tadan kama waigawa ko zataga Anty ta da ido, a kitchen ta hango ta, tana kada miya,
Karo na biyu mai maganar ta kara ambatar sunan maryam din wanan katon kamar mai rada tai maganan
Daidai lokacin da maryam din ta iso gurin da yar na ta take ,
Kada kiji tsoro maryam ki saurare ni da kyau kiji may zance maki, da kyau,
Gaskiya ni bazan iya cutar da mutum dan uwana ba shi yasa naga ya dace in fito fili in fada maki abin da ke gudana akan ki,
Wayan suka zuba wa ido daga ita har yar ta suna sauraron mai magana,
A kofar shiga gidan ku an rufe wani abu wanda daga ke har Yusuf din indan kun taka kun rabu kenan har abada,
Sannan kuma ba zai kara kula koda Anty kiba bale wani naki,
Ke kuma ance a sakar maki ciwo mai kama da ta hauka ko batar hankali,
Don kowa yazaci baki da lafiya ne shi yasa zai guje ki,
Tagumi sukayi suna sauraro sai innalillahi suke ambatawa kawai,
Inda taci gaba da masu kwatancen gurin da aka binzine masu abubuwa akofar gida,
Anty ce ta tambaya cikin saurin jin datayi kamar mai shi tana kokarin rufe wayan ta, da cewa,
A sake cikin sauti mai karfi tace yanzu may abin yi yar uwa,
Mai maganar tace don girman Allah ku rufamin asiri kada ku bari agane cewa nice na fada maki wanan zancen,
Tambayar ta Anty Dije takara yi akan cewa may ye mafitan zancen,
Sai cewa tayi aje daidai gurin da aka bizzine abin a tone tun gudan su bai bi gurin ba,
Don tun daren kwana hudu daya wuce, aka rufe abin agurin,
Kuma wanda akaba kudi don yadiba koda maryam din tabi gurin yace har yau baiga fitan ta daga gidan ba,
Kinga ke nan abin bai fara aiki ba ke nan ko tace cikin nuna kulawa,
A sanyaye Anty Dije takewa mai wayan godiya sosai inda take cewa ai babu komai don duk ciwon musulumi na musulmi ne,
Inda tace insha Allah idan taji wani abu zata kira su ta sheda masu da wuri, wuri,, don su dauki mataki,
Maryam wace tun fara zancen idonta yaciciko da kwalla,
Take,hawaye yafara mata sintiri a idanun ta take dan she,shekan kuka,,
Anty don Allah ku taimaka ku jaye zancen nan tun ba,a halakani ba,
Zan hakkura da Yusuf din don dama nasan cewa ba sa,an yina bane
Kawai dai biyayyane nayi har na takai na fara jin shi a jikina,
A haka ta dinga share hawaye da bayan hannun ta,
Fuska a daure don jin abinda maryam din tace Anty Dije take kallon ta, tace wa yar uwan nata,
Yanzu maryam ina imanin ki da tauhidin ki ya shiga da har zakiyi believed da wanan maganan,
Kiyi imani da cewa duk abinda ya samay ki daga Allah ne maryam ,
Tunda har Allah yasa munji abinda ake yi akan ku kin ga sai kawai mu roki Allah ya kare muna ke,
Da sauri maryam tadan kalli yar,uwar nata tana kada mata kai tace, cikin muryan kuka,
Anty kawai dai a fasa wanan abin ni bazan iya ba gaskiya tun yanzu ace har an fara yiwayiwa mutun irin wanan sherin,,
Tana kokarin share hawayen ta, sheshekan kukanta na tashi cikin tashin hankali,
Murmushi Anty Dije ta yi ta girgiza kai, kaiyya maryam ai idan kince haka sun samu galaba akanki ke nan,
A sanyaye maryam tace cikin muryan kuka, Anty to ya za,ayi,
Anty Dije tace barin kira baba in sheda mashi abinda ke faruwa kafin abu yai nisa,
Daga haka suka bar wajen cikin tashin hankali saboda duk sun shiga rudani,
Yusuf ya kasa wuce saida aka sallami wanan tsoho ya dauke su zuwa, gida,
Badon komai ba sai don ya fidda kan shi a zargin da suka yi mai tun farkon dauko su zuwa asibitin,
Sosai mutanen kauyen sukayi mamakin ganin su tare da mutumin da sukayi zargin cewa dan yankan kaine da farko,
Saboda mugun haduwan da sukaga yayi gashi matashi ga kyau ga kudi kuma,
Nan malam yaroki Yusuf akan don Allah idan an kwana biyu yadawo garin yana da bukatan ganawa da,shi,
Amma kafin ya wuce yasa yaron shi karami yai mai a wani rubutu a ruwa yace yasha,
Yusuf wanda bai, so hakan ba azuciyar shi amma sai ya daure ya sha saboda biyayya kawai,
Da zai tafi yakawo alheri masu yawa yai ma malam da jama,an shi sukayi sallama dashi cikin dadin rai,
Sunkarbi nomban shi don su kirashi a cewar shi idan ya isa,
A hanya ne ya ke tunanen kitan Anty Dije wace yaiwa alkawarin kira tun daren jiya,
Ya so ne da kawai idan ya koma sai ya samu lokaci ya je kwantagora ya fadawa Anty irin shawaran da ya yanke a kan maganar shi da maryam acikin ruwan sanyi,
Duk da yasan cewa akwai rikici a gurin baba don dawuya yadauki yar shi haka kawai yabawa wanda bai san asalin shi ba,
Amma dai shi da kan shi zai fadakar dasu don su fahinta akan Sonny din,
Duk da yasan cewa ko shi don sun san asalin shi dakuma irin cin fuskan da akai mai akan neman mace,
In badon haka ba yasan cewa baza,a bashi ita ba sam saboda su talkawane da suka san mutuncin kan, su,
Zaune take a gurin da tagama sallah isha,i amma tunane duk ya addabe ta azuciyan ta,
Ba komai take tunane ba illa ta yadda za,a bullowa wanan bakon al,amari da yazo mata,
Don dai ita a iya sanin ta batada abokin fada ko kuma hamayya, ako ina,
Amma wai sai gashi kwatsan an wayi gari ana son a cutawa rayuwan ta,
Wayan hannun tane ta daga don ta diba time, tagani, saboda tasan cewa da zaran angama sallah isha,i baba zaizo,
Takwas da rabi taga don haka tamike tafara dan tattara kayan da tai sallah don kada baba yashigo bata a falin su,,
Falon yai shiru, baka jin komai sai muryan Anty Dije kawai da ke koro wa baba da bayani tiryan tiryan,
Kamar babu kowa a falon bayan ita, kowa da irin nazarin da yakeyi, daga baba har aminin nashi da sukazo tare,
Maryam ce a gefe guda tsugune sai hawayen da take zubarwa akai akai,
Baba kan lumshe idon shi yayi saboda mamakin yan Adam daya kama shi,
Yasan cewa Allah ne ya kare mashi yar nashi saboda addu,oin da yake yawaita yi musu, akai akai,
Yarinyar tana bashi tausayi saboda yasan cewa akan shi ce tai biyayya
Wani irin mugun tausayi tabashi da yadan kalle ta da,wutsiyan ido yaga irin yadda take share hawayen dake sintiri a idon ta,
Abokin baba ko ince aminin shi kuma makwabcin su, yai murmushi cikin gyada kai bayan ya gama jin bayanin da Anty tai masu kaf,
Yadan kalli inda baba yake yace, ina kon kwanto, amma ai babu komai idan har sun san wata aibasu san wata ba,
Don kaga Allah ne ya tona masu asiri don ya wargaza masu plan din su,
Amma zasu sha mamaki don ta Allah batasu ba sherin su zai koma masu,
Sallama sukayi wa su maryam din suka tafi tare da kwantar masu da hankali na cewa babu abinda zai faru da yardan Allah,
Hakan yasa hankalin maryam ya da yar uwanta ya dan kwanta amma ba wai gaba daya ba,
Koshi saboda sanin da sukayi wa shi malam na ngaski din ne cewa bakanwar lasa bane shima,,,,,,
Masallacin Jumma,an ya cika saboda anan sarki ke sallah da sauran dattijan gari,
Mahaifin jibrin da yawa daga cikin makwabtan su suna acikin sahun da suke kusan gaba, gaba,
Bayan an idar da sallah jama,a suna kokarin wuce wane sukaji wani bawan Allah mai zakin harshe yana cewa don Allah a,dakata ,
Akwai daurin aure ga wanda Allah yaba ikon tsayawa,
Hakan yasa jama,a da dama suka dan dakata don su sheda wanan daurin auren, da akai shela,
Mahaifin Jibrin tare da, malam Abdulsamad suka matso kusa da liman nan shima Mahaifin su maryam tare da sauran yan uwan shi har su, mijin mahaifiyar ta da ya aikawa yana son yazo ciin gari a yau,
Yakuma zo din duk suna gurin su malam A, A da su KB wanda shima yazo garin saboda matar shi da take dauke da tsohon cikki,
Anan ka gudanar da shardan aure kamar yadda aka sharida wa musulumi, ci, da sha da sutura,,
Sanarwa kawai sukaji mai fada na fadin cewa an daura auren Yusuf da maryam akan sadaki naira dubu hamsi, kacal,
Inda mahaifin Jibrin din ya gabatar da kudin a hannun waliyin auren maryam din watau mijin mahaifiyar ta da malam aminin shi,
Ba,a dauki wani lokaci ba wasu mutane suka gane ko auren wa akadaura a lokacin,
Ciki har da A,A dasu KB da sauran abokan hurdan Yusuf din,
Ba,karamin mamaki mutanen da suka halarci daurin auren sukayi ba don basu da wani masaniya akan zancen auren, shi,,,,,,
ZEEE MAKAWA YALWA,
[4/27, 05:04] Anty Lantana: πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
FUREN JUJI
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
8β£3β£
ZAINAB IDRIS MAKAWA,
YAURI
YA,Allah, Ya Rahaman Ya Rahimee, Ya Maliki, Ya Salam, Ya Fattahu, Ya Haiyyu, Ya Kaiyyumu, Ya Malikil, Mulku,Zullani Wal,ikiram,
Allah kasa mudace ya,Allah kasa mugama da duniyan mu lafiya, Allah ka rahama muna,πππππ
Kiran layin wayan shi yake yi a gagauce tun bayan minti goma sha da suka wuce,
Amma layin baya shiga sam switch, off suke cewa tun dazu,
Ba halin shi bane hakan sam rufe waya don haka yake mamakin abinda ke faruwa,
Layin Jibrin ne yakira don ya ji ko Yusuf din lagiya yake ya kashe duk layin wayan shi,
Kira guda layin Jibrin din yashiga sallama tare da yar raha kamar yadda,suka,saba,
Amma wqnan karon Jibrin din kawai keyi shi KB yaki mayar, mai da martani kamar yadda,suka saba,
Sosai abin yabashi mamaki don ba irin haka suka,saba yi a tsakanin su ba,
Kai ina mutumin yashigane wai duk wayoyin shi a kashe tun dazu,?
Au Yusuf kakw magana gaskiya ban da masaniya don dai jiya yana hanyar shi ta,dawowa kano mukayi magana, dashi,
Amma yanzun nake son daga nan mosque in wuce gidan shi in mai sannu da zuwa,
Ke nan kana da labarin auren shi kai ko ?
Ban fahince ka ba in Jibrin wanda tambayar ta KB tazo mai wani iri,
Aure ?
Wayai aure kake nufi wai ?
Ansa yabashi dace wa wai kaima kana nufin kace min baka da labari,
Bayan mahaifinka ne yai waliyin auren da aka daura mai a massalacin jumma,a dazun nan,
Mamaki kwarai Jibrin din yayi sai kuma ya kama tambaban ko da wace ce aka daura auren,
Zaune yake a gidan inuwan wani ice dake cikin gidan man nashi can gefe guda , yana kallon duk wani mai shige da fice a haraban gidan man,
Mutun biyune saman wata tsohuwan mashin suzuki blue,
Tunda Mr Emanuel ya hango su ya daure fuskan shi,
Saboda suna daga cikin masu zuwa gurin shi yawon maula,
Hakan yasa yana hangosu ya daure fuskan shi saboda yana bakin cikin irin wanan halaiyan na irin mutanen nan masu yawon maula,
Gaisuwa,sukafara dashi tare da tambayar lafiyan jikin sh,
Daya daga cikin mutanen ne kecewa Mr Emanuel din wanda ya,daure fuskan shi tamau, don kada su ji dadin rokin shi,
Mutumin yace ashe yaro ya yi aure shine muka ce bari muzo muyi ma murna,
Mr Ema yace cikin kada kan shi wa ?
Ummmmm, Ummm ba yalo namu bane,
Shiru mutanen sukayi sai zuwa can gudan yace yaron kane mana wanda ya musulunta kwanakin baya,
A,a yana kada kai alaman bashi bane, cikin daurewa fuska,
Mutumin ya dage da cewa shine fa wanda akecewa Yusuf Joseph,
Gaban tsohon ne yaba ba da damm, saboda bai taba zaton haka daga dan nashi ba,
Indan ko har hakane plan din su akan Yusuf din ya rushe ke nan,
Don tun da har yaji cewa anyi aure tsakanin shi da diyan musulmai, yasan cewa mawuyacin abu ne, kuma ya dawo cikin su ,
Don haka bai tsaya sauraren wani abinda zasu ce ba yadogara sandar shi ya mike tsaye,
Fuuuu yabar gurin batare da ya tsaya takan mutanen ba,
Inda haushi yakama su don su azaton su zasu samu kyauta a gurin shi,
Kusan kowa da yadace ace ya kirashi a lokacin da ake bukata samun shi a layin amma layi. Nashi yana a kashe duk wanda yakira shi bai samun shi,
A hankali yake saukowa a matakalan jirgin inda yake saye cikin bakar corth da wandon su,
Bai riko komai ba a hannun shi sai wata yar karamar briefcase da ke rike a hannun shi,
Enoc ne ya iso don taron maigidan nashi wanda yadan dade bai shigo Lagos din ba,
Cikin farin ciki suka gaisa inda yake mai sannu da zuwa a cikin mutunci,
Sun isa gida lafiya inda yasamu gidan shi lafiya lau kamar yana aciki ko yaushe,
Wanka ya fada ya tare da dauro alwala, bayan yafito ne yai sallah tare da mikewa zuwa falo don yaci abinci,
Cibi uku kawai yayi sai yaji karan wayan Enoc wanda matar shi takira a lokacin,
Sai a lokacin wayar shi da take a kulle tun jiya tafado mai arai,
Briefcase din shi ce yasa a miko mai yaciro wayan a ciki,
Sakon nai da miscalls ke ta baiyyana a cikkn wayan nashi a lokacin da