Furen Juji Book Compelet Zainab Makawa

Author :  Zainab Idris Makawa Category :  Read Hausa Novels

Chapter   60 / 84

177K to 180K   out of 251.8K words

Anty Dije taji suna mai sannu da zuwa tare da fada mai cewa zai fita da su da little Mum,
A tsorace maryam ta sake tsaki saboda yawan suruntun yaran da yai yawa,
Tau fa zuwa ina da daren nan yake tambayar yaran,
Suna hada baki gurin cewa gidan Anty Naimat, zamu tafi tare da little mum
Wani murmushi yayi mai sauti yana cewa cikin daren nan zaku bazaku bari da safe ba,
No, Uncle inji Assalam gobe akwai school bamu zuwa ko ina,
Idan mun fita sai na gama zan je nadauko ku ke nan,
Tsigar da yake maganar shi yasa yanayin maryan jin tsoro don tasan ceq zai zube su nan ne yatafi nashi tsabgar,
Idanu ta zare don tagona manufar zancen shi da sauri ta kalli agogo inda taga takwasa saura na dare,
Muryan anty ce ya katse ta tana cewa wai ina maryam ta zuba ma abinci,
Da sauri ta karasa daurin dankwalin dake hannun ta tun kafin anty ta balbale ta tafito,
Karan daurin zanin ta ne dake bada sauti idan ta taka yasa shi daga lumssasun idanun shi yadan dubi gefen datake tafiya,
Wasu shaddane jikin ta masu ruwan makuba dinkin fitted ne anyi aikin wuta akai an darza wasu duwatsu kanani suna walkiya,
Sai wasu takalma plat masu dan tudu kadan adudugen su,
Ganin shi zaune a cikin falin nasu alokacin yasa tai mai
Sannu da dawowa tace mai a takaice ta wuce abinta zuwa kitchen,
Mamakin iya kwalliyan wanan yar karamar yarinyar yake yi,
Yarinyar duk yadda tai kwalliya sai ya burge mutum,
Already abincin yana a cikin kula don haka daukowa kawai tayi takawo mai inda yake zaune,
Kai maryam har kin ban tsoro da,wanan kulan naki ,
Masan da naci dazu baiko gama aikiba fa yadda yai maganar saida kowa falon yai dariya har maryam din dake ta faman daure fuska,
Harara maikama da murmushi ta sakar mai ta gefen ido tace aiko tunda munyi dole kaci shi uncle,
Assalam ya jowa yana cewa zo ka tayani my son kada in kasa ccinyewa ni kadai,
Bayan tagama zuba mai dan kadan tamike tsaye ahankali tana mai kokarin wuce,
Sunan ta yakira a hankali yana mai langabar da kan shi cikin marairaicewa kamar dan karamin yaro ya na mai cewa haba little Mum ai wanan yai muna yawa,
Mikewa tayi gami da dan mai hararan wasa wanda yakarawa fuskan ta kyaun kallo,
Tace cikin yar murya irin nata,
You have to eat, it ,all so pls excuse me,
Da sauri Yusuf wanda sam ya manta cewa anty Dije tana gurin yai niyar kamo ta cikin wasa,
Maryam wace a zaton ta dagaske kamota zai yi sai ta dan zille mai tayi waje tana dariya ,
Wanan abin yasa anty dije cikin farin ciki amma sai tai kokarin boye farin cikin nata agaban su,
Don haka sai ta nuna cewa bata fahince shi ba takawo wani zance na daban,
Kwalaben turaren wuta anty bawa su maryam sukaiwa Naimat din,
Inda Yusuf koda bai gani ba afili yai murna sosai irin yadda yaga tana kokari da yar uwan nashi,

Wakan secret lover's ke tashi a motar inda Yusuf ke marming a hankali,
Yana tukin motar tankar wanda bai son tukin alokacin, a hankali,,
Wayar shi ce tai kara inda yaga kb ne bai fi minti biyar ba yakashe wayan,
Sai kuma ga kiran Jibrin ya shigo again, kamar hadin baki,
Yadai mutumina yace da ya dauki wayan, alokacin wankan dake tashi bai bari suji may yake cewa,
Amma dai taji lokacin da yake cewa gani nan da su maryam za mutafi unguwa,
Batasan ko may yace mai ba sai murmushin da taga ya dan yi,
Fuskanta na gefen widow tana sauraron abin da mawakan ke fadi gamay da secret loves, d two hearts dat beat together,
Kaman kada ya gama wayan sai wani irin annashuwa yazo mai a lokaci guda,
Muryan shi ya kashe ta yadda yaran dake bayan motar baza su iya jin ko may yake cewa ba
Maryam ya ambato cikin muryam maikama da wanda ke rada, yace,
Kiyi hakkuri da ni pls duk da nasan cewa bai kai matsayin da zaki soni a zuciyar ki ba
Badon komai ba sai don kasan cewa na tankar FUREN KAN JUJI,
Don banda wasu yan uwan da zan gwada wa alumma inyi alfahari da su, acikin su,
Kinga kuwa hakan zai sa duk wani mutum mai raunin imanani ya ji kyamar hada wani alaka dani kamar yadda iyayyen Sadiya sukai min ikirari da hakan,
Abin mamaki sai maryam taga kawai hawaye wasu na bin wasu a fuskan shi
Abinda bata taba gani ba a rayuwan ta taga namiji na kuka haka,
Itama maryam haka kawai batasan lokacin da hawaye wasu na bin wasu afuskanta cikin kukan tace may injiwa
Ni uncle bana kyamar yan uwan ka tunda mahaifana basu kyamace ka ba tun farko,
Cikin murya maikama da rada tace kawai dai malam A, A da mukayi nisa da shi nake jiwa,
Murmushi yayi daidai lokacin da zasu karya kwanar da zai sada su da unguwar su Naimat,
Hasken motane ya hasko mata motar A, A din tare da wata yarinya a tsaye hannu rike da na juna,
Yana saye da wani dinkin shadda light green
Ganin hasken yaimai kau a lokaci guda yasashi kokarin kate fuskan shi da hannayen shi,
Gaban maryam ne yabada damm kardai A,A karya yai mata dama,
A zaton maryam Yusuf baigane cewa A A din ta bane can suka wuce, a baya,
Wayan ta ta jowo takira layin wayar shi, tambayar shi tayi da ya isa lafiya ko?
Ya amsa mata da cewa a,a lafiya kalau har ma na kwanta,




ZEEE MAKAWA YELWA
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
7⃣2⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI


IY,YA,NA,A ABBUDDU WA,IYYAKKA NAS,TA,INN,



Duk da ga hasken street light's da ya haske ko ina a titin da kuma hasken abin wuta da ke gittawa jefi jefi a lokacin,
Baisa idon maryan ganin haske ba alokacin, magana Yusuf ke mata amma sam bata ji may yake cewa ba ,
Sai ji tayi yana cewa idan kun shiga kada ku dade zan dan je in dawo pls,
Hakan ne yasa ta gane cewa sun iso gidan su Naimat din ke nan,
A hankali ta sauka motar batare da ta dauki ledar sakon da Anty ta bata takawo ma Naimat ba,
Yusuf din ne bayan ta sauka ya miko mata ledae yabata takar ba a darare, tawuce zuwa cikin gidan,
A lokacin yaran da suke a tare har sun isa ciki ko sun ririke Naimat din,
Sun sami Ibrahim a gida don haka bawai wani sake jikin ta tayi ba,
Saboda dama hankalin ta baya tare da ita a lokacin,
Ganin yanayi da maryam ke cikine yasa Na,imat dan maida hankalinta gare ta,
Saidai maryam din tayi kokarin yin dariya irin ta yake din nan,
Fira sukeyi amma zuciyar ta ya,gurin abinda idon ta ya hasko mata, dazun nan,
Sakon da,aka basu ne sukawo wa Naimat maryam ta bata tai mata bayanin akan ko wanin su sai wani mugun kamshi ke ta shi,,,
Nan Naimat din ta dinga jin dadi saboda wanan sakon da akai aiko mata,
Sun kai kamar minti talatin Yusuf yadawo inda yakira ta layin wayar maryam din,
Tare suka fito da Naimat don ta gaisa da Yusuf din wanda har zuwa yau bai taba shiga gidan Naimat din ba,
Itakan maryam karfin hali kawai takeyi a lokacin saboda abinda tagani yau karara cin amanar da kusan ko da yaushe safiya ke fada mata cewa A, A cin amanarta kawai din ya keyi,
Amma ita sam so ya hana taga gaskiyan hakan da ake fada mata
Magana sukeyi amma acikin yaren su na IBO ne don haka maryam takoma jikin mota ta dan jingina jikinta a kai,
Saboda irin yadda take jin kafafunta baza su iya daukanta ba,
Kallo guda zakai mata zaka ne cewa babu kwanciyar hankali a tare da ita alokacin,
Shigar su mota ba,wanda ya kara yiwa wani zancen komai kowa da abinda yake sakawa a zuciyar shi,
Sun shiga gida tana tsaye tanawa anty bayani sakon Naimat amna sam Anty ta kula da cewa bata a cikin hankalin ta ,
Ledojin da Yusuf ya sayo masu kaji gassasu da kuma drinks masu sanyi da tsada,
Sai wasu kayan tarkace su sweet da sauran su biscuits, kala, kala har leda biyu,
Gudan ledan dagani tarka cen maryam ce a ciki amna lokacin da anty Dije ke ce mata tazo ta dauki nata sai cewa tayi anty tabarshi a gurin ta,
Tasa kai kawai daniyar shigewa dakin su, batare da ko ta juyo ba,
Anty Dije cikin haushi take cewa maryam wai ke wata irin yarinya ce mai taurin kai,
Dan Allah ki duba wanan yaron bai fasan ko mu suwaye ba Allah ya hada mu dashi har yake muna irin wanan biyayyan tankar wasu yan uwanshi na Jini,
Ke ko duk kin bi kin takurawa wa rayuwar ki,
Kin hana rayuwar ki farin ciki, kullun a cikin tsangwamar kan ki da tashin hankali,
Maryam kan tana daki zaune saman gadon ta sai hawaye takeyi na takaici,
A haka ranan ta kwanta ko kayan jikin ta ta kasa cirewa kafin ta kwanta,,

Zaune yake inda ya idar da sallah walha kamar yadda ya saba yi,
Jikin shi saye da wata bakar jallabiya mara hannuwa,
Zaune yake a takure yana jan casbi da hannu guda a hankali,
Wayan shine Jibrin din ya kira shi yana,cewa ga,shi ya taso zuwa KG din shima,
Nan dai sukayi sauran bayanin irin abinda zai zo mai da su na bukata wanda bai samu sayowa ba,
Suna sallama da juna sai abinda yafaru jiya da dare ya fado mai arai,
Ashe bayan ya aje su maryam gurin da A,A yake tare da wanan yariyar yar makarantar su ya koma ya samay shi,
A hankali yafito daga cikin motar shi daya dan Parker nesa kadan daga inda suke,
Tafiyan shi irin na gogagun matasa yan bariki da yake ko yaushe har yazama mai jiki, shi yakeyi ya tun,karo inda suke,
Da farko bai gane ko waye ba sai da Yusuf din ya zo gab da su yagane cewa shine,
Hannu ya mika mai don su gaisa amna sai Yusuf din yaki sai dai ce mai da yayi sallamu Alaikum,
May yasa baku zantar da gaskiya a cijin rayuwa mai karya zai haifar ma arayuwa,
Yaudarar diyan mutane tankar wani taki ne da mutun ke zuwa bawa acikin gonar shi,
Don duk abinda ka shuka sai ka girbi abinka ga hannun ka,
Yauda gobe dama masu karin magana sunce sai Allah,
Yariya ta dauki amana da gaskiya tabaka amma kai ashe yaudar ta kakeyi,
Ko da yake itace dai dama bata san da haka ba amma ai duk wani wanda ke tare da kai yasan da hakan,
Don ruwa ba saa,n kwando ba ne ,
Dakata malam inji A, A yake cewa ina ruwanka da rayuwata da har zaka zo kana min irin wanan nasihar haka kamar wani malami,
Tubabbe irinka da bai ko iya karanta fatiha ba har zaka zo kace ni zakaiwa wa,azi,
Tun,da kai kagane cewa ina cin amanar tane ai in ka isa sai ka hana ta kulani,
Ko kafada mata cewa ga irin yadda nake ko ya kare yana wani shu,umin dariya, a karshe,
Azaton shi ya kashewa Yusuf baki ba zai iya cigaba da maganar shi ba,
Yusuf yai mai wani irin kallon na baka da mutumci yace ai ba sai na fada mata ba,
Don tagani da idon ta kuma tai kokarin confirming ko da gaske yaudarar ta kayi sai katabba tar mata,da hakan din,
So Wait and see what Will happen,
Ya juya kawai yabar gurin cikin kunar rai irin yadda musulmi dan uwar ka zai ma gorin addini ku,
Lumshe idon shi yayi yana mai jin kunar irin tozarcin da ake yawan yi mai akan zaman shi cikin musulmai hausawa,
Murmushi ya yi gami da,wani irin shu,umin murshi daya biyo bayan na farko,
Daga haka yamike zuwa bathroom don yai wanka yafita zuwa gidan Dad,

Anty Dije taimamaki acikin zuciyar ta jin maryam na cewa zata gidan su safiya tunda farar safiyan nan,
Murmushi tayi don tasan cewa, akwai dai saboda Safiya ce indan tazo kullun korafin ta shine maryam bata da zumunci,
Zaune take a dakin da aka warewa safiya da kannen ta acikin dangidan nasu mai gina irin na local people,
Hawaye wasu na bin wasu, ita ko,safiya wace ke zaune gefe acikin tashin hankali sai hakkuri take ba,
Duk da maryam din ta kasa magana balle ta fada mata abinda yafaru yasa ta wanan irin kukan haka,
Sai da ta,samu ta dan tsa,kaita kukan ne tafara tambayar ta ko may ke faruwa,
Sannu a hankali ta zayyanawa safiya yadda sukayi da A A din daren jiya,
Har saida takai karshe safiya tana sauraren ta bata ce komai ba alokacin,
Murmushi safiya din tayi da tagama jin may tace,
Ta ce gwada da Allah ya gwada maki kika gani da idon ki,
Ai yanzu zakiyar da da cewa dan iska ne macuci mayaudari,
Fuska a,daure maryam ke kallon ta tace ke nan ma ke kin dade dasanin kowaye shi ko,
Safiya tace tun yaushe maryam ai shima yasan nasani saboda acikin office din shi na kama,shi, red,handed,
Ido waje Maryam ke kallon Safiya don jin abin da tace, nan dai safiya ta bata labarin cewa taje gurin shi don tai mai magana akan takardun ta,
Shi ne ta samay shi tare da wata yarinyar yar IBO suna kiss,
Na shiga uku maryam tace tasake wani sabon kuka alokacin,
Safiya tace rokona yai tayi dan Allah in rufa mai asiri kada in bari ki sani ki, ki shi,
Harda alkawarin kudi yai mun nace mai ban so yadai daina abinda yakeyi,
Ni a lokacin maryam ke ce ke bani tausayi ina gudun kuyi aure ya dauko maki cutar kanjamau, a karshe,
Rinanun idanun ta da suka sha kuka sukayi jawur,da su, tadaga tana mai kallon safiya da su,
Tace cikin wani irin muryan kuka mai ban tausayi Safiya malam ya cuce ni wallahi,
Sai dai nagode ma Allah da daidai da rana daya bai taba nuna min true colour din shi ba,
Safiya tace ai kin san cewa yai min aike matar aure ce su ko wa yan nan na rayuwar waje ne kawai,
Safiya tadan dafa ta tace ki godewa Allah da bai sa yakai ga cuta maki rayuwa ba,
Kawai ki fita batun shi kiyi fatan Allah ya baki wanda yafi shi nan gaba,
Wani sabon kuka tasa ta shige jikin safiya saida tayi mai isar ta,
Ruwa safiya takawo mata ta wanke idon ta dashi sai faman ajiyar zuciya takeyi akai akai,
Duk yadda safiya taso su karya a tare maryam din taki don haka ta kyale ta kwanta sai barci mai nauyi ya kwashe ta abinka ga wanda baiyi barci ba adaren jiya,
Wayan ta yai kara safiya tadauka azaton ta ko A, A din ne tai mai tas sai taga ashe Anty ce,
Waje tafita don ta sheda mata tana barci hankali anty ya kwanta don jin lafiya maryam din take,,,,

Zaune suke a tangamaymayn falon su na gidan mahaifin shi dake dauke da jibga,jibgan kujerun da Yusuf ya sa masu da dadewa,
Mr Emanuel wanda ke zaune cikin shiga irin ta IBO, da,wani abu kamar zani ko buje daure ajikin shi,
Sai da yadan kurba ruwan Lipton din aka dafa mai as usual sanan ya kali inda Yusuf yake zaune yace mai,
Kada ka man ta da maganar da naima duk Christmas atare da mu zaka yi shi,
Yusuf yai yar murmushi kafin yace ai ba matsala saboda addini na ya yarda min da in shiga church don wasu yan dalilai,
Na ku daine sam ba a yarda ya,shiga muna gurin bautar mu ba saboda tsarkin sa,
Dad sai da naje Jerusalem na fara gane ce wa Muslim suna gaba da mu sosai saboda duk irin abinda sukeyi shine mutum zai yi acan,
Daga Alwala da kuma sa tufafi masu daraja sai cire, takalma don shiga cikin churches din,
Zaici gaba da bayani Mr Ema wanda tunda Dan nashi yafara bayanin abinda yagono a Jerusalem, yake ji tankar yana zuba mai ruwan zafi ne ajiki,
Duk da yasan gaskiyan maganar ke nan Yusuf ke fadi,
Yadaga mai hannu a lamar ya isa haka, bai son jin kareshen zancen,
Murmushi Yusuf yayi don yasan cewa gaskiya yake zaiyano mai baidai son jin zancen ne
Ga mamakin

60 / 84