Furen Juji Book Compelet Zainab Makawa

Author :  Zainab Idris Makawa Category :  Read Hausa Novels

Chapter   45 / 84

132K to 135K   out of 251.8K words

fada kamar wace akaiwa wani abu
Karin bayani sosai Ejoma keyi mashi ta yadda zai fahince ta
Sai ga mama da jakar kayan ta tana ta fada cewa wai a kwai evil din dake cutar su agurin,
Da kyat Yusuf ya samu takoma don ko shi saida yace mata akwai yan rituals a waje sanan ta yarda ta koma,

Tafiya take cikin sauri saboda tana son komawa gida da wuri yau,
Gurin bus stop take kokarin zuwa kozata samu motar da zai kai ta cikin gari da wuri,
Horn taji anayi a bayan ta batare da ta waiga don ganin mai shi ba don bata tsan mani cewa ita akewa horn din ba,
Saida, taji muryan shi yana cewa Maryam bakya ji ne halan,
Sai a lokacin maryam ta juya ta san cewa da ita yake,
A hankali ya samu guri ya Parker motar shi kamar ta wuce sai dai ta daure kawai ta nufi gurin shi,
A hankali ta gaishe shi cikin girmamawa kamar kullun,
Ya amsa mata acikin husky voice din shi
Yatare ta da cewa maryam wai guduna kikeyi ne yanzu ko may,
Don yanzu sai ki shigo cikin school din nan batare da kin je guri na ba,
May nai maki halan kike min wanan judgment din pls,?
Daidai lokacin da ta bude motar tashi ga ta zauna da kyau tadan kalle shi da dauraren fuska tace,
Haka dai kagani malam amma ni may zai sa in ma haka kawai,
Motar yaja suka bar gurin tare da ci gaba da lalashin ta,
Nan yake sheda matacewa yasan ta na fushi dashi don tana gani kamar yaki maida hankali ne a kan zancen su,
Yace ya turawa mahaifiyar shi da wani kawun shi don yaje akai karshen zance,
Maryam dai batace mai komai ba banda cewa da tayi Allah ya kyauta kawai.
A kofar gidan su ya aje ta tare da kara bata hakkurin cewa insha Allah komai zai zama daidai,
Sai a lokavin maryam tadan sauko daga fushin da tayi dashi saboda yana yawan sa mahaifinta na fada da ita da Anty cewa sun mai dashi bi nan,
Rana akeyi ga kuma alamar hadari da ya rufe ko ina giragizai suna yawo alamar ruwa zai iya zuwa ranan,
Tasamu Anty ta rage duk wani aiki da zasuyi a yinin ranan,
Tana zaune tana kallon tv ita da Abubakar wanda ke ta wasan shi shi kadai, a tsakar falon su,
A gajiye ta fada saman kujera tana mai cewa wayyo Allah na wash ,
Har kun dawo inji Anty tana kokarin mikewa tadauki Abubakar din ita maryam,
Ganin yadda take fara,a yau batare da tashige watsa ruwa kamar yadda tasaba ba indan ta dawo yasa Anty gane cewa tana cikin farin ciki yau din,
Tambayar ta yi dacewa halal A, A ya sauke ki naji horn din motar shi, ?
Maryam wace ta dan dakatar da wasan da takewa yaton don jin tambayar da yar ta tai mata,
A hankali tare da sauke yaron dake hannun nata ta amsa da fadin cewa eh a hankali,
Nan take fuskan Anty ya canza ta nuna wa maryam din bacin ranta sosai,
Nan ta shiga yi mata fada akan cewa gaskiya ita zata fadawa baba don yafidda ita daga cikin wa yan da yake zargi,
Maryan cikin marairaicewar murya tace anty kwanan nan zai turo Insha Allah,
Harara anty ta watsa mata irin na ke kika sani din nan,,,,



ZEEE MAKAWA
[3/18, 22:02] Anty Lantana: ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ
FUREN JUJI
๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ
5โƒฃ5โƒฃ
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Jin,jina gare ku ko yau yan uwa masoya novel din furen juji,
Tsayawa rubuta sunan ku zai ci muna time shiya sa nake rubutawa a jam,i gabadaya,
Nagode kwarai da irin kainar da kuke gwada min har kullun,
Allah ubangiji ya karawa,Annabi daraja Allah ka,taimaki musulmi duk inda yake,๐Ÿ‘๐Ÿ‘๐Ÿ‘


Dole yatafi garin kwantagora ya samu Abdulsamad akan zancen Ibrahim da Ejoma,
Don haka yafara shiri matsalar shiguda yanzu shine yadda zai yi handling din maman Choima,
Idan son samu ne cikin wanan week din ya shiga garin,
Sai dai kuma ga aiki yai mai yawa,sosai yanzu da wuya yasamu zuwa cikin,wanan satin,
Zaune yake ya mai,da hankalin shi ga computer shi inda yake ta shigar da wasu sakon,nen masu mahinmanci,
Wayar shi ce tai kara ya mika hannu guda a hankali ya dauko wayar dake aje saman tebur din nashi gefe guda,
Jibrin KG yaga an,rubuta saida yadan sake murmushi yace ya dai man ?
Yace wallahi tun dazu naso inzo office din ka amma aiki ya hanani yau muna entered din kayan da suka shigo cikin wanan satin,
Sai kuma Jibrin din ya canza topic da cewa ga kuma tafiya ta, taso muna,
Kaida wa in ji Yusuf yake tambayar Jibrin din ?
Sai da Jibrin yai yar dariya sanan yace dakai mana ,
Tunda shi KB dama already yana can tun jiya,
Yusuf tace look Jibrin ina son shiga KG so,sai amma aiyuka sun min yawa ,
Dole sai zuwa satin sama koda zan tafi din yanzu,
Jibrin yace zancen baby din nan ce na gurina ya taso shine suka kirani wai inzo zasu sa lokaci,
Yusuf yace wa safiya ?
Ya amsa da cewa ita fa, kaga zamu iya zuwa mu ga su uncle di na akan zance Sadiya dayani
Don ina ga haka zai fi muna sauki da zuwan da zamuyi har sau biyu a cikin lokaci guda,
Shiru yayi kamar mai nazari wani abu yana sauraron Jibrin din,
Ko ya kagani ne man ? Jibrin ya,tambayi Yusuf din
Don haka bayan kwana biyu suka shirya zuwa garin kwantagora ,
Mota uku kawai sukai tafiya da su wanan karon basu zo da mutane da yawa ba,
Badon komai ba sai ganin dayayi cewa yanzu an rage kawo mai hari daga church din su,
Sai da suka kusa kawo wa sanan Yusuf yabugowa anty Dije waya yana sanar da ita cewa zai shigo gari yau insha Allah,
Idan har yana cikin mota yafi bukatar yai tukin mota da kan shi
Gashi kuma da masifar gudu a saman titi sai hankali wanda ke ciki, tare da shi ya tashi,,,

Shikan shi Jibrin yana mamakin yawan shakuwar Yusuf da Anty Dije,
Tunda yaga suna shiga gari, ya karya kwanar unguwar su Anty Dijen,
Saida Jibrin ya kasa daurewa yace wai man nifa har mamakin, kake bani,
Saida yadan juya inda jibrin yake zaune yace namay fa,?
Dariya kuma jibrin din yasa alokacin yana ta girgiza kan shi kawai,
Cak ya tsaya a kofar gidan misalan karfe biyar na yamma,
Yan samarin dake zama gefen gidan duk yamma suka yo kansu gaba dayan su, cikin murna,
Saboda sun san cewa zasu samu abin tabawa ke nan,
Hannu ya mika masu gaba dayan su a cikkn sakin fuska suke ta gaisawa da su,
Wani wanda ya samu kariya a sanadiyar hatsarin mashi yana kokarin taso wa zuwa gurin shi,
Da sauri Yusuf ya nufi inda yake yana cewa malam Aliyu har yanzu kafar nan tana nan ashe, ?
Bayan sundan yi ban hannun sun gaisa matashi wanda Yusuf yakira da malam Ali ya ce ma Yusuf,
Wallahi gani nan dai yanzu wai asibitin kashi na kano nake son zuwa a diba min ita,
Sai,dai kuma abin tafiyar ne sai a hankali wallahi,
Yusuf yace haba, haba dai ai da sai muyi waya ko,
Bari zan gan ka idan na huta ai yanzu shigowar tamu ke nan,

Maryam ce tafito daniyar zuwa nan yar kasuwar bayan kwanar kuka don ta sayo yan abubuwan da suke bukata don yin abinci dashi tunda yace yau zai shigo,
Turus taja tai tsaye don ganin da tai masu akofar gida,
Cikin kasa boye mamakin ta take kallon su
Harara ya saki mata daga inda yake a tsaye yace shine taron da za mu samu ke nan ko, ?
A hankali yake kokarin takowa zuwa cikin gidan nasu,
Gefe maryam ta dan rabe mai don yashige,amma sai yadan kurawa maryam ido wace a ko yaushe cikin kara canza mai take,
Ya na zowa daidai inda take tsaye yasa kafar shi ya take mata yan yatsun kafar ta da takalmin shi,
Wani irin dan sautin kara, ta sake, a lokacin guda da sauri ta daga kai ta dube shi,
Amma sai taga bai ma ko kallon inda take, sai kokarin gyaran kwalar rigar shi yakeyi,
Murya na rawa tace wayyo ya Yusuf katake min kafa fa,
Har zuwa wanan lokacin bai nuna yaji may tace ba,
Sai wani irin zugu take ji a yan ya tsun ta,gashi sai kara matse mata su yake da takalman shi,
Zafi da radadi ke ratsa ta alokacin gashi shi yaki daga kai ya kalli ko da gefen da take tsaye ne,
Wasu hawaye masu dumi suka silalo daga idanun ta,
Takara cewa dan girman Allah ya Yusuf kayi hakuri,
Sai a lokacin dan sasauta mata kadan wani irn ajiyar zuciya ta sake cikin kuka,
Sai da ya hango Jibrin yanufo kofar shigowa gidan yai sauri yadan ja baya kadan,
Yantsun kafar nata, ta kalla sunyi wani irin ja jajir
A hankali ta dafa bangon dake gefen ta, tana bi a hankali cikin dan gyashi,
Nan da nan ya tsuke fuskan shi kamar bashi bane yai mun wanan muguntar,
A lokacin jibrin ya karaso gurin yana cewa an sauke kayan ga mutanen ka nan zasu shigo dashi, yana nufin samarin nan da ke kofar gida,
Sai a lokacin idon shi ya kai ga maryam wace ke kwalla, wahala,
What's going on here man,?
Tankar da dutse yake magana yake magana don ko kallon shi bai yi ba,
Kokarin wuce jibrin dake son jin abin dake faruwa ya yi,
Sai a lokacin maryam tace mugu kawai azzalu,,,,,,
Saboda yadda ya waigo ta rai a bace idon nan sun kada sun yi mai jajir
Matsowa yayi a hankali batare da yadamu da jibrin na gurin ba ya dan nuna ta da yar ya,tsar shi ya ce
Ki kiyayeni fa don bata maki tsari,
Bata son nuna kariya a gaban shi don haka sai ta dake acikin tsiwa itama tace mai
In dan ban ki yaye ka ba fa sai may?
Kai ya gyada mata yace ok haka kikace ko ?
Zaki san kin taba Yusuf maryam,
Ya wuce fuuu ciki yabar ta nan tsaye tana kara kallon yadda kafar ta yai wani jajir a lokaci guda,
Wani hawayen takai ci ya kara zubu mata a fuska ta sa gefen hannun ta takara sharewa,
Sai a lokacin ta sauke wata irin ajiyar zuciya wanda bata masan tayi ba,
Amma zuciyar cushe da mamaki da tambayar abinda taiwa yusuf yai mata wanan salon muguntar,

Da murna Anty Dije ta tare shi tana kuma yi mai korafi cikin harara,
A she saida kaga cewa zaka shigo gari shine ka kirani, ko,?
Yai yar dariya ya sosa kan shi da key din dake hannun shi,
Ai don kada in kara laifi nai ya sa na bugo maki lokacin muna bayan mariga kadan,
Kai Yusuf karage wanan gudun wallahi, mutun baya tausayin kan shi,
Shigowar jibrin ya sa tai shiru nan suka fara irin ba,an da akeyi a tsakanin matar wa da kanin miji,
Falo Yusuf yashiga ya zauna ya bar su nan suna ta shan matar juna a tsakanin su
Shigowar maryam yayi daidai da isowar ta da ruwa a cikin gora taba Jibrin
Batare da anty ta kalli fuskan maryam ba tace maryam ba Yusuf ruwa don Allah,
Jibrin yai sallama da su yana cewa zai tafi ya kai tsara ban da yayo gida don kada zafin buth ya lalata su,

Zaune yake saman kujera amma zaman balance yayi alamar yana tare da gajiya alokacin,
Tashigo falon batare da sallamar ba, duk kan shi na sama idon shi a lumshe bai hana yagane cewa ta gurin ba,
Saboda kamshin da ya daki hancin shi na turaren ta duk a ranan humrah kawai tadan shafa,
A hankalo ya bude idon shi ya sauke su gare ta, gutun hawayen dake makale a fuskan ta yai tozali dasu,
Subbahanallahi ya furta da sauri har saida maryam din tadan razana
Tana waigen bayanta ko wani abu yagani yake kiran suna Allah maigirma haka,
Cikin wata irin murya ya fara magana,
Dan Allah maryam kiyi hakkuri ki yafe min pls, ban san cewa zaki ji zafi haka ba har ki kuka,
Banza tayi da sai ta dangwar da tiren da takawo mai abin shan aรงiki gaban shi,
Tana kokarin mikewa yai yunkurin kai hannun shi da niyar ya rike ta,
Komay ya tuna kuma yai sauri ya jaye hannayen shi gare ta,
A,rau,nane yakara fadin don Allah dai maryam kiyi hakuri
Wallahi wasa nake maki saboda naga baki tare mu ba kina muna kallon mamaki, kawai, shine nataka maki kafa don ki san ba mafarki kikeyi ba,
Kala maryam batace mai ba sai mikewa da tayi tana kokarin barin gurin,
Haba maryam ina mun daina fada dake haka don may zan baki hakkuri ki kyale, ni,?
Ganin zai sa har anty taji ta dauka ko wani abin ne yasa maryam,
Tai saurin dagawa daidai lokacin da shima yadago sai jikin su ya gogi juna
Cikin sauri tabar falon batare da ta ko waiwayo inda yake tsaye ba,
Sai da yaga shigewar ta ya karkada kan shi yana murmushi don dariya ma ta bashi,
Sai gab da magrib ya bar gidan zuwa gidan shi don yaje ya watsa ruwa,

Washegari zaune suke saman wani benci a kofar gidan Abdulsamad din,
Cikin yaren su suke magana ,
Abdulsamad din ne bayan ya gama jin bayani Yusuf a kan zancen Ibrahim da Ejoma,
Yadan gyara yace wa Yusuf aiko don yariyar ta musulunta bazan hana Ibrahim auren ta ba sam ,
Ba don komai ba sai don jahadin da zai yi, ceto rayuwar yarinyar da ga kafurci,
Kai Yusuf ya kada don ya kasa ban,banta sakanin shi da Abdulsamad wanda ya rike musulunci gam gam gam tankar addinin da aka haife shi a ciki,
Abdulsamad din ne ke bashi shawaran cewa idan yazo yadinga zuwa yana gaisawa da mahaifin shi tunda yafara saukowa,
Yusuf wanda dama yana da niyar yin hakan amma kuma sai yaji dadi da shawaran da aka kara bashi akai,
Yaji dadi sosai na rashi samun matsala akan zancen Ibrahim din da Ejoma wanda dama bai tsamani haka din ba daga dattijon,
Sun shirya cewa azo da ita nan kwantagora a musuluntar da ita zai fi don mutane su sheda musuluntar nata,
Daya tashi wani katon shago ya shiga yai wa mahaifin shi sayayya a ciki sai daga ciki babu abin maye sam,
Direct gidan su ya wuce don yasan cewa yanzu suna gida basu fita ba tukun,
Taron da ya samu yau ba yabo ba fallasa a kai sai dai shi bawai yadamu bane da yadda ake wani daure mai
Tunda yasan cewa ba wai laifi yayi ga Allah ba akai,
Sun danyi hira da mahaifin saidai duk akan viwon shi ida Yusuf din yake cewa zai zo ya kai shi asibitin Turkish da ke abuja don adiba shi,
Ga mamakin shi sai yaji mahaifin nashi bai yi musu ba akai, sabanin yadda ya zata zai ce bazai tafi ba,
Karshe Mr Ema din yake cewa Yusuf yana son wanan Christmas din yazo gida ayi da shi,
YUSUF bai musa ba sai cew yayi in sha Allah zai zo a lokacin,
Dan dattijo ya bata fuska shi jin, dan ,nashi yace Insha Allah acikin maganar shi,
Daga gurin mahaifin shi ya juyo zuwa gidan Anty Dije don ya yi breakfast,
Duk da yake a gidan mahaifin nashi yasa may su, suna batun yin break,
Maryam bata gida yau tunda safe ta tafi gidan su SAFIYA,
Ba don komai tayi shawaran zuwa wanan uguwar ba don kawai gujewa haduwa da Yusuf din wanda ke gari,
Tun safe sai dare zuwa bayan isha,i ta dawo daga u,subu can uguwar su safiya din,
Da yar fara,ar ta ta dawo tunda tana zaton ya,tafi ko tunda da Jibrin suka zo garin don haka tana zaton suna tare
Amma sai fara,ar ta ya lake lokacin da taji wanda ya ansa mata sallamarta,
"Sannu da dawo"
Abinda ya furta mata ke na,
A cikin matse fuska ta ansa mai da "Yauwa"
Wani murmushi yayi kama da yake, duk da dare ne sai da maryam tagane na mugunta ne,
Yau kuma unguwa aka tafi har dare haka,?
Kafin ta san ansar bashi sai taji duk ta dabur ce,

45 / 84