Furen Juji Book Compelet Zainab Makawa

Author :  Zainab Idris Makawa Category :  Read Hausa Novels

Chapter   10 / 84

27K to 30K   out of 251.8K words

Dije ta gama abinci kenan tana ko gyara ko ina na gidan,
Daga waje yadan tsaya duk da cewa an bashi umarni akan ya shigo ko yaushe yake bukata,,,,
Amma sai yaji cewa bazai iya shiga ciki kai tsaye ba
Don haka daga daga,waje kadan yadan tsaya yace Salamu Alaikum don Allah ko Assalam na ciki,
Cikin mamaki mai ma Assalam sallama duk suke
Shiko Assalam har yagane murya da wani irin ihu yafita kofa inda Joseph ke tsaye yadaga shi sama cak yana dan juya shi,
Sai suka kama dariya a tsakanin su, daidai lokacin da duk sauran yan gidan suka leko ta kifar falo suna kallon su,
Ànty Dije ke cewa a, Joseph shine baka shigo ba ka tsaya daga nan kana cewa kana ma Assalam sallama,
Dan sosai kai yayi da key din motar shi yace ai zan shigo nakira Assalam ne yai min jagora,
Falon anty ta bude mai yashigo daidai lokacin da maryam ta dauki buta don zuwa yin alwalar sallah magrib,,
Bayan sun gaisa da Anty dije sai kwai ta fara gabatar mai da abincin a lokacin don dama har ta gama komai,,,
Cikin nuna jin kunya yace mata ya gode bazai ci ba
To ke nan kai kana jin tsoron cin abincin mu Joseph shine shi Assalam, ka ke kawo mai sweet, time to time,
No haba Anty gaskiya ba hakana bane,
Kawai dai naga cewa nashigo late evening ne kin rida kin gama cooking din ki ko
Idanzaka ci kaci kawai don sama mu a aje extra ko yaushe,
Badon yaso ba yadan dauki spoon ya fara ci a hankali,
Yamai yar jin nauyi da kunya duk da cewa daga shi sai Assalam ne a falon zaune,

🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
1⃣2⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA

Ejoma ce zaune a saman wani dutse dake ta, bayan dakunar kwanan su zaune,
Duk abin duniya yakai mata ko ina sai tunane take yi lokacin da Amina ke mata kalamai masu ratsa jiki
Har yake mata tayin shiga cikin addinin su yana cewa zai aure ta zai zamay mata tamkar uwa ko uba,
Dan siririn hawaye ne ya silalo mata daga cikin idon ta ya biyo ta kumatun ta,
Muryan Aminu ke mata yawo a kwakwalwal ta inda yake cewa bai taba ganin wata mace mai irin surar jikin ta da yaji yana so ba aduniyar nan in har zata amince mai shi yayi alkawarin aurenta,
Wa yan nan kalaman ne sukayisukayi tasiri a zuciyar Ejoma har ta yarda da maganganun Amina yai galaba akanta,
Don Alokacin tana ganin kamar cewa tafi ko wata mace dace, da masoyi,
Kamshin turaren shi na THE wanda ya hade dana JOJOBA,
Shiya dawo da ita daga tunanen nadamar da takeyi a lokacin,
Kamar ya wuce inda zai tafi amma kuma sai yanan yarinyar da irin yadda yaganta zaune a takure yasa shi jin wani irin tausayin ta alokaci,guda ya tsargu mai a zuciya,
Cikin yaren su na IBO yake mata magana, a cin taushin harshe,
Yake mai ce mata may ke faruwa da itane har hakan yafaru da ita,
Wani sabon hawaye tafara shirin sakowa saida ya dakar ta da ita,
Cikin daga mata hannu yace
Hy ,I don't want dis your cry, cry pls,,,
Just tell me what happen with u,
Nan takoro mai da duk abinda yafaru tunda ga farko, tana fadi cikin sheshekar kuka,
Yana tsaye hannu cikin Aljihu yana saye da farar suit, sai bakin wando,
Wata yar jar ,T-shirt ke ta cikin rigar suit din nashi,
Ya kafa farin glass a idon shi wando ,zaka iya ganin fararen idon shi kar daga cikin glass din,
Yakai wani dan lokaci a tsaye yana nazarin yarin wace duk taba shi tausayi,
Don yasan cewa wanan abin yana daga cikin destiny' din ta ne dama,
Bayan dan tunanen daya yi na yan dakikoki, sai ya dan nisa kadan wanda ko ita ba lalai ne in har taji ba,
Nobar wayan Aminu yabukata daga gurin ta, ba, bata lokaci ta bashi dama nobar na a kanta ta haddace shi tsab,
Tana mika mai bai tsaya ba ya juya kawai ya wuce abin shi, batare da yace ma mata komai ba,
Tuki yakeyi amma zuciyar shi jin ta yakeyi kamar zata fito daga cikin jikin shi,
Why some people are not trusted,
Why men's are cheating girls nowadays,
Some say girls are to blem too,
Amma shi a gurin shi ai mace abin tausayi ne sosai,,
Amma wasu maza sun dauki mace abin wulakantawar su duk lokacin da suka gama da ita,
Sosai maganar Ejoma ya tsaya mai a rai gashi ta bijirewa iyayen ta,
Shikuma saurayin yayi rejecting din ta at last, su kuma yan uwan ta mai makon suyi hakkuri da ita,sun ki sun dauko ta sun kawo ta nan ,,
Unguwar su jibrin ya nufa don KB baya,gari yana Abuja,
A wayar shi yakira,jibrin din yana maisheda mai cewa yana son su hadu,,
Inda yake yai mai kwatance gurin wani aikin hannu da yake koyo,
Joseph saida suka,sha kwana sundan yi tafiya kadan batare da ya waigo inda,jibrin yake ba ya ce,
Ko kasan Aminu Aliyu masuga,
Jibrin wanda tun shigar shi motar baiyi magana ba ya sai yanzu,
Yace dangida namasuga, ke nan ko don naji kace namasuga wanda ke uguwar jankidi,, ko ?
Joseph wanda yakai iyakar kaduwa yace ban san ko a ina yake ba,
Yana mai karya kwanar filin kwallo yake ce ma jibrin ina son ganin shi ne,
Ok kawai jibrin ya ce mai da yace hakana,
Nokia shi ya ciro cikin aljihun shi ya kira wani kanin shi Abdullahi,
Yake tambayar shi ko yasan inda Abdullahi yake zama,
Gurin da Abdullahi yai masu kwatance suka tafi,
Aminu yana zaune saman mashin din shi lipan wani abokin shi yana tsaye suna magana ya ji ana mai horn da mota abayan shi,,,
Abokin ne ke ce mai ga wata hadadiyar mota fa kamar suna magana nake ga,,
Aminu wanda ya juya bayan shi sai gefen shi kawai mutum zai iya hangowa,,
Jibrin ne ya isa inda su Aminu suke yai masu, sallama, nan yake sheda ma Aminu cewa,, suna son ganin shi pls,
Bayan Aminu ya saurari duk abinda jibrin ya tambaye shi ne,
Ba musu ya ce masu lalai yana tare da Ejoma sai dai ai ba wai lalai dole bane ace shi kadai ke taraiyya da ita,
Maganar shi taba Joseph mamaki, duk bayanin da suke yi bai yi magana ba sai kallon su kawai yake yi,
Daga karshe Aminu ya dan bugi kafadar jibrin yana cewa,,
Haba jibrin may zanyi da kafira ina zan kaita, kai min adalci mana kaima,.
Kasan cewa ba abinda zanyi da arniya kamar Ejoma a gidan mu,
Jibrin Joseph yace cikin wata irin murya mai nuna gajiya da sauraron magana,
Muje kawai dan Allah, is ok hakana,
Ido yabi su dashi har suka bace mai dagani,
Inda abokin shi yake ya koma yana tsuki yace ji mun wa yan nan fa wai akan zancen Ejoma Ebere ne suka zo suna bata min lokaci,
Ina ni ina KAFIRA ,,, ARNIYAR banza, wace ko kama ruwa batayi,
Dariya mai karfi abokin shi ya shiga yi don jin kalaman Aminu,
May kake ma dariya haka ne wai
Nuna shi da yatsa yayi cikin dariyar yace bata kama ruwa kai sai yanzu ka san da haka bata kama ruwa,
Lokacin da kake holewa da ita duk wanan baizo ma arai ba sai yanzu,
Malam kawai kayi JAHADI mukan mu je Onitsha musha bukin gaban dodon tsafi,
Kai dan Allah shere kawai da banzaye kaji ni duk in rasa wace zan aura sai ARNIYA
Kaifa mutumi dafa cewa kayi zaka musuluntar da ita ka aure ta to yanzu ina zancen musuluntar ya tafi,
Kai jafar ka ga alamar musulunta a,wanan yarin balle har kai zancen yinta,
Jafar yace gaskiya tunda tana,son ka musuluntar ta ba wani abubane mai wuya,
Kai malam kaga idar har kana ra,ayi zaka iya,don wanan ai taimako ne,,,
Ka jin tsoron Allah Aminu,
Kamar yadda baka so a diyar ka ko wata yar uwanka wallahi su ma haka ne wanan abin yake da zafi a gurin su,
Kamar ace kaunar ka ko diyar ka ta hada connection da Dan ,Ahalkitabi, ya zakaji a zuciyar ka,
Har kuma ace ya bata ma yar uwar ka, ko diyan ka,, shin zaka ji zafin abin da yai ma ko kuwa,???
Duk wanda yan dake, gurin su kace gaskiya da ciyo wanan abin hakan bai kamata ba,
Zafin maganar su ya ji don haka ya hau mashin din shi, ya,buga ya bar gurin cikin fushi,,,,

Da hannu guda yake tukin motar hannu shi guda yana yi yana shafan fuskan shi a hankali,
Wata bangararen zuciyar shi kuma maganar Aminu ce ke mai yawo a kai,,,
Tsawon lokaci suka dauka yana tafiya a hankali da motar,
Ba, wanda yai ma wani magana tunda suka fara tafiya,daga shi har Jibrin din,,,
Gidan Anty Dije kawai zuciyar shi taraya mai yatafi alokacin,,
Kofar gidan Anty Dije yai parking jibrin baiyi mamakin hakan ba don yasan cewa yakanzo gidan,
Sai a lokacin ya dan kalli jibrin din yace mai, ina son in,gaida sune,,,,
Bayan shigar su cikin gidan sun samu Anty da yara a falo suna karatun hadda,
Nan suka zauna suna kallon yadda anty ke wa yaran karatu cikin fasaha,,,,,
Joseph yana zaune gefe duk sai yaji yaran sun kara birge shi,,,
Saida suka gama ne Anty Dije ta waigo inda suke suka fara gaisawa,
Nan sukan dan fara hiran karatun yarw sai kuma na yanayi dake zuwa,,,,,, saidai hiran duk akan zafin da aka fara ne a lokacin,
Maryam maryam Anty Dije ce ke kwalawa maryam kira a wanan lokacin
Maryam wace ke daki tana gyarawa ta ansa daga can,,,,,,
Daidai kuma lokacin da wayar da ke a cikin aljihun rigarJoseph tai kara,
Aisha ya kike, ?maryam wace ke shigowa don amsa kiran Anty Dije
Idon shi, a lumshe yake magana yadafe goshin shi,
Batare da ta kalle su ba tace Anty gani
Baki gaida mutane ne maryam , ?
Wai may yasa baki iya gaida mutane, maryam, sai a lokacin ya bude idon shi da suke a lumshe,
Ya sauke su ga wace ta shigo falon
Cikin kwantar da murya kamar ta shagwaba, ta dan rusun na tace ina wunin ku, a kunya ce,
Jibrin ne ya amsa mata da lafiya lau,
Jin gudan bai amsa mata ba yasa tadan saci kallon shi inda yake zaune,
Dammmm gaban ta yafadi don gani wanan dan Christian din da tagani kuma gashi da shiga kamar ta yan musulumai,
Shiko ido yazuba mata kamar itace yake kallo, hakan yasa ta wani daure fuskanta ta ma,u,,
Don ita dai gaskiya bata ga abinda zaisa su anty su kama hurda dashi ba,
Sai muryan Anty Dije ya bugi kunnenta tacewa maryam dauko ma su abin sha dan Allah,
In har ba kunnenta ke mata karaba da,zata shigo kamar Aisha taji yace,
Amma kuma sai gashi taji yana kamar magana da maishi ta tsigar soyayya,
Tir tayi da Allah waddai da irin halin wasu diyan musullumai masu kokarin watsar da daranjan su da kima, soboda kwadai, suna, hurda da diyan kafirai,
Ruwa da goran kunun aya, tadauko hade da cups sai dai har yanzu wayar yake yi,
Ji tayi yana cewa ina gidan Anty yanzu haka,
Cikin wani irin mamaki ta kalli inda yake zaune, yadan kwanta Abayan makarin kujerar,
A cikin zuciyan ta tace ji wai Anty Allah ya tsari anty da zama antyn ka,
Kwantacen gidan tajiyana ma wace suke wayar tare,
Gaskia bazata iya zuba ma kafiri ruwa ba,don haka ta dan gware ruwan da cups din tafito,
Amma tana mamaki jin cewa, wai gidan Antyn shi, sai kace wani dan uwar mu, can Allah dai ya raba mu,
Tana tafiya ita kadai har tana tuntube,tana guna,guni, a fili ,,,,,
Ba,afi yan mintina ba sukaji sallama Aisha, tana sanye da wasu materials dinkin redemaid, tasa yellow,
Da wasu takalma masu tsini a kasan su, rataye da wani handbag na company Gucci,,,,
Joseph dake zaune yai mamaki kwarai da ganin Aisha har gidan Anty, don bai taba tsan manin cewa zata biyo shi nan ba,
Cikin girmamawa ta gaisa da Anty Dije duk da bawai sanin ta Anty Dije tayi ba ,sun gaisa a mutnce da ita
Sai ta juya inda su jibrin suke zaune tana mai kallon su, yar karamar harara ta sakar mai,,
Tace ance mun an gan ku,a tudun wada, lokacin Anty Dije ta mike don ta basu guri,
Joseph da sai a lokacin ya iya magana tun shigowar Aisha yace, Anty
Ina son zamu, wuce ,don ina son zanga Dad dina kafin gobe,
Ku bari mana kudanci a binci dan Allah saboda ku na kara yawan shi,
Da wata kasalaliyar murya ya ansa a hankali da kinbari wallahi mun gode,
Jibrin ne yace kai Man ka tsaya kawai kaci abinci don ko mun tafi ba abincin, zakaci ba acan,
Juyawa jibrin yayi yanamai kallon inda Anty Dije take tsaye kusa da kofa ya fara bata, labarin abinda yafaru da Ejoma yarinyar da yanzu haka tana gurin baban Joseph da zama,,,,,,,
Dawowa tayi inda ta tashi tana maimata Innalillahi ,cikin tashin hankali, da nuna damuwa,
Kai kawai take iya girgiza a lokacin saboda tana mamaki, yadda za,ace diyan muna musullumai suna bibiyar diyan arna suna lalata dasu,
Cikin sauri ta kalli inda Aisha take zaune sai wani irin salo takeyi a gaban Joseph,
Nan ta kara yin tir da irin masi rayuwa irin na Aisha saboda kwadan duniya ka wulakanta kanka,
Don dai shi wanda takeyi kashi baima san cewa tanayi ba don ko kallo ta baiyi ba tunda tashigo,
Wanda ma nunawa yayi da bai ji dadin shigowar nataba
Ita dai Anty Dije fatan ta koyau she Allah yasa Joseph ya gane hanyar gaskiya,
Sai a lokacin maryam tashigo falin cikin shirinta na isalamya,
Kallo daya ta watsa masu inda suke gabadayan su,
Wata uwar tsana da takaicin ganin su ya rufto cikin zuciyar ta
Annurin fusakarta duk yagushe, ta bata rai, tana mai murtuke fuskan ta,tankar taga wani mugun abu,
Duk wanda ke falin yaga irin mugun kallon da maryam ke watsa masu a lokacin,
Amma sai suka dauka kila halinta ne hakana kawai,,,,,,,

Barci yake yi amma kuma yana mafalkin garin da yafi kauna lokacin da yake yaro,
Watau garin mahaifiyar shi da yafi kowa kaunar ace za,a tafi wanan garin,
Kusan wata biyu kenan ko yaushe yana cikin ganin wanan nahiyar a mafarkin shi ko kuma tunane,
Don haka yanasa wa ranshi son zuwa ya dibo yar tsohuwa mai munhinmanci tilo guda data rage masu,
Watau mahaifiyar maman su wacr tun suna yara aka hana su zuwa gurin ta cewa wai ita witch ce
Inji dangin uban su, haka yasa busu saba da ita ba sam,,,
Yadda yaso shine sai yaga yadda zancen Ejoma ya kai karshe sannan zai koma Lagos, gurin sanar shi,
Amma sai elders sukace sai nan da karshen wata zasu kara zaunawa,
Don haka yabata gudu taboye yadda zata iya taimakawa rayuwar da abin bukata,,,,,,


Gari ya nuna alamar hadari kamar ,ruwan sama, zai iya fadowa kowani lokaci,
Zaune take da dauri zani a gaba duk da tana da riga a jikinta amma daurin gaba tayi,,,
Wake take tsinta a wani tire maidan fadi, sai wakan su na yan church take rewa cikin wata murya maiban tausayi,
Cikin sauri take aikin duk da ta tsufa,
saboda yanayi, da garin ke ciki don ruwa na iya zubowa ako wani lokaci
Wani kare ne kwance gefen benci da take zaune, daganin shi zaka ce ko shi kadai ake kiwo a gidan saboda koshi,
Jin karan motar da karen yayi yana nufo gidan su shi yasa shi mikewa tsaye yana haushi cikin karfi,kamar zai tashi sama,
Horn din mota ce duk ya ruda gidan yar tsohowar dake zaune a lokacin tana kokarin mikewa don jin yadda karen ta ke ta haushi alokacin, guda.
Jin horn din mota ya tabbatar mata da cewa a,kofan gidan ta ake horn, din
Sam bata kawo cewa bakon ta bane don rabon da ta, ga wani yazo gurin ta har ta manta, lokaci,

10 / 84