Furen Juji Book Compelet Zainab Makawa

Author :  Zainab Idris Makawa Category :  Read Hausa Novels

Chapter   24 / 84

69K to 72K   out of 251.8K words

Yaso ya koma gurin Ibrahim don yai mai bayani amma sai kuma ya kasa saboda gajiyar da ya kwaso,,
Don haka baima,sauko kasaba kamar yadda yasaba, indan yadawo yakan je gurin mama su dan yi hira,
Don kawar mata da zaman kadaici duk da yasan Ejoma tana iya kokarin ta da yar tsohuwar,
Washegari, musalin karfe takwas na safe, Joseph yasamu ya sauko tare da takardun Ibrahim na jiya a hannun shi,
Dakin nashi ya nufa don yakai mai yasamu ya cika idan zai fita yau sai ya tafi dasu ya mayar,
Tun daga yar hanyar da zata sadaka da dakin Ibrahim zaka ji muryan shi rarara, yana karanta suratul Maryam,
Jin maryam mu da yake ambata aciki yasa Joseph tsayawa guri guda cif,
Yace a hankali maryam in ,Qur'an, ?
Ji kawai yayi yai kundunbale fadawa dakin yaga may yaron keyi haka,
Ibrahim wanda ke zaune kamar a tsugune can wani dan sakon gado yana rike da Qur'an din shi yana mai karantawa,
Jin kamshin turaren Joseph dayayi a dakin yasa shi dan bude indon shi da suke a lumshe,
Don ya tabbatar da kamshin da hancin shi ya shako mai na Joseph din shine agaban shi ,ko,kuwa,?
In ko har shi din ne to ko jiya ma da,dare da ya jiwo wanan kamshi tabbas shi din ne a gurin duk da bai bude ido yatabatar da hakan ba,
Daidai ya kai A,ya" yadan dakata kadan yana mai cewa Sadakallahul,Azeen,
Ina kwana yai mai acikin yaren su na IBO, Joseph ya dan daga mai hannu yana mai cewa,sorry for disturb pls,
Takardun ya mika mai yace mai, ya cikia inda bai gane ba yasa may shi yai mai bayani,
Daga haka yajuya kawai yabar dakin yana jin wani irin abu kamar kasala tana lu,lube shi,
Sai zakakkan muryam Ibrahim ke mai yawo a kunuwa shi kamar a ciki yake wanan karatun,.
Lumshe idon shi yayi yabi bayan kujerar da yake zaune yadan kwanta,,

A hankali maryam ta ajiye, plate din da ta debo abinci, agaban Anty nata,
Wacce ke kwance saman dogon kujerar da ke cikin falon nasu,
Anty Dije tadan dago kai kadan ta kalli maryam wace ke kokarin juyawa don komawa dauko ma yar nata ruwan sha,,,
Cikin murya ta wanda je jin jiki Anty tace wa maryam ,
Maryam ba,zan iya cin wanan abincin ba don sam bakina bai min dadi wallahi,
Cikin dan marairaice murya Maryam tace anty dan Allah ko kadan ne kidaure ki danci, zaifi rashin cin da bakya, son yi,
Da taimakon maryam Anty Dije tadanci abincin kusan spoon, hudu, gana biyar ta mayar tana mai cewa ta koshi,
Bazata iya karawa ba haka don ji take tankar zata amaye dan wanda taci,
Gudun kada tai amai Maryam ta kyale yar nata tana mai tatara plate din zuwa kitchen,
Ido Anty tabi maryam dashi tana mai jin dadin irin kaunar da yar uwar nata ke yawan nuna mata ita da yaran ta,
Ringing Tone din wayar Anty Dije ne ya karade gidan nasu a lokacin,
Da sauri maryam ta isa inda,wayan take tana ruri, don ganin mai kiran yar uwar nata,
Yusuf Joseph tagani baro,baro a screen din wayar,
Kurawa wayar ido tayi har saida ya katse don kan shi,
A hankali Anty tadan dago kai daga inda take, kwance tana son tasan kowaye ke kiranta ya katse,
Don tana,son kaunar nata ta fada mata kowaye a layin,ke,kiranta,
Tana kokarin aje wayar ne wani kiran nashi yakara shigowa again
Dole ta nufi inda Anty take kwance, da hannu take mata tambayar waye akan layin,
Joseph tace tana kokarin kara mata wayan a kunen ta,
Da hannu taimata alamar, ta dauka kawai sai ta maida kanta saman hannun kujer a hankali,
Cikin muryan mai,kama da ta maijin kasala take magana,
Hello, ina wuni ?
Mai wayar batada lafiya ,
Juses crisis,
Dif maryam tayi tana mai cewa wa,iyazu,billlah,
Jitayi tankar ta aje wayan do haushi,
Sai jin shi tayi yana cewa may yasa may ta haka,
Zazzabine ke damun ta yau kwana biyu ke nan,
Jin wa,iyazu,billah da tafada dazu yadan sosai mai rai don yasan kalmace ta nuna wani tsari ga tsanar, abu,
Don haka yanzu sai yadan gyara harshen shi da cewa ayya sorry fa ina gaisheta pls anjima zan bugo mata,
Kagin ma ya kashe har maryam ta kashe wayar bin wayar yayi da kallo,
Sai mamaki kuma yake a ran shi cewa may yasa musulmai ba su iya boye felling din su in suka ji an ance Juses,a gaban su,
Maryam ko a hankali ta juyo gurin Anty tana fada mata abinda yace mata,
Yinin ranan duk a kwance anty ta ti shi saboda yanayin jikin ta duk ba dadi,
Ganin tana wahala da yawa yasa maryam bugawa yaya illiya waya tana sheda mai abinda ke faruwa xa yar uwar nata,
Wace duk kwanakin nan akwance take bata jin dadin jikin ta,
Ga wani amai dake zo mata yanzu duk abinda taci sai ta fitar dashi koda ruwa ne,
Hakalin Maryam ya tashi sosai cikin dare da Joseph yabugo muryan ta kamar na mai kuka take mai magana,
Tana sheda mai yadda ciwon ke matsawa yar uwan ta yanzu sosai,
Shiru yadan yi nawani lokaci har maryam din na,,zaton ko cewa ya kashe wayan ne,
Tace cikin siririyar murya, hello,,
Yace ina jinki kunje asibiti, ta girgiza kanta alokacin kamar yana ganin ta tace a,a
Saidai zuwa gobe insha Allah zamu tafi yaya yau ya bugo waya yake cewa mutafi goben,
Ok to barin yi magana da shi Illiya din tukun 'I will call you back,,,
Ok tau nagode tace tana mai kokarin aje wayar a lokacin shikuma yana mai ce mata ina Assalam yana lafiya ko?
Cikin kosawa da yin wayar tace mai yana lafiya sai anjima,
Itace kuma still dai ta,katse wayar kamar yadda ta yi dazu
Yai shiru yana dan mamakin irin halin Maryam na rashi son mutane
Yasaki ajiyar zuciya yana mai kara nazarin ta,
Tuna wa yayi da zancen kiran illiya don haka nobar shi ce ya kira,,
Bayan sun gaisane yai mai jajen ciwon matar shi sai, ya,kecewa
Dama ya bugo waya ne don ya tambaye shi ko yana iya tura mai doctor lawal yadiba matarshi
Don yadda akace mai tana jin jikin har ta kasa daukar waya daya kirata,
Ya, illiya yai murna kwarai da wanan taimakon da Joseph yai mai na turawa har gida a diba mai matar shi,
Saida Doctor Lawal ya iso gidan sanan Joseph yakira yake sheda masu cewa gashi nan shigowa,
Mamaki ne yakama maryam sosai don ganin cewa yasan yadda shari,ar musulunci yace ayi,
Am.a kuma da,tai tunane saitaga babu mamaki don yana tare da su jibrin yau da gobe dole yasan komai,
An mata allurai dakuma yan magunguna, sai fitsarin ta da akace akai gobe,
Bayan fitar doctor dakamar yan min tina sai,gashi ya kara kira yana tambayar ta
Ta girgiza kai tace ban san may doctor yace ba yadai mata allura,
Nan yai mata sada safe yana mai jaddada mata cewa ta tabbatar da cewa Anty tana shan maganin ta,
Joseph yaso ya shivo saidai yana tsoron irin masifar da tsohon shi ya za,zaga mai,
Inda ya bashi umurni da cewa indan har bashi yace yana son yazo ba kada ya fara yashigo garin kwantagora,
Tunda badon su ya haife shi ba da zai dinga kashe masu kudin shi abanza hakana,
Fada sosai yaiwa Dan nashi lokacin bukin KB da sukayi inda labarin komi yazo kunen Mr Ema din a lokacin ne yai kamar zai daki Joseph din don haushi,
Jikin Joseph a sanyaye don badamar zuwa yadiba halin da Anty nashi ke ciki, don gudun masifar mahaifin shi wanda sam bai son hurdan shi da yaran varin da yake amfana dasu,
Hannu yasa yadan shafo sanjen fuskan shi da ya kwanta mai lub a fuskan,
Ya furzar da yar iska mai dan dumi daga bakin shi,
Ibrahim ne yafado mai arai don haka yatadashi inda yai mai shatar mota zuwa kwantagora da kayan dubiya irin ta marasa lafiya,
Anty Dije tayi mamaki kwarai da irin kayan da Joseph ya bayar ,akawo mata tundaga Lagos har KG,
Lemo, Abarba, Ayyaba, Apple, kwakwa, carrot, water millow, pears, da,sauran su bar manja da garin can saida ya siya mata,
Waya anty tasa aka bugawa Joseph tana son tsi mai godiya na taimakon da yai mata, ga likita ga kayan marmari, da yayo mata,

Likita ya tabbatar da cewa Anty Dije tana dauke da shigar ciki na wata biyu da da kwanaki,
Maryam tafi kowa murna da wanan labarin cikin, wanda har uwar mijin ta tafara zance wai ya karo mata tunda anty tabar haihuwa,
Da sun dan samu matsala dasu yanzu zasu fara mata gorin taki haihuwa kuma ta hana auri wata,,,,


ZEEE MAKAWA
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
2⃣9⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA,,,


Yan uwa musulumai ina mika gaisuwa gare ku ,akan wa yan nan yaran makaranta yan garin misau da ke cikin jahar Bauchi da suka samu harin mota ta hanyar su zuwa kano ziyarar Arewa 24,wanan satin da yagabata suka mutu su ashirin ta re da malaman su,,
Masoya TAKARI novel da FUREN JUJI ina fatan za muyi masu adduan fatan samun Rahamar ubangiji, tare da mika ta,aziyar mu ga yan,uwa, da, iyayyen wa,yan nan yara, Allah ubangiji kasa Aljannan Fiddausi tazama makomar su,👏👏👏👏

Mahaifin , Ibrahim Abdulsamad, yaji dadin yada yaga dan shi ya koma cikin dan kankanin lokaci,
Bakamar yadda suke zube a cikin gari ba da babu mataimaki,
Babu wanda ma yasan cewa suna cikin wani halin bukata na rashin yan uwa da galihu,
Yana ji yana gani matar shi ta gudu mai da yan shi mata, zuwa kasan su,
Wanda bakomai yasa shi kyaleta dasu ba sai tsabar yawan talauci dake cin shi,
Ki abinda zasu ci tunda yai gobara shagunar shi suka kone kurmus,
Amma sai yara,daya daga cikin musulmai wanda zai taimaka mai da wani abin,
Gashi har zuwa yanzu yan uwan shi na da suna kawo mai tayi akan ya koma akidar shi tafarko,
Babu komai acikin wanan sabuwar akudar da yadauko, illa wahala,
Dariya kawai yakan masu yabasu amsar cewa shi yabar su ke nan har abada
Bazai kara dawowa cikin banyar bata ba saidai ya mutu a hakan,
Girman da yaran shi suka farayi ne yadan rage mai wahalar don suna zuwa yin dako a bakin kasuwa sukawo dan abin da suka samu ayini asarrafa,
Ko shi Ibrahim saida bukin KB da akayi ne yasan cewa suna da alaka da Joseph,,
Lokacin da yaga irin yadda Joseph ke yi agurin yazo yana fadawa mahaifinshi cewa baisan cewa IBO bane saida yaji yana yare acikin waya,
Abdulsamad yai dariya inda yakewa diyan shi bayanin ko ya suke da Joseph,
Nan ne ibrahim yace zai je gurin shi ya ziyar ce shi yagani ko za,a samu wani cigaba anan,
Maihaifin na Ibrahim baiki ba don yasan kowaye Joseph zai iya taimama wa ibrahim din,
Sai ko gsshi cikin ikon Allah ibrahim din yazo cikin kamata alheri don bai taba zaton cewa yaron zai can za cikin dan lokaci guda haka ba,
Ga sakon kudi har dubu hamsin anbashi yakawo wa mahaifin shi tare da tsaraba,
Kwanan shi biyu da zuwa inda yakoma shedawa Anty Dije zai koma,
Sako tabayar akai ma Joseph din wani robber da akai sild din shi
Sai kuma kilishi cikin envelop, mai yawa cikin wani babban leda tace Ibrahim yakai wa Joseph,

Bakaramin mamaki Joseph yayi ba lokacin da Ibrahim yagabatar mai da sokon da Anty Dije ta aiko mai dasu,
Dambun nama ne cike a roban sai kuma kilishi mai yawa,
Daga kilishin har Danbun Joseph yarasa wani yafi dadi daga ciki,
Sai mamaki yakeyi yana kada kai cikin jin nauyi, kamar a gaban anty din yake,
Shi yana gani kamar ta ksshe kudin da yakai dubu dari akan wanan abin,
Bai daga daga gurin ba sai da ya kira ta acikin waya yana mata godiya daga karshe ma yarasa may zai ce mata,
Mamaki kwarai anty tayi don jin yadda yake zabga mata godiya akan dan abinda baikai yakawo ba,
Shida ta lodo mata tsaraba har saida ta ba makwabta da kuma gidajen su ita da mijin ta,
Amma,shi gashi ko dubu ashirin bata kashe mai ba yata zabga godiya,
Shin shi Joseph din nan wani irin zuciya gare shi ne wai gashi da bawai, yasan kaidar zumunci ba ne a ddini,
Amma yarike ta tam kamar wata yar uwar sa ta ji,
Ita dai fatan ta dai,akullun Allah ya kebo Joseph, yadawo cikin Islam's,
A hankali Joseph ya maida tsarabar anty wani abincin shi na daban koda yaushe yana amfani da abinshi kadan kadan,

Wani irin gurnani take yi wanda har a fili zaka iya jin yadda takeyi wanan karar,
Joseph dake shirin hawa sama yagama kallon national news, a TVC,
Da sauri yai hanyar dakin na maman choima wace ke faman wani irin Gumza takar ana shirin yankar ta,
Da karfi Joseph da Ejoma ke kokarim daga ta daga kwanciyar da tayi tana fidda wanan sautin,
Cikin wani irin kara tabude idon ta tana mai cewa Joseph's da karfi,
Firgigit take kallon su da sauri ta rugumo Joseph din daga jikin ta,,
Sai kuma ta fashe dawani irin kuka tana magana maiban tausayi, cikin kuka,
Tana mai cewa,Joseph they want to carry u away from us,woooo,
Joseph da ya rungumo tsohuwar zuwa cikin jikin shi, yace mata sowaye,
Cikin kuka tace bata san su ba amma tana yawan gani su,,a tare dashi acikin su,, koyaushe,
Sai yaune babban su ya ce har da ita zai wuce in,har tana rike shi,
Shine wanan gumzar da take tayi cikin barcin ta da ihun da take ta kwasa yanzu,
Joseph yadan tallabo kan kakar tashi, zuwa jikin shi yana mai lalashin ta
Tunda yaga cewa tadan kwantar da hankalinta yasamu ya sata kwantawa don ko zata samu barci,
Yamike zuwa dakin shi jiki a sanyaye, zuciyar fam da tunane kala kala,
Ashe haka wanan yar tsohuwar ke wahala idan tace mai tayi wanan mafarkin,,
Hankali shi yatashi matuka yana tunanen may ke shirin samun shine haka,
Washegari, tunda safe Joseph yabar gida zuwa gidan wani babban pastor da ke zaune a cikin Lagos,
Saidai bayan bayanin da Joseph yai mai sai ya umarci da azo mai da wnan tsohuwae wurin shi
Joseph yakoma yazo da maman choima acikin shirinta na irin manyan matan IBO,
Pasto ya riko hannun mama zuwa yan wasu lokota,
Can sai ya sake yadan daga kai yana mai kallon Joseph wanda ke zaune gefen su saman wata far kujera, yana mai rike habar shi da hannu guda yana dan shafa, gemun shi,
Idon da pastor yadan tsura mai baisa Joseph ya canza daga yadda yake zaune ba tun farko,
Pastor yadan kada kan shi yai yar gyarar murya wanda yasa duk suka kura mai ido,
Don jin irin bayanin da zai masu gamay da mafarkin da takeyi,
Mama inji pastor kada ki damu wanwn bawani abin damuwa bane danki zai zama wani abu ne nan gaba shiyasa kike ganin wan nan abin,
Amma,zai bata holy water wanda zata dinga wanke fuskan ta dashi har zuwa sati,
Idan ta kara wanan mafarki sai su dawo, duk kan su,
Sukai godiya Joseph ya kawo kudi yabawa pastor pastor yaka da kan shi alamar aa ba,zai karba ba,
Yace we are just send to help, the, neediest,
Yai masu addu,a a baki dayan su inda sukai sallama dashi zuwa gida,
Tun,daga wanan ranan maman choima ta fara amfani da ruwan holy water, kamar yadda pastor ya umurce ta tayi,

Shiri yakeyi sosai saboda tunda safe yake son takama hanya zuwa kano don dibo wasu kaya da wani tsoho yai mashi tallan kayan company,
Duk shirin da,Joseph keyi hankalin shi na gurin kakar shi wacce ta nuna batason zuwan shi garin kano sam,
Saida ya gama,shirin tsab ya sauko cikin shigar kananin kaya,
Kayan ya karbe shi sosai don ya fitar mai da surar shi tsab,
Karfafan namiji mai duk wani siffa mai nuna karfi daga jikin da namiji
Saidai Joseph ba mutum bane mai son magana don haka ko murmushi da wuya kaga yayi ta, kasafai,
Guda guda yake tako hannu shi guda na acikin ajihun wandon shi guda kuma yana dauke da yar briefcase din shi,
Direct saman kujerar da maman choima take zaune ya nufa inda shima yazauna gefen hannun kujerar,
Yadan langabo kanshi

24 / 84