Author : Zainab Idris Makawa Category : Read Hausa Novels
Daya daga cikin driver s din da suka zo daukan shi yakar bi wata yar case da ke hannun shi,
Bawani bata lokaci su,kabar airport din shi da wa yanda suka zo tariyan shi,
Sannu a hankali yakarewa gidan shi kallo gidan da yakewa kallo tankar wani sabon guri da bai taba zama ba,
Saboda gyaran da ya turu da kudi akai mai,
Anan falon ya zube saboda yana tare da gajiya, ba abin da yake bukata sai ya dan watsa ruwa ajikin shi,
Ko zaiji dan karfi karfi ajikin nashi, kafin ya samu dan abin da zaici,
Motsin da yaji ne ya sanya shi saurin daga kai, don ganewa idon shi kowaye,
Hakan yai daidai da Ejoma, wace ke sauko daga wani dan steps da yafito wani part na gidan,
Da saurin ta tazo daniyar rungumar shi kamar yadda su ka saba idan yadawo koda gurin aiki ne,
Da sauri yadan jaye jikin shi daga gareta amma yana mai,mata murmushi,
Dan yaron dake rike a hannun ta ya daga sama cikjn wasa yana zagaya da shi,
Sauke yaron yayi yana mai kallon Ejoma wace ke saye da wani bakin buje da yafitar mata da surar bayanta baro,baro, gashi dan guntu, daidai iya katarar ta,
Ejoma ce tafara magana bayan taga ya, sauke yaron daga daga shin dayayi,
Tace brother we don base, woo,
Shima murmushi yai mata yana cewa where my grandma ?
Grand mother dey for village since, tree months ago,
Murya kasa kasa yake tambayar ta ya akai haka ,
Ejoma tadan tabe baki tukun sai tace,
You know Dad no dey allowed her to go to her church,
A dan tsora ce ya dago fuska cikin mamaki da jin mamakin zancen ta,
Saikuma ya maida mamakin nashi zuwa dan murmushi mai sauti, saboda tunawa, da sanin kowaye mahaifin shi,
Fuska kumshe da murmushi yace ma Ejoma is alright, i, will go and seen soon,
Daga haka ya haura zuwa sama inda dakin shi yake don yadan watsa ruwa,
Cikin daga murya Ejoma ke cewa brother your food is ready on the table,
Yakai wani lokaci a sama sannan ya sauko daidai lokacin da Ibrahim shima yashigo gidan, don taron shi,
Duk atare suka taru suka ci abinci, gabadayan su,
Tsab ya mike yashiga wani dan bayi dake makale a cikin makewayin,
Alwalar sallah azuhur yadauro alokacin amma saboda gajiya nan ya tsaya a falo saman sallaya,
Addu,oin da yajeyi bayan sallah ne ya gabatar alokaci har tsawon wani lokaci,
Brother are still bearing the Muslim,
Idanu ya zuba mata don mamakin kalamin ta, saboda yaji abinda tace kamar a mafarki,
Don haka ya shafa addu,an shi ya fuskan ce ta, da kyau,
Gyaran murya yayi yace mata dama ana canza addini ne anyhow,?
Sai ta girgiza kanta tace ba haka bane kawai dai taji Dad na cewa evils spirit din da suka shige shi har ya juya zuwa Islam,
An, kore su dakarfin addu,oin pastor's masu yawa daga cikin pastocing su,
Wani iri Yusuf din yaji a cikin zuciyar, wanan maganar ya kasance mara misaltuwa agare shi,
Shin dama ashe har yanzu Dad naga bakar shi na cewa sai ya canza addinin shi da yake ra,ayin yi a rayuwar shi,
Gaskiya zai dauki wa Dad duk wani mataki da yakamata yadauka wanan karo,
Ai bashi kadai bane, dan shi yafara zama musulmi, da zai ce ba zai hakkura ba ,
Koda kuwa Dad din zaiyi barazanar kwace mai duk wani dukiya da ya mallaka a rayuwar shi batare da yabar mai koda kwandala ba,
Ya tuna da labarin da Abdul samad yabashi, na,wani matashi , da yai zamani da manzon Allah S,A,W
Maisuns Mus'ab Ibn Umair, matashine, mai ji da kanshi a cikin garin makka,
Matashin ya fito daga wani family mai karfin arziki sannan,sannan ya kasance dangata sosai daga duk wani matashi na zamanin,
A wancan lokacin kaf samarin Makkah suns jin jins mashi wajen ado, don ko turaren ma dayake amfani dashi alokacin abin kallo ne,
Sannan mahaifiyar shi takasance mai tsananin sonshi wanda hakan ya haifar da shakuwa mai karfi gaske a tsakanin su,
Tufafin da Mus,ab Ibn Umair yake sawa, da takalmin shi masu matukar, tsadane so sai,
A lokacin da manzon Allah SAW ya fara wa,azi da kira ga mutanen makkah akan subi addinin Allah, watau musulunci,
Yawan wa,azin da yake saurare daga Annabi yaji ya gamsu zai shiga addinin islama.
Hakan yasa ya fuskanci tsanani da azaba da rashin galihu,
Inda yakoma yakassnce tankar almajiri, duk wanda yaganshi bazai gane shine shiba
Dan yadda ya koma ma abin tausayi don hatta suturar jikin shi duk sun yayyage,
Sai watarana mahaifiyar shi tace ya kai Mus,ab kadawo vikin addinin mu kafita,wanan addinin na islama, da kashiga
Amma sai Mus,ab yaki suka dinga azabatar da shi azaba mai tsanani, amma yaki ya tsaya akan addinin shi na islama,
Daga karshe ya koma gurin Annabi Muhammad, (SAW),
Ya hakkura da duk wani daular duniya da ake kwadaita mashi, anan
Yusuf yanisa ya waiga inda yake tsaye a bakin window,
Yace a ranshi kida Dad zai kwace mai duk wani abu da ya mallaka bazai fita cikin addinin islama ba,
Shi yanzu yasan cewa yafi karfin duk wani barazana da mahaifin shi zai mai akan dukiya,
Kwana biyu kawai yayi da hutawa, ya shirya don zuwa ya dibo, kakarshi wace bai san halin da take ciki ba a yanzu,
Ba karamin tausayi matar yake ji ba a matsayin ta na wanda, ta rage mai yake gani kamar uwar shi,
Tana zaune ta mike kafa a saman wani tabarman roba, a gefen da dan inwa yakai acikin gidan nata ,
Sai ganin shi tayi kamar a mafarki don sam batayi tsan manin cewa zata kara ganin shi arayuwar taba ,
Tadade rungumay dashi a jikin ta tana kuka tana wani gwalanci irin na yare,
Sai kuma komay ta tuna tasake shi da sauri tana ta tatabashi kamar tana tuhumar ko ba shi bane a gabanta,
My child are still in that religion ?
Mumushi yayi ya jawo goshinta ya man,na da nashi yace mata
Even you mama you will joined me, very soon
Dan tura shi tayi baya yawuce tangal, tangal kamar zai fadi,
Dariya tabashi a yadda yaga tanayi don daga hannun ta tayi tana wani kewaya shi a saman kanta tana cewa over my death body,
Komawa tayi ta zauna tana wani bubuga kafa wai ita tayi fushi,
Direct wuce yayi zuwa cikin dan falon ta na ginar kasa wanda saboda tsufa har yana batun zubewa,
Photo mahaifiyar shi ce yai tozali da shi, wace ke saye da wani zanin irin na matan IBO,ta daura wani dankwali daurin gwagwaro,
Murmushi takeyi da aka dauke ta kamar zatai magana
Yadade yana kallon photo yana maiji dama ace ta musulunta ka fin ta mutu,
Shigowar grandmother, yasa,shi barin gurin zuwa saman tsofin kujerun dake falon,
Itama zama tayi saman kujerar dake gab dashi, tana mai mai kallo cikin da muwa,
Shine yafara magana yana mai tambayar ta may yasa ta dawo kauye da zama,
Bayan tasan cewa babu wani wanda zai kula da ita anan yanzu,
Yace ga gidan shi can abirni babu kowa aciki mai yai hana taje can ta zauna,
Saida mama tadan waiga kamar akwai wani gidan wanda zai ji abin da zata fadi alokacin,
Tadan kara gyarazaman ta har kusa dashi tace,
That your father is very wicked,
He can killed person, woo
Nan take sheda mai cewa bayan tafiyan shi taji mahaifin nashi na waya da wasu cewa a kama Joseph ai masa duk wani horo da ya dace dashi don yadawo cikin Christianity,
Murmushi yai mata don dama yasan cewa shine ke turowa ai mai wanan wulakancin,
A ranan Yusuf bai yarda ya kwana wanan dan kauyen da yar tsohuwar ba dawowa sukayi tare,
Inda taga duk gidan ya canza mata saboda gyare,gyaren da akayi wa gidan,
Sosai gidan ya canza mata cikin dan lokaci har ta rasa gane ko ina ne part din ta na da,,
Ganin Ejoma da tayi tazo taron ta yasa ta gane cewa lalai agidan shi suke,
Wanan karon sosai ya shirya ma shiga garin na kwantagora
Badon komai ba sai don ya tunkari mahaifin shi wanda ke ta yi mashi bita da kulli,
Motorcine har guda uku yatanada don wanan tafiyan,da yake son yi kafin ya fara harkokin gaban shi,
Saidai wanan karon ba,a gidan mahaifin shi zai saukaba kamar yadda ya saba,
Hotel lafiyayye aka kama masu tun kafin su iso garin,
Har abincin da zasu ci an tanadar masu shi, KB ne yai wanan hidimar,
Zaune take tana kwalliya a bakin mirror saboda tana expecting din zuwan A,Adin ta,
Muryarda taji yana sallama tuni zuciyar ta, ta tsinke
Zabura tayi saye a dan tsorace, tadan saurara ko kunnuwar take mata karya,
Bashi bane a zahiri don sam ba su tsan manin cewa zai zo a wanan lokacin ba,
Muryam Anty Dije ce ya kara tabbatar mata da cewa shi din dai ya shigo,
Inda taji Anty na tacewa sannu da zuwa Yusuf
Kaine tafe babu ko labari, zuwa balle a shirya ma,zuwan naka,
Wani murmushi yayi mai sauti yace bana son ku wahala ne ai shiya sa ban fada maki ba,
Sigar dayake magana kawai zai tabbatar ma da ya kara samun canji a rayuwa,
A,hankali yake karasowa zuwa inda anty take dauke da Abubakar a hannun ta,
Ya saye da wani yadi mai laushi baki ajikin shi sai wata yar jar hular dara dayasa wa kanshi,
Gadan gadan yanu yau,fi inda take da yaron dagani duk hankalin shi na gurin yaron, wanda bai taba gani ba, sai
Cak yadauki Abubakar yafara dan wasa dashi ,daidai gitowar Maryam wace kamshin ta kawai kawai, zai saka gane tafito,
A hankali ta iya furta mai sannu da zuwa,daga haka tasa kai da niyar fita kawai,
Gabantane yafadi saboda ganin yadda Yusuf ya canza gabadaya cikin lokaci guda,,,,,,,
ZEEE. MAKAWA
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
4⃣1⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA,
Yusuf ya canza gaba daya ya wani murje yayi fari sosai da yar jiki daidai shi,
Wasa ya keyiwa Abubakar yana cewa wanan little friend din bai sanni ba , ama baka kai abokina kyau ba,,
Muryan ta na rawa ta iya furtawa Anty ta cewa zata dan fita,
Sai,dai kuma Yusuf din yadan tare hanya ta daidai inda zata dan wuce, zuwa waje,
Yaro nai yai sallama yace wai ana sallama da Maryam a waje,
Maryam da ke shirin fita hanya kawai take nema takumaji muryan Anty ta nacewa dan Allah maryam dan dauko wa Yusuf kujerar roba a waje,
Maryam wace dama a cike take don tasan cewa A,A yagajine har ya turo yaro,
Don yana zaton ko ta manta dashi a waje saboda motocin da yagani a kofar gidan su yasa,shi, zaton baki sun masu yawa ne,
Batare da tai magana ta juya tanufi inda kujeru suke aje a,dan wani kwanar da fridge din su na waje yake,
Kanta ta kawar gefe har ta isa gaban shi,ta ajiye mai kujerar, cike da jin haushi ta aje mai daidai inda yake tsaye,
Yana yawan dagula mata kwanciyar hankalin ta idan ya na a gari,
Ya zauna a hankali yana mai cewa bissimillahi, azu,bikalamatillah tammah
Kafin Anty ta takara sata yin wani abin da saurin ta tabar, gurin,
Tana shan kwana suka hada ido da Yusuf yasakar mata wani tsadadden murmushi wanda duk duniya ba mai mata irin shi, sai Yusuf amma ta kasa gane ko ta may ye,
Saidai da yake tasan cewa, murmushi wani part ne na rayuwar shi sai kawai ta share zancen
Kanta kawai takawar gefe cike da kara jin haushin shi,
Kafin ta karasa ficewa sai ga muryan Anty Dije na cewa,
Ki dauko mai ko ruwa mana maryam kinsan cewa, ba wuta falon da zafi,
Murmushi da yafitar wanan karon mai sauti ce don har Anty taji shi,
Komawa tayi cikin wani irn bata rai kamar bata taba dariya ba arayuwar ta,
A cikin tire ta jero, kayan shan har da da su cup,
A gaban shi ta ajiye kayan, shan tasan cewa idan bata zuba mai ba Anty zata kara kwafsa mata dole badon taso ba ta dan duka don ta zuba mai,
Kamshin turaren BUSSHIRAH da ta shafa ya gauraye ma hanci har saida ya yar ajiyar zuciya,
Muryan yaron dazu ne ya ratso kunnen su, yakara sallama yana cewa wai yace tazo don ba dadewa zai yi ba,
A lokacin Maryam tai yunkurin ta mikewa, sai ji tayi yana cewa ta karbi Abubakar daga hannun shi, pls
Sosai suka shaki numfashin juna tare da hada idon su a lokaci guda,
Maryam ce tai saurin kauda kanta gefe tana mai jin wani irin abinda bata taba jin shi ba arayuwar ta,,
Babu shiri tabar gurin da sauri daga haka tafita zuwa kiran da A,A ke mata,
Sai zuwa dare, ya shirya zuwa gurin mahaifin shi, saboda bazai iya kwana a garin batare da ya tafi ya gan shi ba,
Mr Emanuel yana zaune tare da abokan shi su biyu da suka zo mai hira,
Kasan,cewar shine mai hali acikin su dan sauran basu kai shi arziki ba ko kadan,
Duk idan an fara labaran NTA shiga yakeyi don kallo da sauraro,abinda kasa ke ciki,
Don haka sauran abokan hiran nashi suka mike zuwa gidajen su,
A kofar get din gidan suka ga shigar su Yusuf, tare da guards din shi,
Motocin suka bi da kallo inda hankalisu yabasu cewa shine yazo gari,
Sunji haushin barin gidan da sukayi batare da ya iske su a ciki ba,,
Yusuf din ne ya fara fita daga cikin motar da yake acikin ta, yadan dade tsaye da kofad motar rke a hannun shi kamar mai nazarin wani abu
Saidai a cikin zuciyar shi addu,a yake yi na neman rinjaye daga ko wani irn masifa da zai riska, agidan
Tunda motocin suka tsaya Samuel dake zaune a saman dining table ya mike tsaye,yadan leka tagar falon nasu don yaga kowaye,
Cikin murna ya ce "Ah, brother Joseph,, har ya mike kamar zai tafi sai sukayi ido biyu da mahaifin nasu wanda ya watsa mashi harara dole ya koma ya zauna,
A, cikin takon shi mai kama da ta kasaita, yashigo falon
Idon shi cak ya sauka ga na mahaifin shi wanda alama ta nuna cewa, ya cika fam, a ida yake jira kawai yake yi ua fashe,
Da harshen su na yaren, IBO ya gaida mahaifin nashi, wanda ke zaund daure da wani katon zani na atamfa da akayi shi kamar buje,
Kallo guda Mr Ema yai wa dan nashi yagane cewa har yanzu yana nan daram a cikin addinin Islama,
Mr Ema wanda tun dan nashi bai shigo ba ya nasa cewa zai falfale shi da masifa in har yana cikin Muslim har zuwa yanzu,,
Amma suna hadda ido sai yaga yaron nashi ya kara mashi wani irin kwarjini a fuska,
Har yaji cewa bazai iya ba amma dai karfin hali irin na kafiri, balle Mr Ema mai hali kamar na kafiran farko,,,,
Cikin kakausar murya, yafara wa dan nashi magana kamar haka,
Wai kai may kake nufi da zuwa gurin mu bayan kaba mu baya,
Yanzu mai kazo bida a gurin mu da har za ka,shigo min gida kai tsaye batare da izini na ba
Addinin naku bayace mutum bai da ikon shiga gidan wani batare da izini ba,
Joseph kabani mamaki kabani kunya a idon duniya,
Duk so da kaunar da na nuna maka acikin diyana sakkaiyan da zakai min ke nan,
Karasa addinin da zaka shiga sai addin musulunci addinin da yake na yan ta,addah,
Kafita kabar min gida na muddin kana cikin wanan addinin baza mu taba shiryawa da kai ba,
Duk da nasan cewa kana ganin kamar a yanzu kana da arzikin ka to ina son ka sani cewa gidan maina da kake harkoki dashi a Lagos na karbi abina,ko
Sai katafi gurin yan addinin ka suyi maka,contribution din sadaka subaka jari idan zasu iya,
Yakare maganar ko fadane yana huci kamar zai fashe,
Saida Yusuf yaji mahaifin nashi yadajatar da masifar da yakeyi ne,
Sai ya saki wani irin ajiyar zuciya lokaci guda yadago ida nun shi a hankali ya dubi uban,
Yace Daddy kayi hakkuri da abinda kagani that is my Destiny,
I can't change it,
Wasu kwalaye guda biyu masu kyau ya ciro daga cikin wani dan leda,