Furen Juji Book Compelet Zainab Makawa

Author :  Zainab Idris Makawa Category :  Read Hausa Novels

Chapter   5 / 84

12K to 15K   out of 251.8K words

kiran abokan shi daya bayan daya suna gaisawa,
Daga karshe ya kira KB inda suka dan dade suna hira akan ginar da ya bashi kula dashi na yan marayu
Yai mamaki kwarai da jin dan kudin da aka kashe wa ginan,
Inda ya yaba da irin saukin da aka samu a wurin kayan aikin unlike irin yadda anan inda suke harkoki basu tabuwa,
Don haka yai alwashi a cikin zuciyar shi zai gyara gidan mahaifin shi da suke a ciki very soon,
Kafin su kashe wayar KB ke tanbayar shi ko yaushe zai shigo KG, din,
Yace mai sai nan da sabon wata daidai lokacin da zasu fara yin shirin programs din su na wasan Daba da za suyi,
Sun dan jima a wayar suna hira sanan suka yi wa juna sallama, suka, kashe wayar ,,,
Su na sallama da KB yakira Daddy shi inda a lokacin daddy yana zaune tare da yaran shi suna hira,
Mr Emanuel yaji dafin kiran da Joseph yai mai a wanan lokacin,
Don dama shima yana da niyar kiran shi akan maganar ginan da yaji cewa wai yana wa wasu hausa wai da sunar tai mako,
Taupa Joseph yace a cikin ran shi watau abin duniya baya boyuwa kenan,
Can kuma yace ai ba mamaki don kusan shiya kuda suke da mutane dole wani zai iya fadawa baban nashi,
Muryan Mr Emanuel ce tadawo dashi daga tunanen da yakeyi inda yake cewa,
Joseph u, no dey hear word,
I always warn u about dis people,,
Jin uban ya ci gaba da fada ne sosai yasa Joseph yai sauri katse shi da ce,
Dad, am doing all dis b,cos of u
Saboda kai ke zama ko yaushe a cikin su indan har mun nuna cewa bamu tare da su a fili a baza mu samu biyan bukatar mu ba,,
Ajiyan zuciya Mr Emanuel yayi don jin kalaman dan nashi,
Shima ta fanin Joseph din sanyayar ajiyar zuciya yayi,
Don jin ya ciwo kan tsohon na shi cikin lokaci guda,
Bai tsaya wani dogon magana ba yai sallama da dad din, ya, kashe wayar
Don gudun wani sabon magana,
Rigingine ya ke kwance saman gadon sai tuna nen maganar Dad yakeyi,
Yasan cewa za su kara kwasar rikici da tsohon nashi,
Idan har tsohon yaji cewa zasuyi wasan nin matasan kasar kwantagora a cikin su har da shi Joseph din wanda yaba da gagarumin gudun mawar shi a taron da za,ayi,,,,
Cikin, gwanin ta yake tukin motar shi daidai lokacin da ya ke kokarin shiga get din gidan su,
Mahaifin shi da aboksn shi, suna zaune saman wasu benci guda biyu, da ke harabar gidan,,
Cike da sanyi jiki yake tunda yai arba da su zaune suna ta dirkan giya sai shewa sukeyi a tsakanin su,,,
Nan da nan maganar Jibrin yazo mai arai inda yace komai darajan mutum idan ance yana shan giya,
Kimar shi da girman shi ya zube ke nan a idon duk wanda ya ganshi a hakan,
Don haka sai yaji a, lokaci guda duk wanda ke gurin kimar su ta zube mashu a idon shi,,
Yan samarin da ke gefe suna karta suka zo suka tare shi cikin murna da jin dadin ganin shi,,,
Buth din motar shi ya bude masu suka fara jidan tsarabar da yazo dashi zuwa cikin gida,
Inda dattawan ke zaune suna dirkan giya yanu fa don kwasan blessing,
Kirari wani daga cikin su ke mai irin kirarin yan gidan su da ake masu a can kasar su,
Jin kirarin yadan sashi yin yar murmushi daga nesa saboda yana son wanan kirarin na kakan su da ake masu,
Karasowa yayi inda suke yadan yi kamar ya duka yace masu barkan ku da gida,
Gabada yan su sukace mai blessing my child,
Ya hanya ya ya kabaro lagos yai dan murmushi yace daga Abuja yake shine yace bari ya kara so nan,,
Wani dan gajere mutum daga cikin su yadan kalle Joseph din daidai lokacin da yake zuba bommi a cikin wani cup,
Yace waiting dis boy want, in dis town, no b last month i saw him,,,
Baban Joseph da ya sha yai tatil yace cikin murya tsatsaye,
Na, me send for him wooo, i wan tell him about d white men,
Joseph da yaga kamar shirmay suke zubawa ga warin giyar bommin da su ke sha duk ya cika mai hanci,
Sai cewa yayi sai anjimar ku yana kokarin shigewa,
Wani daga cikin su ya dan yafito shi da hannu yana mai alamar yazo ya zauna
Wani daga cikin sune ya iya bude baki yana cewa come nd join us my son,
No tnxs kawai yace yana mai kokarin mikewa tsaye yabar gurin
Tunda ya shiga gida baiyi marmarin fitowa ba saboda yan dattawan dake waje suna holewar su,,,,
Sai sha daya na safe ya ke shedawa su KB yana cikin gari,
Duk sunyi mamakin jin cewa yana gari don basu sa rai cewa zai shigo very soon haka ba,,
KB ne ke ce mai ya na tafe yanzun nan,
Sai Joseph din ke ce mai ya bari har zuwa yamma don dama wani program yazo yi a church din su,,,,

Church kan ya ciki makil yau saboda kiran gagawa da akai ma duk wani mabiyin wanan church din
Kamar irin su Joseph da iyayyen su ke ciki yazama dole su zo wannan taron da ance mai ma,anace taron,
Wasu turawane ke perching kamar kuma shawa da umurni suke ba sauran mutanen,
Inda suke neman hafin kan duk wanda ke cikin addinin da ya kawo gudun mawa mai tsoka
Indan an hada kudin daga baya sai su shiga daji inda kauya wa suke su fara masu wa,azi da kuma jan ra,ayi da abin duniya, har su samu galaban jan ra,ayin su
Ihu da murnan jin wanan shawaran church din ya rude dashi, saboda suna ganin cewa zasu iya cin galabar yan kauye da,dama a, hakan,
Kafin wani lokaci an fara yawo da ture ana karban gudun mawan gurin jama,a,
Wani dan kyamushashen bature ya kara tashi yace
Wani hanya kuma guda da zasu bullowa al,umma dashi ita ce
Suna da wani baiwa da zasu iya kara jan ra,ayin mutane da shi cewa,
Duk wanda baida lafiya za su warkar dashi indan har yaji sauki to ya zama dole ya bi akidar su,,,
Sannan su kara tabbatarda cewa har wa yan dake a ciki idan su na da wata cuta zasu iya zuwa a warkar amma da sun ji sauki ya zama wajibi a kara masu mukami acikin church,,,
Joseph najin haka ya mike kamar mai waya a zuciyar shi yana cewa yan yaudara ne kawai da cuta,,,,,,,

ZEEEE MAKAWA,,,,,,,,
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
6⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA

Zaune take gaban mirrow tana dressing kusan duk abinda mace zata bukata na fente fuskan zamani ta na dashi a gurin,
Dogon rigar atamfa ce ajiye saman gadon ta gefe hade da dan kwalin shi da gyalen shi,,,
A hankali tadauko rigar ta zura a jikin ta, ta gyara tsayuwar rigar cifcif a jikin ta ,
Ta mika hannu ta dauko dankwalin ta fara daurawa a kan ta,
Batafi minti shidda ba taga komai takara feshe jikinta da turare,har zuwa gyalenta,
Kinsan da gyale da hijab sun fi daukar kamshi a kayan mace,
Saboda hatsari mace ta dinga shafa turare a jikin ta yana kawo wa mata breast cancer so sai, wlh,,,,
Amma idan kin dan sa wa top din ki is ok ko ina ki kabi zaki na kamshi so sai, har na wani lokaci (pls be aware)
Wasu takalma ta jawo wanda sukayi matching colour da gyalen ta, da yan kunen ta ,,,,
Tsaye take gaban mirrow tana kare wa kanta kallo,
A, lokacin wayar ta yai kara cikin sauri ta dauko murmushi tayi don ta san ta bata lokaci,
Haba Aisha kin san fa cewa ance ba makara don Allah kada kisa a rufe get ba mu shiga ba,
Daidai lokacin ta rufe kofar dakin ta, don gudun kada yan kan,nen ta su shiga mata cikin dakin suyi mata barna,
A kofan gidan nasu ta iske Amina kawar ta cikin motar saurayin ta suna jiran ta,
Baka jin komai a motar sai sautin kida dake tashi kamar kune mutum zai fashe,
Duk inda suka bi dule a waige su don jin,karar kidan motar da ya hayhake ko ina,
Tunda ta shiga motar gaisuwa kawai ya hadasu da saurayin Amina
Ba su tsaya ba sai wani mating wuri da aka killance a rubuta da manyar haruffa, kamar haka,
SAFARA MOTEL,,,,,,
Sai wasu yan kananin gloves da ke haska wanan rubutun yana bada launi kalakala,
Duk saurin da sukeyi sun makara don sun samu an rufe get, ko,,,
Komawa Aisha tayi baya tadan jin gina bayan ta da mota, da sukazo da ita,
Tunda har an rufe get yanzu dole sai ta samu partner da zasu shi ga,
Sauriyi Amina ne keta faman zirga zirga bidan wanda yadace ya hada Aisha Sanda da shi,
Sanin halinta na zama first class ya sa bai yi gigin hada ta da kowa ba,
Wata mota ce ta dan no inda suke tsaye tunda ganisa kaji engine din motar kasan yar lafiya ce,
Rangerover sport, ce ta dan no tun daga nesa aka kashe mai ido da hasken motar,
Duk da bai san kowaye ba aciki yasan wanda yasan shine,
Don haka yai tsaye guri guda har na cikin motar ya fito
KB ne yafara fitowa ta gefen mai zaman, banza,sai kuma Jibrin wanda ya balle, marifin motar baya ,ya fito,
Tunda ga nesa ya gane su KB don haka yasan cewa,
Yanzu za ai solving din problem din su, ma,ana Aisha ta samu irin da zai hada su,
Joseph ne yafito karshe sanye yake da dinkin shadda mai ruwan makuba ,
Sai sarkar gold da zoben gold din guda biyu a hannun shi,
A hankali yake takowa har zuwa in,da su KB suke tsaye da Lawal abokin su,
Hannu sukayi da lawal din inda ba bata lokaci lawal ke fada ma su bukatar shi,
Ya na mai nuna Aisha inda take tsaye, cikin second duk suga wai amma banda Joseph, wanda kamar ma bai gane may ake nufi ba,
Inda lawal yaci gaba da fadin sun bar pass din su, a gida ne gurin sauri,
KB ne ya waiga inda Joseph ke tsaye yana kallon ya ce,
Man wanan taimakon ka ne, pls
Cikin nuna rashin ganewa yake kara tambayar su, komai zai mata nan dai KB yakara mai bayani,
Kafadar shi dan daga alamar ba damuwa ai,
Shigowan su a cikin dakin taron ya haskaka so sai don mai MC yai announcement din shigowar su kamar yadda idan wasu sun shigo ake cewa ga yan kungiyar kaza nan sun iso,
Kallo ya koma gare sai kuma dan kus kus yatashi a gurin kamar yadda aka saba, inda anga kirstan na shiga cikin musullumai adinga a queuzing din su ta hanyar da bai dace ba,
Wanda yin haka najawo ma su sanyin gwiwa, so sai,
Mafi yawan mutane sai mamakin Aisha sanda sukeyi a cikin su ke don sanin cewa sunan ta na cikin fitattun yamatan da ke tashe agari,
Kuma gashi kayan ta sundanyi shigen kala da na jikin Joseph din wanda shi bai ko dago da hakan ba,
Zaman su bada wani dadewa aka fara program din bukin,
Ana aka fara gudanar da abubuwan da aka tsara a gurin,
Zaune Joseph yake yadan tokare habar shi da hannayen shi dukka biyu,
Yana kallon yadda ake guda nar da bukin abokin su, wanda yai aure,,,
Wani can wanda Joseph din bai sani ba yazo ya ja KB da hira har suka bar kujerar,
Jibrin dake gefe a zaune wayar shi taikara bayajin may ake cewa don haka ya tashi yadan koma can ta waje kadan ko zai ji kiran,,,
Yanzu,daga Aisha sai Joseph ke zaune, a inda aka tanadar masu, suke zaune,
Daga inda KB yake suna magana ya jiyo muryan MC na cewa ana bukata Joseph da Aisha su fito su taya ango farin ciki,
Saida KB ya dafe kai don yasan cewa da wuya Joseph din ya fito tunda baida masaniyar hakan,,
MC nata nata abinda akace text kb yayo mai cewa yafirmta dashi da yari yar nan suyi rawa,
Kamar kada ya tashi sai yatuna cewa bazai kyautawa angon ba inda har bai fita ba don haka ya fara mikewa batare da ya kalleta ba yace mata sai ki tashi mu fita ko,
Ba wani rawa sukayi ba sosai amma anji dadin fitar nasu don Joseph ya nuna kulawar shi ga ango,,
Wasu yan mata dake ge fe zaune suna kallon yadda ake ta
Su ka fara yan suraitai kamar haka,
Au dama wanan ba musullumi bane ke inji wa ya fada maki,
Dayar tace bakiji lokacin da ake cewa ana son Yusuf Joseph yafito tare da,Aisha sanda
Sai gudan tace kai amma anyi harasa wallahi guy kamar wanan kuma bai sallah,
Dayar tace gaskiya ni saima kawai naji haushin shi ya kamani wallahi, ita kuma Aisha don kwadai sai wani shige mai take ta yi,
Wace ita ce cikon ta hudun masu hiran da tun da suka fara zance bata ce kala ba,
Tace kai ku dai na daukar wa kan ku wahala ma,
Iyaka,ku da shi kuyi mashi fatan alherin shiga cikin islama indan har yana da rabon shiryuwa, Allah yasa yagane gaskiya yadawo hanya,
Sai ta farkon tai caraf ta ce a haka ?
Wanan ai yai nisa baya jin kira, in bashi ba ai tun yana yaro da ya musulunta, ko,,,,,
Ita dai wace bata maganar sai cewa ta yi ai abin daga Allah ne kawai, in Allah ya nufe shi da shiryuwa saiko ya shiru, yadawo hanya,
Haka dai kusan ko wani kujera suke ta zancen su kamar yadda gurin buki ya tana da
Kai kana kallon wani wani yana kallon ka,
Ganin cewa dare ya fara yasa Joseph yai su KB magana akan cewa su zo su tafi don shi baya yin dare sosai a waje,
Don duk haka tarbiyar yaran IBO suke duk ganin kada su basu yarda,su kai karfe takwas na dare waje,
Wana na daga cikin irin tarbiyar da suke wa yaran su,
Idan kuma sana,a ce bakin karfe shidda andawo gida ke nan daga gurin sana,a,
Saidai kuma tun karfe bakwai na safe anbar gida ke nan zuwa gurin bidar kude, (Allah ya kyauta)
Wanan haduwar da Joseph yayi da Aisha itace silar haduwar su,
Don tun a gurin da ta ce ya ara mata waya takira kawar ta don su wuce tasamu nobar shi,,,
Da zai tafi ma lake mai tayi akan ya bata lift zuwa gida saboda dare yayi a cewar ta,
Anan yabar su KB daga shi sai Aish sanda suka kamo hanyar zuwa gida,
Da kwatance tai ta yi mai har suka iso gidan su, Aisha din,
Koda ya Parker motar shi bai ce mata komai ba sai jiran yakeyi tafi ta yasamu ya wuce
Ita ta tsaya wani yanga kamar wace bata da lakka ajikin ta
A hankali ta dan waiga inda yake tana cewa nagode fa,sai wani lokaci ke nan kuma ,
Kai ya kada mata yana mai cewa No ba matsala ai ,,
Tana fita yafigi motar shi da karfi yabar uguwar zuwa, gidan su,,,,,,,,

Gudu yake shararawa a motar shi tanyar ta zuwa kudu, don kirar da yasa na gagawa daga abokan sanar shi saboda meeting din da zasu yi don kara wa mai farashi saboda harajin da gwaunati ta saka masu,
Shi kadai ne a cikin motar sai kidar da ya sa nawakar wani dan yaren su inda yake wa egwaii of Benin kirara,
Wayar shi dake gefen shi tai babirashon, hannu ya mija yadauko wayar hankali shi na saman titin kadan don yafara jin kamshin okene,
Ganin bakuwar noba yayi acikin wayar shi dan mamaki ya baiyana a fuskan shi kadan,
Don gani bakuwar nobar kuma yasan cewa wanan wayar sai special mutanen sa ke kiran shi da ita,
Kamar ya aje saidai ya dauka yana mai karata a kunen shi,
Muryan mace yaji tana mai

5 / 84