BUZU BOOK1 COMPLETE Hausa Read Novels By Aysha Cool.txt

Author :  Aysha Cool Category :  Hausa Read

Chapter   55 / 64

162K to 165K   out of 190K words

ɗan lokaci, ba tare da ta yi tsammani ba ya yi magana.

"Duk na yi ƙoƙarin ɓoye matsanancin farin cikin da na shiga, da na ji za ki haihu. Na kasa ɓoye damuwar da na shiga, da na ji na rasa abin da yake cikinki
Ban san dalili ba kawai na ji ina matsanancin son, abin da ban taɓa gani ba, kuma yanzu na rasa shi, ba tare da na yi tsammanin hakan ba".

Jiki a sanyaye Nana ta ce "Sayyid idan kai ka ce haka, ni na ce me?"

Ya ɗan girgiza kai ya ce "Ba za ki gane ba" ya tashi ya naɗa rawaninsa, ya fice daga ɗakin.

Nana duk ta gaji da kwanciyar, ta yinƙura ta fara mayar da kayan wardrobe ɗin da ta watso.
Ta ɗaga labulen window, dan iska ta ƙara wadatar ɗakin, kawai ta hango Siyama ta fito, sanye da doguwar riga da ɗan ƙaramin mayafi, ƙonuwar hannunta, ko gama warkewa ba ta yi ba.
Sai dai Nana ta ga Sayyid take tunkara.

Ganin tana tunkaro shi, ya sanya ya sunkuyar da kansa, daga kallon gurin da take tahowa. Sai dai tana ƙarasowa inda yake ta tsaya tare da yin murmushi ta ce "Sannu da ƙoƙari" ya jinjina mata kai, ba tare da ya kalli inda take ba.

"Amm dan Allah magana nake son mu yi"

Ya ɗaga kai ya kalle ta cikin mamaki.
Ta ɗan sunkuyar da kanta ta yi murmushi, ta ce "Dan Allah a abubuwan da suka ɗan faru, na rashin kyautawa da na yi maka, nake son ka yafe mini na san na yi kuskure, ka yi haƙuri"

Ya ɗaga idanunsa ya kalle ta, ya mayar da kansa ya sunkuyar.

"Ka yi magana mana" ta yi maganar cikin iyayi.

Jinjina kai ya yi, yana ƙara kawar da kansa gefe.

Ta sake cewa "To ai ba zan gane ba, idan ka haƙura, ka yi magana"

"Ya wuce"

Ta saki murmushi ta ce "Na gode sosai" ta juya ta koma cikin gida tana murmushi. Tabbas Buzun nan, irin mutanen da idan ka ɗora kana relationship da su, za a ga ka haye, ya haɗu ta kowane ɓangare. Ta yi maganar a zuciyarta.
Nana rasa abin yi ta yi gaba ɗaya, ta ji ƙirjinta tamkar ta haɗiyi kibiya, wani abu ya tsaya a tsakanin maƙogwaronta da ƙirjinta.

Ta zauna ta yi shiru, kawai ta ji sallamar Siyama. Nana ta ɗaga kai ta kalle ta, sai dai ta kasa magana.

Siyama ta zauna a kusa da ita ta ce "Ƙawata kwana biyu ba ki zo ba"

Nana ta kalle ta ta ce "Kina lafiya?"

"Ashe kuma ba ki da lafiya? Ya jikin naki?"

Nana ta kalli Yusra ta ce "Ya aka yi ki ka san ba ni da lafiya? Waye ya gaya miki?"

"Sai an gaya mini, ina ganin komai ai. Ko kin manta gidanmu ne nima? Allah ya baku wani."

Nana ta ce "Ina cikin damuwa, dan Allah kar ki dame ni"

Yusra ta yi murmushi ta ce "Na sani, amma kin san faɗa ya kaure a tsakanin Ƙaisar da dattijo? Kuma duk a kan ki?"

Nana ta ce "Waye dattijo?"

"Wanda ya ke kawo muku ziyara, da ke da mijinki, idan ba ki yi wasa ba, abu mara daɗi zai iya faruwa. Kodayake kar na yi shishshigi, gurin shiga hurumin da ba nawa ba. Amma abubuwa na daf da rikicewa. Me ma ya faru kafin ki yi ɓarin cikin jikinki?"

Nana ta ɗan yi shiru tana son ta yi tunani, amma ba ta iya tuna komai ba, tana ɗagowa ta nemi Yusra ta rasa.

Damuwa da rashin sanin abin yi, ga takaicin abin da ta gani ya haɗu ya sanya, ta tashi ta sake watso kayan wardrobe tana gyarawa.

A cikin kayansa, ta ci karo da wata 'yar ƙaramar jakar fata, mai kama da laya, sai dai ta fi laya girma, da ya kan saka a wuyansa wasu lokutan.

Ta yi shiru tana kallon jakar, ta yi ƙoƙarin ta ga ta ina za ta buɗe ta, ta ga mene ne a ciki, amma ta kasa.
Ta ajiye ta, ta ci gaba da gyaran kayan, ta sake ɗaga wata riga, sai ga kuɗi turmus a ciki, na Nigeria da na Nijar.

Har ta kai hannu za ta ɗauka, ta waiwaya ta gan shi a tsaye yana kallonta.

Ta kalli kuɗin ta kalle shi.

"Wannan kuɗin fa?"

"Nawa ne?"

Ta kalle shi ta ce "A ina ka samu?"

Wani irin kallo ya yi mata, jin tambayar da ta yi masa.

"Me ki ka ce?"

Ba ta ji ko ɗar ba, ta sake maimaitawa.

"A ina ka samu?

"A ina ma samu? A gurin Habu. Ai ya gaya miki sana'ar da yake yi ko?"

"Dama shi ya gaya maka, na je gidan kenan?"

Ya girgiza kai yana mayar da kayansa ya ce "A'a"

Da ta tuno yadda ta ga ya kalli Siyama, wani narkakken baƙin ciki yake tokare mata zuciya, kamar ta kwaɗe shi ko ta samu ta huce.

*****

Alhaji Zailani ne, tare da Alhaji Fatuhu, zaune a kan fararen kujeru a wata farfajiya.

Fuskar Alhaji Fatuhu, cike da ƙwarin gwiwa yake duban Alhaji Zailani ya ce "Zailani, babu komai dan Allah ka karɓi shugabancin nan, na san za ka iya. Da a bawa wani da ba a san yanayin amanarsa ba, ba gara a baka ba?"

Fuskarsa ɗauke da damuwa ya ce "Haba Alhaji Fatuhu, yaya za a yi kana abokina, aminina a yi maka wannan cin kashin, kuma ka ce na karbi shugabancin nan na yi yaya da shi?"

"Wallahi za ka iya. Na fi jin tausayin ƙanan 'yan kasuwa, idan aka bawa wanda bai dace ba shugabanci, za a karya masu ƙaramin jari"

"Ƙananan 'yan kasuwar, da su suka yi wannan bita da ƙullin, da rubuta takardar lallai a sauke ka daga kan shugabancin nan, su ka ke tausayawa?"

Alhaji Fatuhu ya yi murmushi ya ce "Nima da ƙaramin ɗan kasuwa ne, kafin Allah ya kai ni matsayin da nake a yanzu. Kuma na san ba dukkannin su ne, su ka yi mini haka ba. Ni dai fatana dan Allah ka karɓi tayin riƙon ƙwaryar shugabancin nan da aka yi maka" Alhaji Fatuhu ya ɓata lokaci sosai da sosai, kafin ya shawo kan Alhaji Zailani ya amince zai karɓa.

*****

Gaddafi tuni ya koma gurin neman khɗinsa, saboda takaicin abubuwan suke faruwa a gidansu, ya fara damunsa.
Baba ƙiri-ƙiri haka ya zuba ido ya yi shiru, ba ya iya cewa uffan, sai dai ya zuba ido a kan lamarin gidansa. Sai ma dai idan an dafa a zuba a ba shi ya ci. Sosai al'amuran gidan su Nana, suka fara canzawa kullum sai an ɗora abinci sau uku a rana saboda hidimar da Jamila take yi da su. Ƙarewa ta saka ana ta yi musu gyare-gyare a cikin gidan.

Babban abin da yake damun Hajiya Sa'a da Jamila, shi ne yadda take ta ƙoƙarin janyo ta, cikin ɗaya mummunar ɗabi'ar da suke aikatawa ta lesbian.
Sai dai Jamila ta kafe da kai da fata, taƙi amincewa da hakan.
Sai da Hajiya Sa'a ta yi mamaki, saboda a ƙulumboton da ta yi wa Jamila, babu yadda za a yi ta iya kaucewa duk wata buƙata da ta zo mata da ita, amma ta kasa galaba a kan Jamila.
Duk wani shashashanci da suke yi tana kallo, amma sam ba ta ji abin ya kama hankalinta ba, balle ta yi sha'awar aikatawa.

Ta fito harabar gidan tana shirin tafiya, sai ga Mus'ab ɗa ɗaya tilo ga Hajiya Sa'a. Yana ganin Jamila ya tsaya. Duk da ba shiga harkarsa take yi ba, amma ta yi ƙoƙarin tare shi daga shiga cikin gidan, ya yi mummunan gani.

"Ina wuni?"

"Lafiya ƙalau Jamila. Ya ki ke?"

"Lafiya ƙalau Alhamdilillah. Amm Yaya Mus'ab ko za ka ajiye ni a hanya ne, ba na jin daɗi"

Ya yi murmushi ya ce "Me zai hana? Bari na kai wa Mummy saƙon nan"

Da sauri ta ce "A'a ai bacci take yi, ta ce kuma kar a tashe ta"

"Ok to mu je na ajiye ki" ta yi gaba ya bi ta a baya.

*****

Nana kuwa ita ma a wannan karon, basar da Sayyid ta yi, ta ƙi kula shi sam. Shi ma ya maze ya share ta.

Baccinta ya yi nisa sosai ta ganta a daji ita kaɗai ƙwal. Ta ɗaga kanta ta ga wani ƙaton tsuntsu yana shawagi a saman kanta.
Ba ta tsorata ba, ta ɗan ja numfashi ta ce "Ƙaisar laifin me na yi maka, ka zaɓi ka hukunta ni ta wannan hanyar? Me ya sa za ka zama dalilin zubewar cikina?"

Tsuntsunan nan saukko ƙasa, ya yi girgiza Ƙaisar ya bayyana. Ya zauna yana fuskantar ta ya ce "Komai ma kin yi mini, babu abin da ba ki yi mini ba, abin da ya dace nake yi"

"Ba ka tsoron Allah Ƙaisar, ba ka tsoron Allah ya kama ka da hakkina, abubuwan da ka ke aikata mini na cutarwa.
Kai ka yi mini, wannan tsohon ya yi mana, mijin nawa ma na fara daina gane kansa. Ya fara ƙoƙarin cutar da ni"

Ya ɗan kalli saman bishiya sannan ya ce "Babu abin da ban gaya miki  ba ai. Amm kin tuna abin da na nuna miki, Alhaji Zailani yana yi wa abokinsa? Da gaske ya faru a zahiri. Kuma tsafi gaskiyar mai shi, domin kuwa al'anura sun fara juya wa Alhaji Zailani baya. Nan zuwa wani ɗan lokaci zai rasa komai nasa. Lafiyar sa da dukiyarsa."

Cikin matsananciyar damuwa Nana ta ce "Dan Allah idan ka na dama ka yi wani abu a kai mana. Ka tona abin da aka yi masan"

Ya girgiza kai ya ce "Ba ma shiga abin da babu ruwanmu, ko warware wani abu da aka yi wa wani, muddin ba yarjejeniya aka yi damu, aka bamu damar yin hakan ba. Zan iya taimakonsa ne kawai bisa amincewar ki, da kuma umarnin ki. Zan gaya miki inda abin yake ya saka a je a tone, ko kuma ki je ki tone. Idan ba haka ba nan da kwanaki uku rak za a tono ƙwarangwal ɗin yaron nan, a kuma yin wani tsafin da ita."

Har Nana ta motsa baki za ta yi magana, sai kuma ta fasa, dan tana amincewa a taimaki Alhaji Fatuhu ba ta san me zai biyo bayan hakan ba, ka iya tabbatar da buƙatar Ƙaisar a kanta.

AREWABOOKS

Kasancewar ba ta salla, ya sanya har gari ya waye tana bacci.

Bayan ta yi wanka ta rasa abin yi, ta ɗebo kayan wankin ta, ta shiga banɗaki ta wanke. Nasa dama Habu ne yake zuwa ya ɗauka.

Ta gama, ta saka hijjabinta, ta ɗaukko bokitin, ta fito daga ɗakin. Yana kan kujera a daf da gate ɗin, yana aikin dafa shayi, gefensa ga radio tana yi.

Ba ta kula shi ba, ta zagaya baya, ta yi shanyar kayan nata. Ta fito ta ja ta yi turus tana kallon ikon Allah.

Siyama ce a tsaye, da ɗan ƙaramin flask a hannunta. Nana ba ta san me take ce masa ba, ta ga ya sauke rawanin fuskarsa ya saka hannu ya karɓi flask ɗin, ya yi magana.

Kawai ta shiga ɗaki, a ƙofar banɗakin, ta jefar da bokitin jin wani irin matsanancin ɗaci yana taso mata.

Ta cire hijjabinta kawai ta tsaya ta riƙe ƙugunta, ta tsaya tana jiran ya shigo, amma bai shigo ba, zuciyarta ta din ga raya mata, yana can su na hira da Siyama.
Kawai ta buɗe ƙofa ta shiga banɗaki, sai dai ta rasa uban abin da ya kai ta banɗakin ma. Ta gama tsayuwarta ta fito daga banɗakin.

Tana fitowa ta gan shi a tsaye, da flask ɗin a hannunsa, ya nufo ta zai yi magana, ta riga ta ɓarar da flask ɗin. Farfesun kifi da dankalin ya tarwatse a ƙasa.

Ya kalli gurin ya kalli yadda take huci, zuciya ta yinƙuro shi, sai dai ya ga Ƙaisar a bayan Nana, ya zubo masa ido.

Ya haɗiye wani abu, mai ɗaci. Ya kalli Nana ya ga yadda idonta ya rufe, ta fara ƙoƙarin wuce shi ta fita. Ya riƙe ta yana ci gaba da kallon Ƙaisar.

Ya kwantar da Nana a kan katifa, idanunta a rufe sai hawaye da yake fita, ta gefen idonta.

Ya durƙusa ya gyara gurin ta ɓarar da abincin.

Ya sake kallon yadda Ƙaisar ya jingina da bango, ya tsaya a kan Nana.

"Tun da ka yi abin da ka yi, ya kamata ka bani guri" Ya yi maganar yana kallon inda Ƙaisar yake.

"Gurin ka na zo ne? Idan ba gurin ka na zo ba, sai ka ƙyale ni"

"Ka zubar mini da ciki, kuma saboda rashin kunya, ka zo haɗa fitina a tsakaninmu"

Ƙaisar ya yi murmushi ya ce "Ina mamakin yadda Aljani yake shiga al'amuran bil adama har haka. Kai ka fara lalata cikin, ni kuma na zubar da shi."

Sayyid ya shafi fuskarsa ya ce "Waye Aljanin a tsakanin ni da kai?"

Ƙaisar ya ce "Ba da kai nake ba. Ka san da wanda nake"

Buzu ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Ka gaya mini, wane ne ni? Daga ina nake? Kuma suwaye iyayena? Me ya kawo ni ƙasar nan?"

"Ba ni za ka yi wa wannan tambayar ba, zuwa yanzu na san ka bambance tsakanin ni da shi"

"Haka ne, na banbance, yanzu ka tafi ka bani guri, ka bar ni da matata"

"Ba zan tafi ba"

Buzu ya durƙusa ya kwance rawanin kansa, ya cire rigar jikinsa, ya ɗago Nana da take cikin yanayin gushewar hankali.
Ya fara cire kayan jikinta, tamkar an aiko wa Ƙaisar saƙon mutuwa ya murtuke fuska.
Bai tsinke da lamarin ba, sai da Sayyid ya rungume Nana yana sumbatar bakinta.

Jikin Nana ya din ga rawa, tana fatan ta saka baki a maganganun su, amma ta kasa, tana ganin duk abin da yake faruwa, amma tamkar an ɗaure ta, ta kasa motsa ko da ƙaramin yatsanta.

Da ƙyar ta fizgo numfashi ta tashi a zabure, ta ce "Sayyid" ya taso da sauri daga inda yake zaune ya nufo ta.

Ya kasa magana, ita ma kuma ta kasa cewa komai, sai rarraba ido da take yi, ta yi zaton mafarki ne, amma ta ji ɗakin yana ƙarnin kifi, ga kuma flask ɗin da ya shigo da shi.

Da ƙyar ta ce "Ina wanda ku ke magana da shi?"

Ya kalli ɗakin ya ce "A ina?"

Ta kalli daidai gurin da Ƙaisar ya tsaya, ta ce "Wanda ya tsaya a nan, wani dogo"

"Ban yi magana da kowa ba" ya yi maganar yana girgiza mata kai.

Ta yi ajiyar zuciya ta ja ta zauna, tana jin kanta yana ciwo.

****

"Suwaiba" Alhaji Fatuhu ya kira sunanta.

Ta kalle shi ta ce "Ya dai?"

"Ba na jin daɗin jikina ne, kuma wani abu ne yake damuna"

"Me ke nan?"

"Ƙara ta za a kai kotu"

Ta waro ido ta ce "Kotu kuma? Me ka yi?"

"Kayan nan da suka yi ɓatan dabo, ranar Litinin zamu shiga kotu da 'yan kasuwa. Kujerata ma an sauke ni. Amma bai dame ni ba, kayan mutane nake tunani"

Ta kwaɓe baki ta kaɗa kai ta ce "Ai Alhaji Fatuhu duk ɗan da ya hana uwassa bacci, shi ma ba zai yi ba. Babu irin wahalar da bamu sha tare ba, amma abin Duniya na samuwa, ka auro yarinya ƙarama saboda ka ƙuntata mini, ka ci duniyarka da tsinke. Ai ga shi kai ma Allah ya kama ka" Ya yi zuru da ido yana kallonta.

Ta gama maganganunta ta bar masa ɗakin.

Tana zuwa bedroom ɗin ta, ta rufe ƙofa, hawayen da ta maƙale ta ba su damar gangarowa.

Ta hau nanata "Innalillahi wa innalillahi raji'un"

Ta ɗauki wayarta ta kira Yayanta.

Yana ɗagawa ya ji muryarta wani iri, ya ce "Lafiya kuwa?"

"Yaya Baban su Raudah wai za a kai kotu, 'yan kasuwa su na zargin ya cinye musu kuɗi, dan Allah ka yi wani abu a kai dan Allah"

"To ikon Allah, amma ba sai ki bari sai da Safe ba, kya kira ni. Amma ku kuma kin tabattar bai ci kuɗin ba?"

Suwaiba ta ce "Yaya kai ma ka san shi da gudun Duniya, da abin mutane wallahi zan iya rantsuwa bai ci kuɗin kowa ba"

"Ki bari zan kira ki da Safe" ta ajiye wayar jiki a sanyaye cikin damuwa.

Kasancewar a sashen Fadila yake, ta fahimci damuwa a tattare da shi, sai dai fafur ya ƙi gaya mata, ya lallaɓa ta ta yi bacci.

*****

Da daddare Nana ta kasa karanta Alqur'ani, amma wannan karon ta samu ta saka a wayarta, ta daɗe tana saurara tana jin nutsuwa na ratsa ta.
Kasancewar jini ya ɗauke, ya sanya ta yi sallar Isha'i, ta kwanta karatun Alqur'ani yana tashi ƙasa-ƙasa a wayarta.
Tana kallon Sayyid, ya shirya ya kwanta a ƙasa, gurin da yake kwanciya da. Gaba ɗaya sai ta ji ta damu. Ta daɗe idonta biyu, tana jira ta ga ko zai ta so, amma bai tashi daga gurin ba.
Ta tashi a hankali ta nufe shi, har ta ƙarasa kusa da shi, ta kwanta.

Ba ta ce masa uffan ba, ta caza masa hankali har ya biye mata.
Bayan wani ɗan lokaci ya numfasa ya ce "Kin daina fushin?"

"Ba kai ka saka na yi fushin ba? Amma ka yi haƙuri"

"Me na yi miki?"

"Me yasa za ka yi wannan yarinyar magana, har ta baka abu ka shigo mini da shi ɗaki?"

"Ki na gurin kin san meyafaru?"

Ta tashi daga jikinsa, ta ce "Ni ba na son jin meyafaru kawai babu ruwanta da kai, kar ka sake kula ta. Dan wallahi za ka iya nema ta ka rasa. Idan ka na son ta maye gurbina ba wani abu, ni zan iya tafiya ta na baku guri".

"Ki daina faɗar abin da ba za ki iya aikatawa ba"

"To ka ci gaba, zan baka mamaki kuwa" ta yi maganar tana tashi zaune, da nufin ta bar masa gurin."

Amma ya riƙe ta gam, yana yi mata numfashi a wuya. A gurin suka kwana tare. Sai Asuba bayan ta yi wanka ta yi salla, ta koma kan katifa.

Tana tsaka da bacci, ta ji yana tattaɓa ta, ta buɗe idonta ta kalle shi tana yanutsa fuska, saboda bacci ne a kan ta sosai.
Wayarta ya ajiye mata a daidai kunnenta.
Waƙar Ali jita ce take tashi, ta Aminiya. Shiru ta yi tana sauraren baitukan tana kallon kyakyawar fuskarsa da ya tsare ta da manyan idanunsa yana kallonta yana murmushi.
Ita ma murmushin ta sakar masa, ta yinƙura ta tashi zaune, ita sam ba ta san da waƙar ma a wayar ba, kasancewar ba gwanar jin waƙa ba ce, amma har cikin zuciyarta take jin baitukan, tamkar shi ne yake rairai
mata.
Gaba ɗaya suka manta, da batun saɓanin da ya shiga tsakaninsu.

(BAYAN MAKONNI BIYU)

Gaba ɗaya Fadila ta rasa abin da yake yi mata daɗi, hankalinta ya ƙi kwanciya, tun da aka fara zaman kotu ta ji halin da ake ciki ta rasa

55 / 64