BUZU BOOK1 COMPLETE Hausa Read Novels By Aysha Cool.txt

Author :  Aysha Cool Category :  Hausa Read

Chapter   23 / 64

66K to 69K   out of 190K words

fito?"

Nana ta ce "Eh, ina ta yi wa wannan ɗan uwan naku magana, ya yi mini banza"

Sule ya kalle shi ya ce "Banza ya ce miki?"

"A'a ya yi mini shiru"

Ya ce "Auu shiru bai yi magana ba? Ba shi da lafiya ne, ki yi haƙuri"

Ta ce "Kurma ne?"

Sule ya ce "A'a yana ji, magana ce ba ya yi"

Maimakon ta tafi, sai ta ce "Bebe ne kenan?"

Sule ya ce "Bebe me kenan?"

"Ba komai, buɗe mini na tafi"

Ya ajiye kwanon hannunsa ya buɗe mata, ta ɗauki kayan har za ta fita, sai ta waiwaya aikuwa karaf idanunta a cikin nasa.

Ta ja kayanta ta fice ta tafi gida.

*****

Cikin damuwa Mama take kallon su Jamila, Suwaiba jiki ya ɗan yi kyau kwana biyu. "Jamila, wai haka za mu ci gaba da zama babu wani ci gaba? Kun san da an aurar da yarinyar nan kanku zai juyo, kuma haryanzu kuma babu wani tsayayye na kirki, duk sai takarce"

Jamila ta ce "Taɓ, ai wallahi babu wanda ya isa ya yi mini abin da ake yi wa Nana, wallahi bujirewa zan yi"

"Ke dalla rufe mini baki, kafin a kai ga hakan ba sai a samu mafita ba, na gaji da kashe kuɗi a gurin malamai, babu wani saurayin kirki mai kuɗi, duk sai gayyar tsiya".

Jamila ta ce "Ni fa auren nan ko na yi shi, ko kar na yi shi bai dame ni ba, ni damuwata na samu mai kashe mini kuɗi, nima na ɗana rayuwar jin daɗin nan, wannan baƙin talaucin nan na gidan nan, idan ka biye masa, haka rayuwar ka za ta ƙare, ka je kuma auri talaka irin Baba ka ci gaba da gyangyaɗa rayuwa, jin daɗi sai dai ka ga wasu suna yi"

Suwaiba ta ce "A ina za a samu mai kuɗin, mu ba wani shegen kyau ba"

Jamila ta ce "Kanti za mu shiga wallahi, dan ni ina ganin allura ma zan yi"

Suna cikin maganar, Nana ta shigo da sallama, kasa amsa sallamar suka yi, sai bin ta da kallo, ganin kayan da suke jikinta, ga hannunta ta jakar kaya.

Nana ba wani shahararren kyau ne da ita ba, sai kyakyawan diri, domin jikinta shi ne babban rashin tsaronta. Idan ta taho ta gaba duk hijjabin da ta saka, baya ɓoye ƙirƙirar ƙirjinta. Baƙa ce mai matsakaicin tsayi.

Ta fito tsakar gida ta ɗebi ruwa ta yi wanka, ta yi alwala.

Jamila ta kasa jurewa ta ce "Nana ina ki ka samu wannan rigar? Ta yi miki kyau sosai" Nana ji ta yi tamkar ta share ta, saboda yadda suka haɗa kai da babarsu, su ka wulaƙanta ta, suka ɗauki gaba da ita.

Amma ta yi yaƙi da zuciyarta ta ce "Da gaske?"

"Wallahi ta yi miki kyau sosai"

"Na gode" ta faɗa a taƙaice.

"Waye ya baki?"

Nana ta ce "Gidan da nake aiki ne suka bani"

"Zan zo a din ga bani aro"

Ta jinjina kai ta ce "Idan ma so ki ke sai na baki"

"A'a aron dai" Nana na shiga ɗaki, Mama ta ce "Mara zuciya, me take da shi da za ta baki? Ba ga uwar ɗakinki nan tana baki kaya ba"

Nana na saka ƙafarta a ɗakinsu, ta ganta a libraryn Ƙaisar.

"Meye haka kuma? Salla fa zan yi" ta yi magana tana waiwayen ganin ta ina za ta gan shi.

A kan kujera ta hange shi, yana rubutu a cikin wani littafi, ba tare da ya kalle ta ba ya ce "Ai ba a kira sallar ba ko?"

"To me ka kawo ni nan na yi maka, a yanzu? So nake na yi azkar kafin a kira sallar" Nana ta faɗa a hasale.

"Wanda za ki aura ba shi da lafiya, an ce ki je ki duba shi kin ƙi, me ki ke zato?"

Ɗan shiru ta yi, sannan ta kalle shi ta ce "Kai ka saka shi ciwon ciki kenan?"

Ya ajiye alƙalamin, ya rufe littafin, ya tashi ya ce "A'a, ba ni ba ne ba, miyagun ƙwayoyin da yake sha ne kawai suke tambayarsa, duk ba wannan ba, haryanzu ba ki shirya barin gidan nan ba."

"Wai in bar gidan na je ina?"

Ya tura littafin hannunsa, tsakiyar wasu littattafai ya ce "Yanzu ba wannan ba tukuna, kin ga da kin yadda da sharaɗinmu, da kin ceci ɗan yaron nan da yake ta ƙaunar ki"

A razane Nana ta ce "Wane yaron? Ba dai Haidar ba"

Ya harɗe hannayensa a ƙirjinsa ya ce "A'a ba shi ba, kalli mudubi da kin yarda ki na da halin ceton yaron nan, amma baƙin taurin kan ki ya sanya zai rasa rayuwarsa"

A gigice Nana ta ce "Wai wani yaron?" Da idonsa ya nuna mata mudubin. Muhsin ne a kwance, babu inda yake motsi a jikinsa, ga robar abinci, ga oxygen a hancinsa. Gefe mamansa ce, idanunta jawur saboda kuka. Ga kuma yar mahaifinsa Hajiya Sa'a a gefe.

Nana ta gigice ta ce "Muhsin"

"Eh, kin makara, an riga an bayar da jininsa ga wani aljani, mutuwa zai yi yaron"

"Innalillahi wa innalillahi raji'un, meyasa ba ka yi komai a kai ba?" Ta yi magana cikin kuka.

"Ina cikin aljanu masu son zaman lafiya, dama da zan yi wani abu a kai, sai dai ta hanyar ki, kuma farkawar sa ta ƙarshe ma sunan ki yake ta kira. Kash Allah sarki, dama sunan uwarsa ya kira da take zaune kusa da shi, tna lissafa dukkanin numfashin da yake fitarwa, cike da ƙauna da kuma fatan ya ci gaba da rayuwa, ba ke ba da ba ki sam ciwon sa ba" yayi maganar yana hura iska a jikin mudubin, a take komai ya ɗauke.

Nana ta rikice cikin kuka, ta rasa abun yi gaba ɗaya.

"Ƙanwar babansa ce ta bayar da jininsa, aka yi mata domin ci gaban samun duniyarta. Wadda dai ta bayar da turare a kawo miki. Shikenan mun gama je ki yi sallar ki"

"Nana" ta ji Baba ya kira sunanta da ƙarfi. Ta ɗago kai ta kalle shi, tana zaune a cikin ɗaki ta haɗa kai da gwiwa tana ta kuka.

"Me aka yi miki? Ko wani ne ya mutu?" Ta girgiza kai alamar a'a.

"To gidan aikin ne suka yi miki wani abu?" Ta girgiza kai alamar a'a.

Baba ya sake cewa "To kukan me ki ke yi, an ce tun da ki ka dawo ki ke abu ɗaya ko jikin ne?"

"Baba babu fa komai" ta yi magana tana tashi tsaye. Ta kalli gari ya yi duhu sosai, da alama isha ta wuce. Ta yi shiru ta tuna abin da ya sakata kuka, amma ta kasa tuna komai.

Ta yi alwala ta yi sallar magariba da isha'i, tana jin wata irin matsananciyar damuwa da tashin hankali a cikin zuciyarta, amma ta kasa tuna ko a kan mene ne. Abincin da ta zo da shi ta kasa ci, ta kira Nasiru ta bashi, ya karɓa ya gudu waje kar Mama ta hana shi ci.

Sai dai tun da sanya haƙarƙarinta a ƙasa take addu'a, amma bacci ya gagara, ta yi juyi, ta kuma amma ko alamar bacci babu a idonta, har aka yi kiran sallar farko, a kunnenta ta tashi ta yi alwala, ta yi nafilfili ta zauna har aka yi sallar asuba.

Har gari ya yi shaa, tana zaune. Ta tashi zata fara shirin fita, kawai idanunta suka sauka a kan jakar da ta dawo da ita, daga gidan sarkin baka. Ta ɗaukko jakar ta hau buɗewa. Sai dai ta zazzage jakar kaf babu komai a ciki.
Ta yi guntun tsaki, ta ajiyeta, sai dai ta yi shiru tana tuno abubuwan da suka faru a gidan sarkin baka. Ko ba komai ya karrama ta, ya mutunta ta, tana matuƙar son sanin halin da yake ciki a yanzu.

Ta gama shirinta, ta yi wa Baba sallama ta tafi gidan aikinta.

A ɗaki ta iske Haidar bai ko tashi ba, kasancewar ba ta samu bacci daren jiya ba, ya sanya ta nemi guri ta kwanta a ƙasa, bacci mai nauyin gaske ya ɗauke ta.

Ji ta yi tamkar wani abu ba dai-dai yake ba, ga baccin tana yi, amma ba ya mata daɗi sam. A hankali ta buɗe idonta, kawai ta ga Alhaji Zailani a cikin ɗakin.
A mugun sukwane ta tashi, ta ja da baya ta kalle shi ta ce "Lafiya, me ya kawo ka nan?"

"Gidana ne" ya bata amsa.

"Eh na san gidan naka ne, amma a cikin gidan naka akwai inda shari'a ta yi maka iyaka, tun da ba duka mutanen gidan ne iyalinka ba"

Ba tare da ya amsa maganar da ta yi ba ya ce "Mun fara magana ba mu ƙarasa ba, na zo mu ƙarƙare ta yau"

Cikin takaici Nana ta ce "Wace maganar?"

Ya nuna mata gefen gadon Haidar ya ce "Zauna mu yi magana"

"Ni ba zan zauna ba, ka gaya mini ko ma mene ne a haka"

Ya nemi guri shi ya zauna, a gefen gafon Haidar yana tsareta da idanunsa.

"Buƙata ce da ni a gare ki, wadda idan ki ka amince ke ma za ki samu biyan buƙatun ki"

Ta ce "Ni na ce maka ina da buƙatar wani abu ne?"

Alhaji Zailani ya ƙara tattara hankalinsa a kanta ya ce "Ko ba ki faɗa ba, na san ki na da buƙata kema. Kasuwancina ne ya fara yin baya, an ce mini muddin na yi tarayya da mace irin ki, taurarin ki za su haska nawa." Galala Nana take bin sa da kallo, yadda ya zauna babu kunya babu tsoron Allah, yana gaya mata maganganun banzar da babu komai a cikinsu sai jahilci da hauka.

Ko a jikinsa da kallon da take yi masa, ya ci gaba da magana. "Idan ki ka amince, zan baki kuɗi, kuɗaɗe ba ƙanan kuɗaɗe ba, kuɗin da sai kin rasa yadda za ki yi da su"

Cike da takaici Nana ta ce "Kai yanzu bawan Allah, ka na da kuɗin da zaka bani wanda sai na rasa yadda zan yi da su, me za ka yi da wasu kuma? Ai ina tunanin idan ka haɗa ka riƙe sun wadace ka"

Ya miƙe tsaye ya ce "Ai ba a daina neman kuɗi, ki amincewa buƙatata, zan baki kalar rayuwar da ba ki taɓa tsammani ba a rayuwar ki"

Nana ta ja da baya ta ce "Ba na buƙatar kuɗin ka, ko zan koma ga Allah a talauce ba zan abin da ka ke so ba, ko zan yi wannan mummunar ɗabi'ar ba zan yi da mushriki irin ka ba, Allah ya tsare ni daga sharrin ka"

Alhaji Zailani ya ce "A'a ba ki da wani zaɓi fa, tunda aka kasa riƙe budurwa kamar ki a gidanku, aka bar ki, ki ka fito yawon rainon yaro. Kuma na san tunanin ki bai wuce budurcin ki ba, babu lallai wani abu ya shafi nan gurin ma. Budurcinki ba zai taɓu ba, kuma idan ki ka samu kuɗi, za ki iya rayuwar ki ba tare da wani ɗa namiji ba. Ki yi tunani a kai" ya nufi hanyar fita ya fice daga ɗakin.

Jikin Nana ne yake wata irin tsuma, cike da tsoro da razani, ta dafe saitin zuciyarta da yake wani irin bugu tamkar ta fasa ƙirjinta, ta fito.

Ta kalli Haidar da yake ta baccinsa hankali kwance. Jiki a sanyaye ta tashi Haidar, ta yi masa wanka ta fita da shi falo tana ba shi Abinci.

"Ke me ki ke bawa ɗa na haka?" Ta ji muryar Shukura cikin ɗaga murya.

Nana ta kalle ta ta ce "Ƙosai ne da kunun gyaɗa"

"Ƙosai? Ki ke ba shi, a gidan uban wa ki ka samo wannan tarkacen ki ke bawa yarona?"

"Kunun a nan na dama, ƙosan kuma daga gida na taho da shi, shayi ba abincin yaro ba ne" Nana ta faɗa kanta tsaye.

"Shut up malama, ki kwaso jagwalgwalo daga waje ki kawo shi kina bawa yarona kashe shi za ki yi? Na san wani concoction aka haɗa a ciki ki ke ba shi, dan samun guri?" Nana kamar ta yaɓa mata magana, mussaman da take cike da takaici, da mamakin abin da babanta ya yi mata, amma ta yi shiru, ta haɗiye.

Haidar dai hankali kwance, yaka ta ɗaɗɗakar kunu a cikin feeder, ta tafi a fusace za ta fizge kwanon ƙosan ta yi jifa da shi.
A zuciye Haidar ya buga mata feeder hannun sa, yana ihu.

Nana ta haɗe rai ta kalle shi, sai ya nutsu.

"Ɗaukko kwanon da ƙosan, ka zo ka bata haƙuri, ko kuma yau na saka a kwano a kai wa kare ya cinye ka, sai wataran za a sake haifo ka"

A ruɗe ya tashi ya ɗaukko kwanon ya kawowa Nana, yana cewa "Sorry Anty"

"Ba ni zaka bawa haƙuri ba, maminka za ka bawa haƙuri"

Mummy da take kallon duk abin da ya faru ta ce "Lallai tsakanin Haidar da Nana sai Allah. Sannan ke Shukura ban da abin ki, soyayya ce ta sanya har ta ɗauki abin ta ta bawa ɗanki. Sati biyun nan wallahi har ya yi kumari, ba nan ki ke complain na ramar sa ba? Malama ki wuce ki tafi makarantar ki, sannu da ƙoƙari Nana"

"Yauwwa Mummy ina kwana?"

"Lafiya kalau Nana, ya ɗan naki?"

"Yana nan lafiya ƙalau"

Kasancewar a fusace yake, bai gai da Mummy ba, sai da Nana ta yi magana. Nana tana ganin mutuncin Hajiya Amina, tana da kirki sosai da sosai, Nana ta din ga mamakin yadda take zaune da Alhaji Zailani da wannan mummunar ɗabi'ar da yake aitawa. Kodayake wata ƙila ba ta san yana yi ba. Wata zuciyar ta bata amsa.

Abin ya din ga damunta a zuciyarta, amma ta rasa wa za ta gayawa. Tare suka yi girki da Jummai. Har na dare suka yi bayan sun kammala yau ma Jumman ta roƙe ta, ta ajiyewa masu gadi Abinci kafin ta wuce gida.

Tun da ta tafi hanya take saƙawa tana warwarewa, idan ta ajiye aikin nan ba ta da wata makoma, yanzu Allah ya rufa mata asiri, ba ta da fargabar abinci ko kaɗan, dama abinci shi ne babbar damuwarta, ga kuma albashi mai tsoka da take sanya ran fara karɓa. Sai dai ga ƙoshi ga kwanan yunwa, ko dai ta ci gaba da zuwa tana fuskantar barazana daga mai gidan, ko kuma ta koma zaman gida ba ta da abin yi, yunwa ma kaɗai ta ishe ta.

Duk da akwai 'yar tazara kaɗan daga gidan aikinta, zuwa gidansu, amma har ta je gida tunani take yi.

Tun a ƙofar gida ta haɗu da Nasiru, ya ce "Nana kin dawo? Me muka samu yau?"

Ta yi murmushi ta ce "Ba komai"

"Bayan ga leda nan a hannun ki"

"Shinkafa ce, ka bari sai mu ci da daddare, ko an yi girkin dare ne?"

Nasiru ya ce "Tuwo ne, kuma tun da ga shinkafa ba zan ci tuwo ba, yauwwa ni na manta ma, ɗazu Baba ya yi wasu baƙi, yana ta shiga yana fita yana faɗa, ke yake jira ki dawo"

Ta yi sak, ta ce "Ni kuma?"

"Eh"

A ɗan marairaice ta ce "To me kuma na yi?"

Ya ɗan ɗage kafaɗarsa ya ce "Wallahi nima ban sani ba"

Ta kalli gidan ta ji gabanta ya faɗi, sai ta ji sam ba ta ƙaunar shiga gidan ma.

Ta daure a hankali, tana takawa da ƙyar, cike da fargabar rashin sanin abin da za ta tarar.

Ta yi sallama babu kowa a tsakar gidan, ta shiga ɗaki ta ajiye ledar abincin hannunta.

Gaba ɗaya ta rasa abin da yake yi mata daɗi, a zullumi take kawai Baba ya zo ya gaya mata me kuma ta yi a wannan karon.

"Laa Nana kin dawo?" Ta ɗan zabura, ta kalli Jamila dan ba ta san ta shigo ɗakin ba. Ta ce "Eh ya gidan?"

Jamila ta ce "Lafiya ƙalau, ga kunun aya can da na ajiye miki a jug, a gidan maman khairat muka yi, na san ki na son shi, shiyasa na ce bari na ajiye miki"

Nana ta yi murmushin ƙarfin hali, ta ce "Amma kuwa na gode sosai da sosai, bari na yi sallar magariba na haɗa da abinci"

Jamila ta ce "To shikenan, ga shi can ma an yi kira"

Nana ta ce "Amm yauwwa Jamila, Nasiru ya ce mini Baba yana nemana, dan Allah ko kin san abin da na yi yake nema na?"

"A'a, ai ban daɗe da dawowa ba nima"

"Ok to na gode" haka dai a ɗarare ta yi sallar magariba, duk da tulin damuwar da take ciki, ta ɗauki jug ɗin kunun ayar nan, domin ta ɗan sha ta bawa Nasir sauran, dan ko sha'awar abinci ba ta yi. Shi ma dan kar Jamila ta ji haushi ne, tun da ta ga neman shiri take yi da ita.

Ta buɗe jug ɗin ta kai bakinta, ta ji an ce "Kar ki sha"

Ta waiwaya ba ta ga kowa ba, ta sake kaiwa bakin ta aka sake cewa "Kar ki sha" kawai ta ɗauki fitila ta haska jug ɗin.

Jini ne a ciki yake ta tafasa, tamkar akan wuta. A razane ta saki jug ɗin kunun ayar ya zube. Ta din ga sauke numfashi, ta yi maza ta janyo zani ta goge gurin, dan kar Jamila ta zo ta tarar da abin da ya faru. Ba ta gama wannan taradaddin ba, Baba ya kwaɗa sallama muryarsa a sama kamar tashin hankali.

Wani fitsarin tsoro ne ya kama Nana, tun kafin ta san abin da ta aikata.

"Nana ta dawo ne?"

Jamila ta ce "Eh tana ɗaki"

Cikin hargowa ya ce "Ki na ina fito ki zo nan, magajiyar tsiya da jaraba"

Dumm ƙirjinta ya sake bugawa, a karo na babu adadi, jikinta ya din ga rawa yana neman gaza ɗaukarta, ta fito jiki a sanyaye tana jiran ji abin da Baba zai ce.

"Ashe kin je gidan Ummi, ta ce miki ku je ku duba yaron nan, ki ka ce ba zaki ba, ki ka ƙara nanata mata ba kya son sa. To ƙanin babansa ya zo nan ɗazu, sun ce a tattara duk wani abu da ya san ya yi miki a mayar masa. Kuɗin aurensa dubu saba'in, kuɗin da ya bayar aka kai ki gurin mai magani, da kayan shafe-shafe da ya kawo, ki na gidan mai magani aka yi amfani da su a gida, kusan lissafin dubu ɗari da sittin, sun ce a mayar musu, kuma ni ban san inda zan je na nemo wannan kuɗin ba, dan haka sai ki shiga ki fita ki san yadda za ki yi a nemi kuɗinsu a ba su."

Ayshercool
08081012143
Page 21

Idan da sabo, Nana saba da ire-iren waɗannan ɗabi'un na Baba, amma na wannan lokacin sun ɗaure mata kai fiye da yadda take tunani.
Duk cikin kuɗin nan, babu wanda take tunanin ta

23 / 64