DAFIN HARSHE BOOK 2 COMPELET HAUSA NOVELS BY IYAM.txt

Author :  Maimuna Tijjani Iyam Category :  Tknovels

Chapter   30 / 39

87K to 90K   out of 116.4K words

duhu ya mamaye ko'ina alamar dare ya daɗe da yi. Na lalumi wayar da yake wajena na kunna haskenta tare da duba lokaci da ya nuna mini ƙarfe goma sha ɗaya da rabi na dare.
"Subhanallahi! Umma kin ga har dare ta yi". Na yi zancen ina tashi na sassauƙe labulen tagogin sannan na rufe ƙofan ɗakin, na zo na zauna a nutse na soma faɗin"ni kuwa Umma ina kayan cikin falon suke na ga har cikin ɗakin babu komai. Daga tabarman nan fa sai ƙunshin kayan sakawanki".

"Na sayar da komai da yake cikin ɗaki da falon nan, duk kuɗin su ƙare akan jinyata kafin Alhassan ya kawo min ɗauki. Amatullah tabbas Sawwama da ƴaƴanta su cika cikakkun masoya a gare mu, don ba kowa ba ne za a yi masa abin da na yi Alhassan kowa har ya dube ni da idon rahama a lokacin da nake buƙatar taimako daga gare sa". Kalamanta suka sanya jikina yin sanyi ƙalau na taƙaita zance ta hanyar gyara mata wajen da za ta kwanta na kwantar da ita bayan na yi mata alwala da ruwan goran da Yaya Alhassan ya kawo mana ɗazu da ya zo shi, na shafe mata jikinta da addu'a ni ma na kwanta a gefenta. Sai dai bacci ya ƙi ziyartar idanuna haka na yi ta tunani masu nauyi, kafin wasu hawayen tausayin kanmu da yadda rayuwa ta mayar da mu ya fara zuba daga idona.
Ina ma wanda ya mutu yana dawowa tabbas da sai na bayar da duk wasu abubuwan da na mallaka a cikin duniya, don kawai Abba ya dawo ya ga tsantsar nadama da dana-sanin da yake kwance a cikin idanun Umma, zan zo ya dawo ya ga yadda ta yi kewarsa a duniya yayin da ta soma amfani da tarin nasihohin da yake yi mata, Allah mai iko wai yau bakin Umma yake furta mini kalmar Allah ya yi miki albarka.

Ban iya runtsawa a wannan daren ba har aka ƙiran sannan asubahi na tashi na yi alwala na yi sallan, sannan na zo zan tashi Umma don na yi mata alwala ta yi na ta sallan na ji shiru, na soma ƙiran sunanta ina bubbuga matashin da kanta yake kai nan ma ba ta tanka mini ba. Nan fa ido ya raina fata na soma jijjiga ta ina ci gaba da ƙiran sunanta amma har yanzu shuru.

"Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Umma don girman Allah kar ki yi mini haka. Ki yi wa Allah ki buɗe idanunki". Na yi furucin cikin tsananin kiɗima da ruɗewa, ganin zaman ba zai haifar mini da ɗa mai ido ba ya sa na na baza ma waje, ɗakin Umman Amira na nufa ina buga mata ƙofa tare da ƙiran sunanta amma ba ta amsa wa, babu abin da nake iya furtawa illa kalmar innalillahi wa inna ilahirin raji'un. Na daɗe buga ƙofan kafin Baba Habu mijinta ya shigo da alama daga masallaci yake.

"Ke lafiya?". Ya watsa mini tambayar cikin zafin rai.
"Daman jikin Ummata ne ya tashi shi ne na zo ƙiran Umman Amira, ta taimaka ta zo mu je ta duba ta".

"Wani irin ta duba ta? Likita ce ita ɗin ko kuma da na ilmin sanin jinya? Warin da yake fita daga jikin Hafsatu da matata ta shaƙa jiya shi kaɗai ma sai da ya haddas mata cuta, daren jiya ba mu runtsa ba. Haka ina zaman zamana aka sa ni kashe ƴar dubu uku ta na sayo mata magunguna shi ne fa har ta sha ta kwanta yanzu da zan fita Masallaci. Don haka ba za ta je ko'ina ba idan jikin ya yi tsanani ki ɗauke ta ki kaita asibiti likitoci su duba ta".

Cike da mamaki na ce"Baba ni ce Amatullahi, ko ba ga shaida fuskata ba ne?".
"Na shaida ki tsaf fuskarki ai ba ɓoyayyiyar fuska ba ce a cikin unguwan nan, na gane ki sarai ko ba Amatullah ɗiyar ba ce Malam Manniru da ta yi cikin shege har hakan ya yi sanadiyar mutuwarsa ba, sannan ko kwanaki arba'in bai cika a ƙasa ba kika sanya ƙafafunki ki ka gudu daga gida kika bi Saurayin da ya yi miki cikin ku ka je can ku ka ci gaba da baɗalarku ba". Yana gama zancen ya zo ya buɗe ƙofar ɗakin ba ko kusa ban yi tunanin a buɗe take ba ya shige abin sa.
Har ƙasa na durƙushe akan gwiwoyina ina ta wani irin haki tamkar wacce ta fafata a gasar tseren gudu a matakin duniya gabaɗaya.

Ina cikin wannan halin Ustazu Abdulwahab ya shigo cikin gida ya dawo daga masallacin sallan asuba, ya tambaye ni me ke faruwa? Cikin sanyin amo na zayyana masa komai ya ce mu je ya duba ta. Na yi gaba ya na bi na a baya muka ka isa wajen Umma.
Ya kai minti biyu yana kallon fuskarta sa boda tun da na tashi na kunna hasken wayata na ajiye. Sai can ya tsuguna a gabansa tare da kai hannunsa daidai hancinta hakan bai yi masa ba sai da ya riƙo tsintsiyar hannunta na ɗan danna yatsansa kafin na ga ya jijjiga kansa.

"Don Allah me yake samun ta? Tun ɗazu fa ban ga ta yi motsi ba. Shi yasa tun jiya nake ta ce mata mu je mu asibiti".

Ya ɗan yi jim kana ya ce"Amatullah ko da kun je asibiti babu abin da zai sauya daga abin da Allah ya rubuta zai hare ta". Da hanzari na tari numfashinsa"me ye kake nufi?".
"Sai dai haƙuri don ita kam ta riga mu gidan gaskiya, ta riga da ta amsa ƙiran Ubangijinta". Ji na yi komai na duniyar ya tsaya mini cak haka na zube akan gwiwoyina ki hawaye na kasa yi illa kafe Umma da na yi ido jikina ya na rawa, ƙasa-ƙasa nake ji yo sautin muryar Ustazu Abdulwahab sai dai ba na iya tantance abin da yake bakinsa yake furtawa balle har na fahimta. Ina nan kamar gunki na kasa motswa har izuwa lokacin da ya fita ya je ya ƙira matarsa suka dawo tare. Ita ta riƙe ni sa boda yadda jikina yake rawa ina ga ni Ustazu Abdulwahab ya rufe wa Umma idanunta da suka kafe sannan ya lulluɓe ta da zanin da ta lulluɓu da shi.

Ɗakinta ta kai ni ta zaunar da ni sai na kasa yin komai, ba na iya yi ki da magana ba balle kuka. Idanuna ne kawai suke motsawa. Ban san adadin awannin da na ɗauka zaune a wajen ba har zuwa lokacin da Anty Sawwama da Anty Zulaihatu suka zo su. Duk kukan da na mutane suna yi akan gawan Umma ni ko hawaye na kasa yi.
Duk wanda ya zo ya ji labarin cewa na dawo gida ni yake tausayawa akan mutuwar Umma, sai dai ni kuma Allah cikin ikonsa ya saka mini wani nutsuwa na mussamman duk abin da ake faɗa ina ji sai dai ba na iya mayarwa. Har aka shirya Umma na je na yi mata addu'a ban yi kuka ba, sai da na ga an fito da ita za a fitar da ita waje don a yi mata salla. Ana ɗaga makarar na yanke jiki na faɗi, sai farkawa na yi na ganni a cikin ɗakin Anty Sawwama sai dai har zuwa wannan lokacin maganata ba ta dawo ba. Har aka yi kwanaki bakwai ba na iya yin magana ba na iya yin bacci ba na komai illa na zauna waje guda na yi shuru ni ba tunani nake yi ba, haka nan ni ba nazari ba.

Ranar da aka yi sadakan bakwai ina zaune Yaya Alhassan ya shigo ya same ni. Ya zauna kusa da ni yana kallona yayin da na yi ƙasa da idanuna.
"Amatullah". Ya ƙira sunan cikin sanyin murya mai cike da damuwa, kamar ya kunna wuta haka na ji hawaye suna zuba daga idona bakina ya fara rawa ina ta ƙoƙarin yin magana amma na kasa, sai da na ja dogon numfashi na fesar kafin na yi nasaran faɗin"Yaya Alhassan shi kenan Umma ma ta tafi ta bar ni? Ba za mu sake gana wa ba? Me yasa Allah yake jarabta na da rasa dukkan mutanen da nake so? Allah na tuba na tuba ka yafe mini". Cikin wani irin cushewan amo na yi zancen ina ci gaba da fitar da hawayen da na shafe tsawon kwanaki ba tare da na yi su, bai hana ni yin kukan ba kamar yadda bai dakatar da ni ba illa idanun da ya zuba mini.
[12/21, 12:04 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*

©️ Maimuna Tijjani Iyam

_______________________________________

Page 7️⃣5️⃣

Na daɗe ina kukan har sai da na ji numfashina yana sama yana ƙasa tamkar wacce aka sanya igiyan kirtani aka zarge min wuyana da shi. Haƙwarana suna karafɗiya da ruwa tamkar sabuwar haihuwar kazan da ruwan sama ta yi mata mungun bugu.
"Yaya Alhassan duniyar gabaɗaya ta fara ba ni tsoro komai na cikinta ya daina burge ni. Tabbas iyaye daban suke a cikin dukkan jerin mutanen shi kenan Abba ya tafi ya bar ni yanzu ma Umma ta bi shi, ina zan saka raina? Ina zan soma kaina na ji sanyi da sauƙin halin da nake ciki? Wallahi zuciyata zafi take yi mini raina yana tafasa tamkar ƙirjina zai fashe. Na daina samun bacci tunani ya yi mini yawa har ina tsoron zuwan wani rana da za su zo ku tarar da gawata a cikin ɗakin nan, zuciyata ya buga na mutu kowa ya huta".
"Ke Amatullah". Yaya Alhassan ya dakatar da ni cikin kakkauran amo, ban iya ɗaga ido na kalle shi ba illa rusunar da ƙwayoyin idanuna ƙasa da na yi wasu hawaye su na ci gaba da ambaliya a bisa kuncina suna zarce wa har izuwa tudun wuyana.
Sai da ya sassauta amonsa kafin ya zarce da faɗin"Amatullah ki zama mai tawakkali, haƙuri da miƙa lamuranki ga Allahu malikulƙuddusu mana. Sarkin da ya yi mana alƙawarin komai tsanani yana tare da sauƙi haka nan komai duhun dare hasken alfirjir zai keto ya yi wannan baƙin duhun daren. Allah ba ya taɓa jarabtar Bawa da abin da ba zai iya ba don haka ki lallashi zuciyarki ki ba ta haƙuri akan wannan jarabawan da suka faru da ke. Ki sani Allah ya na tare da masu haƙuri kuma a ko wani irin yanayi su ne da riba. Zuciyata ta kan cika da rauni a duk lokacin da na zo na iske ki a cikin ɗakin nan kin yi shuru ki na tunani, zuciyata ta kan karaya a duk lokacin da na zo na tarar da ke ba kya iya furta komai illa kallo da ido. Amatullah ina jin ki har a cikin ƙasan raina ke ɗin ƴar uwata ce kuma jinina, duk wani abun da ya shafe ki ina ji kai tsaye tamkar ni ya shafa".

Shuru na yi ina ci gaba da sauraron zancen da ya ɗaura da su cikin sanyin amo da sigar lallashi"Amatullah ina ji a jikina in sha Allah rayuwarki za ta inganta. Matuƙar ina raye a cikin wannan duniyar ba zan taɓa bari ki yi kukan maraici ba, zan tsaya miki a cikin ko wani irin yanayi na daɗi ko akasin hakan. Zan yi amfani da gumina wajen ganin na faranta miki, ina so ki sama nutsuwa ki yi tunani da zuciyarki ki duba ki ga abin da kike ganin ya dace ki yi wanda zai taimaki rayuwarki, in ma karatu ne, sana'a ko kuma aure" . Babu shiri na ɗago kaina ina bin sa da kallo cikin rawar harshe na furta"aure kuma Yaya Alhassan?". Ya gyaɗa mini kansa cike da tabbatarwa ya ce"aure mana Amatullah me ye za ki zauna ki yi a cikin gidan? Ke fa yanzu ba yarinya ƙarama ba ce kin yi girman da kin mallaki hankalinki kanki. Aure shi ne rufin asirin ko wacce ɗiya mace komai gatanta, komai dukiyarta, komai iko da izzarta ke ko da kuwa uban ne ya fi kowa kuɗi a kaf cikin nahiyar Afrika da kewayenta aure shi ne cikar mutumcinta. Duk wani farin ciki, nutsuwa da kwanciyar hankalin mace ta na samunsa ne a cikin gidan aurenta amma idan ta yi dace da samun abokin zama na gari. Wanda ya san kima da darajarta". Bai gama maganar na dakatar da shi cikin faɗin"Yaya Alhassan to ni yanzu waye ma kake ganin zai iya aurena? Aure fa baban lamari ne alaƙa ce da in an ɗaura ta ake fatan ta ɗaure har zuwa ƙarshen numfashi. Ko Annabinmu cewa ya yi idan ɗayanku a tashi aure ya zaɓi ƴar gidan mutunci, mai kyakkyawan nasaba da asali, mu faɗa wa kanmu gaskiya duk waɗannan abubuwan babu su a tare da ni. Kar ka manta ta fa har ciki na yi ba tare da aure ba, na sa ƙafa na tafi can wata uwa duniya na yi zaman kaina. Idan tarihi da asali za a bi shi ma babu wani kyakykyawan abin da za a tarar, ko ka manta ni ce wannan ɗiyar da duk unguwa suka shaida cewan mahaifinyarta ta raina mahaifinta ba ta ganin kowa da gashi? Shin waye zai iya yin jihadin haɗa zuri'a da mace mai irin tarihina? Yaya Alhassan akwai hanyoyin bautawa Allah wanda duk wanda ka yi daga ciki da ikilashi zai kai ka zuwa aljanna, ba dole sai ta hanyar aure ba".

Tun da na soma zancen ya yi shuru yana ta kallona ba tare da ya ce komai ba har sai da na kai aya. Ya ja dogo numfashi ya fesar kafin ya furta"aure ya zama dole Amatullah. Shi zai goge duk wani mummunan abun da yake cikin tarihinki, aure ne zai ba ki damar hayyafa ta yanda ko bayan ranki za a ga zuri'arki a tuna da ke har a yi miki addu'a".

Cikin zubda ƙwalla na ce"akwai wani burin da nake so na cimma".
"Wani irin buri ne?". Kafin na kai ga ba shi amsa Umar ya yi sallama a ƙofar ɗakin duk muka juya muna kallonsa, Yaya Alhassan ne ya amsa masa sallamar da hakan ya ba shi damar shigowa ciki tare da cewa"Yaya daman baƙi aka yi, sun zo gaisuwa kuma sun ce su na buƙatar ganin Amatullah ita ma su yi mata gaisuwa".

"To koma ka ce ta na zuwa".

"To Yaya". Ya amsa da shi a taƙaice yana juya wa ya fita daga cikin ɗakin.
"Sai ki tashi ki shirya tun da kin ji akwai baƙin da suka zo gaisuwa ko?". Kaina kawai na gyaɗa masa da hakan ya ba shi damar tashi ya bi bayan Umar. Sai da na ɓata a ƙalla mintuna biyu kafin na goge fuskana na ta saka hijabina na fito falon kaina a ƙasa. Can ƙasan maƙoshina na yi sallama Anty Sawwama ta amsa mini yayin da nake ƙarisowa na zauna kusa da ƙafafunta.
"Amatullah baƙi ne suka zo yi mana gaisuwar Hafsatu, shi ne suka buƙaci ganinki ke ma su yi miki gaisuwa". Sai a lokacin na ɗago kaina don ganin mutanen da ake magana akan su, take na ji zuffa ya keto mini ƙirjina ya buga da mungun ƙarfin bala'i.

Saifullah da Muhammad Taukif idanuna suka sauƙa akan su suna zaune a cikin falon yayin da suma ɗin ni suke kallo.
"Ku ne daman?". Na yi furucin ina nuna su da yatsana. Ban jira amsar kowa ba na ce"Anty me ye waɗannan mutanen suke yi a cikin gidan nan? Wallahi ba na son ganin wannan mutumin balle har mu zauna inuwa ɗaya da shi". Na ƙare zancen ina musu nuni da Saifullahi.
"Daman kin san shi ne?". Amir ya jefa mini tambayar cike da mamaki. Kaina na gyaɗa kafin na ce"shi ne fa wanda na ba ku labarinsa, shi ne wanda na yi aiki a cikin gidan wansa". Daga nan na ƙara kwashe komai da ya taɓa haɗa mu na ƙara sanar da su a karo na biyu. Tun da na fara zancen Anty Sawwama take ta ƙara jinjina kanta.

"Amatullah duk wani abin da ya taɓa faruwa a baya ki manta da shi ya wuce. Yadda ya tako ƙafa da ƙafa ya zo shi har cikin gidan nan don kawai ya yi mana gaisuwa to mu mutunta juna. Su yi abin da ya kawo su mu watse".
Hawaye ne kawai yake ta ambaliya a fuskana ina faɗin"Anty a duniya babu mutumin da ya taɓa gayyaya mini baƙaƙan maganganuna, ya suffanta ni da abin da ko kusa ban aikata shi ba kamar wannan mutumin. Har yanzu idan na rufe idanuna ina tuna munanan kalamansa gare ni". Shuru ya biyo bayan zancena na ƙarshe har na tsawon wani lokaci kafin can na tsinkayo muryar Saif ya sauƙa a cikin kunnuwana.

"Tabbas duk abin da kika faɗa haka ne babu kuskure ko ƙage a cikinsa, na aikata miki abubuwa da dama na zarge akan abin da ba ki aikata ba. Sannan akan idona aka wulaƙanta ki na kasa cewa komai. Sai dai duk da hakan ke ce mace ta farko da ta fara kawo mana ɗauki a cikin rayuwarmu ta warware mana wani babban ƙullin da duk ba mu san shi ba. Ranar da kika sanar da mu wannan abun washe gari na tafi garin Abuja na sauƙa a wannan otel ɗin da kika ba mu bayanansa, haƙiƙa na gane wa idanuna abun mamaki don da idona na kama Yaya Saddam da karuwa su na kwance a cikin ɗakin otel ɗin. An yi rikici sosai har sai daga bisani Anty Muhibbat ta ji komai ta bi mu can Abujan sai dai ga mamakina ko kaɗan ba ta ga laifin Yaya Saddam ba sai ma ƙoƙarin ba shi kariya da take yi ta ko wacce fuska. Hakan ya jefa ni cikin tunanin da na baza ma nemon gaskiyar da yake ƙunshe ƙasan kalaman kariyar da take ba wa Yaya Saddam. Nan na gano cewar kafin aurensu ita ɗin budurwan marigayi abokinsa ne watau Yaya Usman da suka yi wa junansu alƙawarin aure tun suna jami'a, wannan dalilin ya sanya suka mayar da kansu tamkar miji da mata ta hanyar biyawa junansu buƙata ba tare da shakkan kowa da komai ba. A lokacin Yaya Saddam ya san komai

30 / 39