DAFIN HARSHE BOOK 2 COMPELET HAUSA NOVELS BY IYAM.txt

Author :  Maimuna Tijjani Iyam Category :  Tknovels

Chapter   27 / 39

78K to 81K   out of 116.4K words

ne?". Na yi zancen cikin rawar jiki da na murya, duk su biyun suka tashi tsaye muna kallon juna.
Yaya Alhassan ya ce"Amatullah ke ce kika dawo haka? Ke ce kike rayuwa a cikin gidan nan". A raunane ya ƙarishe zancen kamar zai yi ƙwalla. Na ji kaina ya soma juya idanuna suna hango mini abin da yake gabana bibiyu, ƙafafuna suka soma karkarwa na yi lu na faɗi a wajen babu wani gaɓar da take motsa wa a cikin gangar jikina.
[12/18, 3:30 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*

©️ Maimuna Tijjani Iyam

______________________________________

Page 7️⃣2️⃣

Tun daga lokacin ban ƙara sanin takamanmen inda kaina yake ba, ban ƙara fahimtar komai ba haka nan idanuna ba su ƙara gano mini wani haske ba face gilmawar duhu baƙi ƙiri da babu alama ko ɗigon haske a cikinsa. Ban san iya adadin awannin da mintunan da na ƙarar ba na cikin hayyacina ba sai buɗe idanuna da suka yi mini nauyin gaske na yi na ganni kwance a cikin wani ɗaki wanda na ƙare wa kallo tsaf na kuma fahimci cewar ɗakin asibiti ne, kamar yadda na ga robar ƙarin ruwa a maƙale a hannuna na yi yunƙurin tashi sai dai kash! Gangar jikina ya ƙi ba ni haɗin kai wajen aiwatar da hakan a aikatace.
Ban san sa'ilin da ruwan hawaye masu ɗumi suka soma rige-rigen fita daga koramar idanuna ba sai jin ɗumin sauƙarsu na yi a bisa fatar fuskana. Abubuwan da suka wakana kafin na tsinci kaina cikin wannan yanayin da nake ciki ya soma dawowa cikin kwanyanta tiryan-tiryan, na cije leɓan bakina ina jin zuciyata tana buga wa ɓat-ɓat tamkar allon ƙirjina zai dare zuwa gida biyu.

Wahalallen numfashi na ja a karo na barkatai na fesar daga bakina yayin da na kai hannu na fincike ƙarin ruwan da aka maƙala mini a hannu. Na tashi na zauna da ƙyar yayin da nake jin kaina ya na sarawa tamkar zai faɗo ƙasa.
Ban yi aune ba na ji hawayen da suke zuba daga idanuna sun ƙara ƙarfin gudu ta yadda suke wanke mini fuskata babu ƙauƙautawa. A bayyane na furta"Yaya Alhassan me yasa kuka bayanna a cikin rayuwa a daidai wannan lokacin? Lokacin da nake dab da cika buri da muradin raina burin da ya daɗe a cikin farfajiyar ƙirjina. Ba zan iya haɗa ido da ku idan lokacin da ya dace na koma gare ku ya yi tabbas ni da kaina zan kai kaina inda kuke amma ba yanzu ba".
Ina gama zancen na diro daga kan gadon na ɗauki hijabina da yake gefe na mayar da shi kaina na fice daga cikin ɗakin, ina ta faman dube-dube da waige-waige, Allah ya tarfawa garina nono har na fita daga cikin ɗakin ban ga ɗaga cikin waɗanda nake guje musu ba. Daidai na iso ƙofar da zai sada ni da harabar cikin asibitin na ji na yi karo da mutum har sai da na yi tangal-tangal zan faɗi aka riƙo hannuna na tsaya cak akan ƙafafuna, na dafe ƙirjina sa boda tsananin tsoron da na ji yayin da nake cira kai don ganin wanda ya kawo mini agaji.

Idanuna suka gauraye cikin na Yaya Alhassan da yake tsaye a wajen ya kafe ni da idanu kamar yadda ni ma na kafe sa da na wa idanun, da har suka ƙanƙace sa boda azababben kukan da na yi a cikin ɗakin bakin na fito. Shi ya fara janye idanunsa daga kaina yana riƙe ƙugunsa da hannu ɗaya yayin da hannu ɗayan yake riƙe da wani ledan baƙa.
Cike da takaici ya soma faɗin"ina kika fito za ki je bayan ke da ba ki da lafiya har an kwantar da ke a gadon asibiti?". Bai jira na ba shi amsa ba ya ci gaba da faɗin"guduwa kika fito za ki yi ko?". Ya jinjina kansa kafin ya zarce da faɗin"Amatullah me yasa lalle kike son ki ga kin butulcewa ni'ima da ilhaman da Allah Ubangiji ya yi miki ne? Me yasa kike ta ƙoƙarin watsa ƙasa a idanun mutanen da suka ɗaura yarda da amimcinsu kacokam akan ki? Allah ya rufa miki asiri amma ki na ta ƙoƙarin tona wa kanki asiri ga idon duniya, wai ina hankali da tunaninki suka yi ƙaura suka tare ne? Ina wannan ilmin nakin da sanin ya kamata da kowa yake yabanki da shi?. Idan kin zaɓa ki guje mana a wannan karon kam ba zan yi ƙoƙarin dakatar da ke ba, tun da ba ki duba wahala da tudu da gangaran da muka bi kafin har muka gano inda kike rayuwa muka zo domin tsamo ki daga halaka ba, idan a baya mun yi miki uzuri akan duk abin da kika aikata tare da danganta hakan da cewar damuwar da kika tsinci kanki, zafin mutuwar mahaifinki da kuma raɗaɗin kalaman da mahaifiyarki ta furta a gare ki su suka haɗu suka yi taron dangi wajen ingiza zuciyarki har kika aikata abin da kika aikata. Wallahi a yanzu idan kika ƙara gangancin ƙara aikata wani kuskure babu wanda zai yi miki uzuri. Amatullah ba mu zo don mu tursasa ki ba amma tun da har yanzu zuciyarki ta na kitsa miki ki sanya ƙafa ki guje mana ba za mu yi miki tilas ba rayuwarki ce ki na da dama da ikon ki yi duk yadda kike so. Ki na da ikon ki zartar da duk wani hukunci da kike tunanin ya fi dace wa da rayuwarki tun da mai ɗaki ai shi ya san inda yake yi masa yoyo, ga hanyar nan ki tafi duk inda kike tunani da zaton za ki sama kwanciyar hankali daman fatanmu a ko yaushe bai wuce ki yi rayuwa cikin nutsuwa ba, sai dai a duk lokacin da kika nemo mu don mu zame miki gata tabbas za mu ba ki mafaka don na yarda da wannan karin maganan da ake cewa hannun ba ya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar. Kuma babu inda za ki je ko juyin zamanin da zai sa mu sauya ki daga kasancewarki ƴar uwa kuma jininmu. Don haka zaɓi ya rage ga mai shiga rijiya".

Yana rufe bakinsa daidai lokacin da Amir ya iso wajen duk ya bi mu da kallo kafin ya ce"Yaya ya na ganku a nan a tsaye? Ko dai an sallame ta ne?".
"Ba a sallame ta ba Amir ta dai sallama kanta ne, tun da har ta na ƙoƙarin guduwa".
"Guduwa kuma? To in ta gudu ta je ina?"
Cikin da takaicin da ya haɗe da tarin baƙin ciki Yaya Alhassan ya ɗage kafaɗunsa alamar mai sani ba a hankali ya furta"ga ka ga ita sai ka tambaye ta, ta ba ka amsa don ni kam na gama magana da ita sai dai na saurari hukuncin da za ta yanke". Yana dasa aya a zancensa ya juya ya koma cikin asibitin na lura kafin ya gama maganar har sai idanunsa suka kawo ruwan ƙwalla. Na durƙushe akan gwiwoyina sakamakon gazawar ƙafafuna yayin da na fashe da wani kuka mai rikitarwa da narkar da zuciyar mai saurare. Ina iya jiyo sautin ajiyar zuciyar da Amir ya saka kafin ya soma magana cikin sanyin jiki da na murya.

"Amatullah rayuwar da kika zaɓa wa kanki ke nan kuma ki na tunanin wannan hanyar da kika kai hanya ce mai ɓullewa?. Tun ranar da muka wayi gari babu ke tun daga wannan ranar ba mu ƙara yin bacci cikin salama ba, duk ranakun duniya kanmu muke zargi akan duk wani halin da kika tsinci kanki a ciki, kan mu muke ɗaura laifi tare da lashen takobin nemo a duk inda kike a cikin duniyar nan matuƙar ki na numfashi". Shi ma ya dasa aya a zantukansa ya juya ya bi bayan Yaya Alhassan ransa a matuƙar ɓaci idanunsa sun kaɗa sun yi jajir da su tamkar wanda aka watsa masa tsakin garin niƙaƙƙen barkono a cikin idanunsa.
Ji na yi kaina ya yi dum tamkar wacce aka ɗaura wa dutsen zuma. Na soma kokuwa da numfashina da yake maƙale mini a ƙirjina da na ji kamar an sanya taɓarya an tokare mini ƙirjin, jikina gabaɗaya ya ɗauki rawa dole na tashi daga wajen sa boda hanya shiga da fita da mutane suke ta zirga-zirga a wajen. A hankali na soma tafiya bayan na ɗauki hanya komawa cikin ɗakin da na fito yayin da zantukan Yaya Alhassan suke yi mini amsa-kuwwa a cikin kunnuwana tamkar a lokacin kalaman suke ratsa tsakanin leɓɓansa suka fitowa a wannan lokacin.

Ko da na iso ƙofan ɗakin sai na dan yi jim ina daidaita nutsuwata kafin na turo ƙofar ɗakin na shiga bakina ɗauke da siririn sallaman da ya tsaya iya kan leɓena.
Ba su amsa mini ba illa zuba mini ido da suka yi kaman yau suka fara ganina kaina na rusunar ƙasa sa boda na rasa ƙarfin gwiwan da zan iya haɗa ido da su. Jikina ya soma rawa da hakan a tursasa mini durƙushewa akan gwiwoyina ina wani kuka mai tsananin ƙarfi duk yadda na so na yi magana bakina ya ƙi haɗin kai wajen lanƙwansa harshena balle har sautin maganan ya fita ta yadda za su iya ji abin da na furta.
Gabaɗayansu suka yi shuru babu sautin da yake tashi a ciki ɗakin face sautin kukan da nake yi mai matuƙar cin rai na ɗau lokaci ina kukan tamkar raina zai yi bankwana da gangar jikina kafin can na tsinkayo amon muryan Yaya Alhassan a kaurare ciki tsare gida babu alamar wasa ko kaɗan a tattare da shi.

"Ki hanzarta ki sanar da mu hukuncin da kika yanke, don mu ma mu san inda dare ya yi mana".

Sai da na ja dogon numfashi mai nisan zango kafin na sama zarafin raba tsakani haƙwarana da suka manne da juna tamkar waɗanda aka sanya mayen ƙarfe a tsakaninsu.
Cikin raunin da yake fito wa kai tsaye daga ƙasan zuciyata ba tare da wani shamaki ba na ce"don Allah ku yi haƙuri ku yafe mini na san na baƙan zuciyoyinku....". Ya ɗaga mini hannu alamar ba ya son jin wani abu daga gare ni.
"Ba wani dogon jawabi muke buƙatar ji daga gare ki ba Amatullah. Hukuncin da kika yanke kawai muke son ji shin kin zaɓa ki ci gaba da rayuwa a nan inda muka same ki, ko kuma za ki haɗa kayanki mu koma gida gaban iyayenmu mu rayu cikin farin ciki da sanyawar albarkarsu a gare mu? Don ke yanzu ba yarinya ba ce babu wanda zai yi miki dole balle har ya tursas ki ki aiwatar da abin da ba kya ra'ayinsa". A kufule ya ƙare zancen cikin zafin rai tamkar zuciyarsa za ta fito waje tsabar tafasar da take yi, lamarin da ya ƙara azalzalan ruhina hawayen da nake yi suka ƙara karfin gudu suna zuba daga cikin idanua tamkar bakin indararo.

"Na amince zan bi ku mu koma gida tare". Na yi furucin muryata a shaƙe tamkar kwaɗon da aka danna kansa a cikin ruwan zafi. Duk su biyun suka yi shuru kafin can Yaya Alhassan ya ce"kin amince da hakan har cikin ranki ko kuwa dai kawai babu yadda kika iya? Don wallahi ba zan ɓoye miki ba tun da na ga kin yi ƙoƙarin guje mana daga cikin asibitin na ji gabaɗaya gwiwoyina sun yin sanyi ba na son mu yi miki tilas kuma daga baya a zo ana dana sani da cizon ɗan ƴatsa". Na zuƙe majinan kukan da ya zo mini kafin na sama damar cewa"na amince wallahi". Na ƙare zancen cikin karyewan zuciya da rashin ƙwarin jiki.
Kafin su ce wani abu aka buɗo ƙofar ɗakin aka shigo tare da yin sallama da tashin farko na gano muryar Zinariya ce, duk sai da ta gaishe su kafin ta tambayi ya ya mai jiki, Amir ne ya amsa da cewar da sauƙi. Duk suka miƙe tsaye Yaya Alhassan yana faɗin"bari na je wajen Likitan ya ba mu sallama". Amir ya rufa masa baya suka fita tare suka bar ni daga ni sai Zinariya zaune a cikin ɗakin, ita ta taimaka mini na tashi na zauna daga durƙushewar da na yi na jingina bayana jikin matashin da ta sanya mini a bayana don na ji daɗin zaman, na lumshe idanuna yayin da wasu hawaye masu zafi suke fitowa daga cikin idanuna da nake jin sauƙar su bisa fatan fuskana tamkar sauƙan tafasasshen ɗanyen ruwan dalma mai turiri.

"Ya ya jikin nakin?".

"Da sauƙi". Na amsa da shi ba tare da na buɗe idanuna na gan ta ba.
"Wallahi gabadayanmu mun tsorita da irin yanayin da kika shiga lokaci guda fa kika fita daga cikin hayyacinki, babu wani wanda zai gan ki a wannan lokacin ya tsammata miki za ki ƙara yin numfashi ko da na sakon ɗaya ne a cikin wannan duniyar. Waɗannan mutanen da suka ikirarin cewar su ƴan uwanki ne su ne suka kawo ki asibiti tare da ni aka yi komai don jiya har sai dare kafin na bar cikin asibitin nan, don Likitotin sun ce babu wanda zai kwana a wajenki. Waɗannan mutane sun nuna miki ƙauna mai ƙarfi da ta amsa sunanta, a dai cikin wannan duniyar da muke rayuwa a cikinsa da mutanen kirki suka yi ƙaranci da wuya a sama masu kirki da tausayinsu. Daman ki na da ƴan uwa maza ne? Don a labarin da kika ba ni kin ce ke ce ɗiya ɗaya tal a wajen iyayenki?".
Na furzar da iska mai zafi daga bakina kafin na soma ba ta amshoshin tambayoyinta.

"Tabbas kam yadda suka ce su ɗin ƴan uwana ne, sai dai ba muharramaina ba ne. Mahaifiyarsu ce yayar mahaifina uwa ɗaya uba ɗaya. Mai farin kayan shi ne Yaya Alhassan wanda aka so haɗa ni aure da shi ɗayan kuma ƙaninsa ne Amir wanda yake bin bayansa, idan ba ki manta ba su ma na ba ki labarinsu".
Cike da mamaki ta riƙe haɓa"yanzu Amatullah wannan zankaɗeɗen saurayin kika ƙi aura? Shi kuwa me ye laifinsa? Ga shi da kyau, ga ƙira da kuma kwarjini da ɗin da ɗawa ga kuma daɗin murya". Jinjina kawai na yi ba tare da na ce da ita uffan ba don na lura da yanayinta ko da na cewa wani abu, ba lalle ba ne ta fahimta balle har ta fahimci halin da zuciyata take ciki.

"To yanzu me ye dalilin wannan zuwan da suka yi? Don fa sai da aka ɗeba ƴan kallo tsakaninsu da Hajiya Babba ta yi musu tijara mai wasali, wannan ƙaramin har sai da ya fusata ainun don har sai da ya yi yunƙurin kai mata mari Aminu ya amshe cikin faɗan. Nan ta tada tijarar sai an biya ta kuɗin hayan ɗakinta da kika zauna a cikin kaf, Aminu ya bijiro da na shi buƙatar sai da aka biya shi wai kuɗin ɗawainiyyar ciyar da ke da ya yi a lokutan baya. Take suka karɓa lamban asusunsu suka tura musu kuɗin, kafin Hajiya ta bari suka kawo ki wannan asibitin ta kuma gindaya musu sharaɗin yadda suka fita da ke a cikin gidan nan, to su tabbatar da cewar kin fita ke nan har abada ko kin dawo sai dai ki nema wani masauƙin amma dai ba cikin gidanta ba".

Cike da damuwar da yake barazanar tarwatsa zuciyar da take kwance a cikin ƙirjina, na kai hannuna na dafe kaina da yake sarawa da ƙarfi.
"Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Me yasa Hajiya kuwa za ta yi mini haka?".
"Babu wani dalili illa na baƙin ciki da tsanar da ta yi miki tun farko, mussamman da kika ƙi bin layin da ragowar ƴan matanta suke bi. Ga ki da diri da kuma sura komai cif-cif kin ga kuwa ai da kin ba da kai bori ya hau ba ƙaramin harka za a buga da ke".

"Ai kuwa in sha Allahu na bar cikin gidanta ke nan har abada". Zinariya ta yi hanzarin tarar numfashina"ban ga ne kin bar gidan har abada ba ina za ki koma ke nan?". Na kwashe duk yadda muka yi da su Yaya Alhassan na sanar da ita, ina gama ba ta bayanin kawai na ga ta fashe da kuka sosai lamarin da ni ma ya saka ni kuka muka rungume junanmu babu mai lallashin wani a cikinmu.
Ni na fara yin ƙarfin halin tsagaita na wa kukan na ɗago kanta ina share mata hawayen fuskanta tare da faɗin"zan koma gida Zinariya Allah ya yanke mini wannan zaman ƙasƙanci da wulaƙancin. Ke ma ina mai ba ki shawara ki yi wa kanki karatun ta nutsu ki koma gida, na tabbatar da cewar iyayenki za su amshe ki".

Cikin muryar kukan da ya gama galabaitar da ita ta ce da ni"Amatullah ba zai yiyu yanzu in ce zan koma gida ba in kuma na yi yunƙurin hakan to ina mai tabbatar miki da cewar sai dai a komar da gawata. Sa boda mun riga da mun shiga cikin ƙungiya mun kuma yarda za mu yi biyayya ga dukkan dokoki da sharaɗoɗinta duk wanda ya ce zai fita to ɗayan biyu ne ko dai ya haukace ko kuma ya bar cikin duniyar gabaɗaya. Ke ma da ba kya cikin ƙungiyar ina jiye miki tsoron abin da Hajiya Babba za ta iya yi a kanki mussamman yadda suka yi musayar yawu da ƴan uwanki".

Gabaɗaya jikina ya yi sanyi ƙalau na kasa cewa komai har sai da ta ci gaba da maganar"ke dai Allah ya ƙaddara ba za ki saɓa masa ba ta hanyar keɓe wa da wani ɗa na mijin da ba halal ɗinki, ƙaddarar rayuwa a barikin ce kawai a kanki amma babu ƙaddarar saɓawa Ubangiji. Na taya ki murna da ba ki bari sheiɗan ya yi nasara akan yi ba haka nan ba ki taka rawa a lokacin da yake buga gangar sheɗancinsa ba, za ki koma gidan iyayenki cikin aminci da kuma mutunci Amatullah. Ga wannan wayar ki tafi da ita idan kin nutsu ki ba wa ƴan uwanki su saurari abin da yake ciki na san cewa za su fahimce ki". Tana gama maganan ta riƙo hannuna ta damƙa mini wayar yayin da ta fashe

27 / 39