Author : Maimuna Tijjani Iyam Category : Tknovels
kata a kunnenta.
Ban san me ye aka ce mata daga ɗayan ɓangaren ba sai ji na yi ta ce"Oga Deeno ke nan tun da na ce maka ba komai ai na tabbatar da cewar babu ɗin ne. Ni da kai ai ba a jin kanmu, yanzu dai yaushe ya kamata mu zo mu?".
Ta ɗan yi shuru kafin can ta ce"to shikenan in mun shigo zan ƙira ka". Daga haka ta kashe wayar ta mayar da idanunta gare ni.
"Ya ce mu je mu kaman ƙarfe takwas na dare".
Na jinjina kaina cike da gamsuwa"to Allah ya kaimu".
"Amin". Ta amsa da shi a taƙaice muka ci gaba da cin abincin, ji nake yi kamar a ranar lokaci ba ya yi gudu. Ina zaune bayan na gabatar da sallan zuhur a ƙofar ɗaki na yi sallan na zauna akan sallayan na buga tagumi, lokacin Zinariya ta fita za ta je ciro kuɗi.
Kyawawa ta zo ta tsaya a kaina na cira kaina ina kallonta tare da sauraron abin da take cewa" Ranki ya daɗe ki na ba baƙo a waje yana jiranki".
"Baƙo kuma?". Ta gyaɗa mini kanta cike da tabbatarwa tana ƙara wa da faɗin"ƙwarai kuwa ya ma daɗe ya na amfani jiranki da alama. Yana nan da motarsa mai zafi". Na taɓe bakina ina faɗin"babu wanda nake tsammanin zuwansa wataƙila wata yake nema ba ni ba".
"Amatullah fa ya ce yana nema. Kuma duk gidan nan babu wata mai irin sunan nan face ke ɗin dai".
A kufule na ce"ki je ki ce da shi ba na nan". Na yi maganar ina miƙe wa tsaye tare da ninke sallayar da na yi salla akan sa na yi shigewa ta cikin ɗaki na bar ta tsaye a wajen. Na zauna ina ta tunanai kala-kala babu jimawa ta ƙara dawowa ta shigo cikin ɗakin.
"Ranki ya daɗe mutumin nan fa ya dage akan ba zai bar ƙofar gidan nan ba har sai ya ganki, ya yi magana da ke".
Na buga tsaki"ai kuwa zai kwana a wajen, tun da ba shi da aikin yi".
Ta riƙe haɓa"ai kuwa ya yi kirarin in ba ki fito ba har shigowa ciki sai ya yi".
"Don Allah ki fita daga cikin ɗakin nan ki je ki sanar da shi abin da na faɗa miki".
"To shi kenan". Ta amsa da shi a gajarce tare da juya wa ta fice wa daga cikin ɗakin, na dinga buga tsaki kamar zan yi aman zuciyata tsabar takaicin da ya cika muni rai da ruhina.
Kamar wacce aka jefo cikin ɗakin Kyawawa ta faɗo cikin ɗakin kamar wacce aka wurgo ta. Na watsa mata harara"mene ne kuma?".
"Wallahi Ranki ya daɗe ya ƙi tafiya ga shi nan ma ya na shigo wa".
Ta na rufe bakinta na ga mutum zamgan-zamgan ya shigo cikin ɗakin, na yi zumbur na tashi tsaye da zummar ɗura ashariya sai dai mu na haɗa ido da shi na nema zancen na rasa ji na yi tamkar an rufe min baki baki. Na nuna shi da ƴar manuniyar ƴatsata cikin rawar murya da sarƙafewar harshe na furta"Saifullah kai ne? Me ya kawo ka cikin ɗakina?".
Bai amsa mini ba illa zara hannayensa da ya yi a cikin aljihun wandon farin shaddar jamfar da yake jikinsa ya zuba mini idanu, kafin daga bisani ya soma bin ɗakin da kallo.
Ya jinjina kansa kafin ya ce"a nan kike rayuwa ke nan?".
"Wannan ba abin da ya shafe ka ba ne ka fice miji daga cikin ɗaki, tun kafin na tara maka mutane na yi maka tijara".
"Magana na zo mu yi ki saurare ni". Ya yi maganar yayin da na ga yana ƙoƙarin zama akan kujerar roban da yake cikin ɗakin, na yi wuf na janye kujerar ina huci.
"Za ka yi kuskure idan ka sake ka ɗauki kalamaina a matsayin wasa, wallahil azim zan tara maka mutane idan ba ka fita daga cikin ɗakin nan ba. Me ye ya rage tsakanina da ku? Bayan kai ne mutum na farko da ka yi silar kawo komai ƙarshe. Me ya kawo ka cikin ɗakin karuwa mai zaman kanta mace mai mungun nufi? Ka fita daga cikin ɗakin nan kafin na yi mata akuyanci". Na ƙare zancen cikin ɗaga amo tare da runtse idanuna jikina yana cigaba da jijjiga tamkar ana jona mini shock ɗin wutar lantarki. Na ji an dafa kafaɗata na yi azama ture hannuna.
"Kar ka sake ka yi kuskuren ɗaura hannunka a jikina don sai na tabbatar maka da hakan a matsayi mafi kuskure girma da za ka yi a cikin rayuwarka na duniya. Ka fita daga cikin ɗakin nan ba na fatan Allah ya ƙara haɗa ni da wani daga cikin ahalinku balle har mu zauna inuwa ɗaya".
"Ke Amatullah wai me ye yake damunki ne? Da waye kike wannan batutuwan? Sannan waye ne ba kya fatan Allah ya ƙara haɗa ku da shi?". Na tsinkayo muryar Zinariya da hakan ya dawo ni cikin duniyar zahiri na buɗe idanuna da na runtse su na ga dai da gaske ita ɗin ce tsaye a gabana ta na kallo na kamar yadda ni ma nake kallonta. Sai da na yarce ruwan gumin da ya kwanta a saman goshina kafin na sama lasisin faɗin"ba kowa har kin dawo ke nan?". Na yi zancen ina wuce wa na zauna a bakin katifar ina ta faman mayar da numfashi.
"Wai me ye kike ɓoye min ne Amatullah? Na zo na same ki sai wasu suturai kike yi marasa kan gado ga kuma firgici a fuskarki amma ki na ce min ba komai".
Cike da ƙosawa da sauraron zancenta na ce"ba komai na ce miki in akwai a zan gaya miki". Daga haka na kwanta na juya mata baya na lumshe idanuna kamar mai bacci, sai dai musayar wuƙaƙe da mashin wutan da ake yi a cikin farfajiyar ƙirjina ba zai taɓa sauƙar mini da nutsuwar da zan iya runtsawa ko da na sankan guda ba ne. Ban ankara ba na ji wasu hawaye masu ɗumi su na sauƙar akan fatan fuskana. Abubuwan da suka wakana suka soma dawo mini cikin kwanyata.
Ko da na tashi na yi sallan asr ban ba wa Zinariya fuskar da za ta ƙara yi mini wani tambaya, sai da na yi har sallan isha'i kafin muka haramar tafiya otel muka shirya duk abin da mu buƙata muka rufe ɗakin muka tafi.
Muna sauƙa a bakin otel ɗin ƙiran Oga Deeno yana shigowa cikin wayar Zinariya ta ɗaga ta sanar da shi ga mu mun iso ya fito ya yi mana jagoranci har zuwa cikin wani garden muka zazzauna, ya soma yi mana jawabi.
"Yanzu haka shi da tawagarsa su fita zuwa gidan mai martaba amma ina da tabbacin zuwa karfe tara ko goma za su dawo, don haka zan san yadda zan yi na buɗe miki ɗaki ki shiga cikin kafin ya dawo, daga nan kuma ke kike san abin da za ki yi, san a kashe CCTV cameras ɗin dukka sashin. Ni da Zinariya kuma mu ma za mu keɓe". Cike da gamsu na ce"ba damuwa".
Ya ɗan sausata amon muryarsa"don Allah duk abin da za ku yi kar ki cutar da shi, kar ki yi silar da za ki ɓata min aikina ki wargaza min burin da na daɗe ina ginawa".
"In sha Allah babu abin da zai faru". Ya jinjina kansa alamar shi ma haka yake fata.
Muka tashi muka shiga wajen rukunin ɗakunan otel ɗin, shuru wajen yake don an sallame mi kowa babu wanda za a ƙara ba wa ɗaki a cikin VIP site ɗin har sai shi da tawagarsa sun tafi. Ya buɗe mini ɗaki yayin da Zinariya ta miƙo mini jakan jakan da yake hannunta wanda har da babban waya a ciki da ta sayo shi sabo dal da ta fita ciro kuɗi. Muka rumgume juna da ita tare da yi mini fatan alkhairi.
Na ƙarewa ɗakin tsallon tsaf tabbas ya tsaru iya tsaruwa, don babu wani abun buƙatan bisa mutum zai nema a cikinsa ya rasa. Na fito da kayan zan sauya daga cikin jakan, na ajiye shi a ƙasan gadon na shiga cikin banɗaki kamar yadda muka tsara.
Wanka na yi ƙirjina ya na buga wa duk kyawu da tsaftan banɗakin amma hakan bai hana ni ƙanƙaninsa ba, haka na yi wankan na gama na saka wani doguwar riga da ya kama jikina tam sai dai ya sauƙa mini har ƙasa na ɗaura ɗan mayafinsa a kaina. A ƙalla na yi mintin talatin a cikin banɗakin kafin na ji alama an buɗe ƙofar ɗakin an shigo, na yi maza na soma aiwatar da shirinmu na jawo towel ɗin da na gani lanƙaye a cikin banɗakin na ɗaura a kaina ina yi kamar ina tsane sumar kaina, na buɗe ƙofar na fito daidai lokacin da ya waigo muka haɗa ido ni da shi.
Tabbas shi ɗin ne tsaye a gaba ba gizo ba kuma ba a cikin mafarki ba, duk da har yanzu zuciyata ta na buga amma na dake na ci gaba takuwa cikin ɗakin yayin da duk ɗaga ƙafar da zan yi na sauƙe sai ya bi ni da kallo.
Gaban madubi na je na zauna ina kallonsa ta cikin madubin da har yake tsaye inda yake bai ko motsa ba, na sakar masa da wani laulausan murmushi mai kashe zuciyata kana na juyo ina yi masa wani shu'umin kallo.
Ya nuna ni da ƴatsansa zai yi magana na yi caraf na mashe zancen cikin faɗin"Amatullah".
"E na gane ki, amma me ye kike yi a nan? Ta ya ya kika shigo cikin ɗakin nan? Sannan mafi muhimmanci ma ya ya aka yi kika san da cewa ina cikin otel ɗin nan har kika gano ɗakin da nake?".
Na ƙara yin wani murmushin a karo na biyu kafin na ce"ban yi zaton waɗannan tambayoyin ne za su fito daga bakinka ba". Ya katse ni"wani tambayoyi ke nan kike so ji?". Ya ɗan ja numfashi sannan na furta"na za ta tambayata za ka yi shin dama har izuwa wannan lokacin ban mance da kai ba".
"Ina cikin da aka ce ki na ɗauke da shi?".
Ba tare da tunanin komai ba na ce"na zubar don zai hana ni rawan gaban hatsi ya kuma kawo mini cikas wajen cin duniyata da tsinke". Ya yi shuru kamar ba zai yi magana ba sai kuma ya ce"me yasa kika bar gida? Sannan da kika bar gidan ina kika koma da zama?".
Na kashe masa ido ɗaya kafin na ce"bariki na shigo ta yadda zan sama cikakken ƴancin kai".
Muryarsa babu alamar wasa ya ce"tashi ki fita daga cikin ɗakin nan". Na tashi daga inda nake zaune na iso gabansa na riƙe ƙugu ina faɗin"ai na ga waje babu inda zan fita". Bai ce da ni komai ya wuce ya shiga banɗaki da alama wanke fuskarsa ya yi ya fito ya ɗan yi turus da ya ganni har yanzu ina cikin ɗakin.
Ya nufi wajen wayar talhon da yake kan teburin ɗakin yana faɗin"bari na ƙira otel ɗin na ji uban waye ya buɗe miki ɗakin nan har kika sama damar shigowa". Na yi hanzarin miƙe na riƙe wayar"kar ka yi hakan don kamar ka ɗauki wuƙa ne ka daɓawa cikinka". Ina rufe bakina aka soma buga ƙofar ɗakin a hankali kuma a nutse, muka haɗa ido da shi"ana buga maka ƙofa ka je ka buɗe ko kuma ni na je na buɗe". Ya yi banza da ni da hakan ya ba ni damar juya wa da nufin zuwa na buɗe ƙofar ya yi hanzarin shan gabana.
"Me ye haka za ki yi?".
"Buɗe ƙofar mana zan yi". Na ba shi amsa cikin halin ko ina kula.
"Koma zan je na buɗe". Ya yi maganar a gajarce yana nufar ƙofar ya buɗe abinci aka kawo ya ƙarba ya shigo da shi ya ajiye akan teburi, muka tsaya mu na kallon kallo ga juna.
Ganin ba shi da niyyar jin komai ya sa ni zaunawa na soma bubbuɗe abincin, ya fi minti goma ya na kallona kafin ya koma cikin banɗakin. Hakan ya ba ni damar tashi na yi wuf na je na ɗauko jakar da na ajiye na ɗauko wannan ƙwayar da wannan wayar na ɓoye ta a jikina, na zo na jefa ƙwayar maganin a cikin ƙaramin flask ɗin ruwan shayin da aka haɗo tare da abinci na jijjiga kana na ajiye, na ja plate ɗaya na ajiye gabana na soma ci, a haka ya fito daga banɗakin ya same wannan karon da alama wanka ya yi don ya fito yana tsane fuskar da wani ƙaramin towel.
Ya zauna a kujerar da take saitina da na ɗago kai muka haɗa ido sai na sake masa murmushi na ci gaba da cin abincina.
Sai da ya gaji da kansa ya ce"me ya kawo nan? Me ye kike nema daga gare ni?".
"Ka ci abincin tukunna sai mu yi magana".
"Na fi buƙatar amsar waɗannan tambayoyin fiye da komai a yanzu".
"Ko kaɗan dai ka ci sai mu yi maganar". Ina gama maganar na ɗauki kofi na tsiyaya masa ruwan shayin wanda ina da tabbacin shayi ne na musamman kuma na girma aka yi masa. Na miƙa masa kofi ya ƙi karɓa ban yi ƙasa a gwiwa ba na ajiye masa a gabansa na koma na ci gaba da cin abincina.
A ƙalla ya yi mintuna ashirin kafin ya ɗauki kofin shayin, nan ma sai da ya daɗe da shi riƙe a hannunsa kafin ya kai bakinsa ya kurɓa, na ji wani sanyi a cikin raina tare da wani nutsuwan da ya yi bake-bake a cikin ruhina.
Sai da ya kusa sanye wa kafin ya ajiye kofin ya na kallona ya ce"ke nake sauraro".
Na ajiye cokalin da nake cin abincin da shi na ɗauki gorar ruwa na kora na yi hamdala kafin na dawo kan kujerar da yake kusa fuskantar wanda take zaune a kai na zauna.
[12/17, 4:47 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
©️ Maimuna Tijjani Iyam
______________________________________
Page 7️⃣1️⃣
Tagumi na zabga tare da zube idanuna akan sa yayin da shi ɗin ma ni yake ta faman kallo, cikinmu babu wanda ya ce uffan illa murmushin da yake ta sakar mini na lura izuwa lokacin maganin da na sanya masa a cikin lemon ya fara aikinsa a cikin jikinsa.
"Ka na ta kallona ba tare da ka ce wani abu ba, ahalin ka san cewa kai nake sauraro". Na yi zancen muryata can ƙasa ina sarrafa harshena cikin salo da hikima. Sai da ya lumshe idanunsa kafin ya cikin wani irin yanayi ya ce"Amatullahhhh".
"Na'am ya Sheikhi". Na yi caraf na amsa ina ka she masa ido guda da hakan ya ba shi damar soma zuba tamkar bakin indararo, hakan ya sa na yi wuf na fito da wayar da take jikina na danna recording na soma naɗar muryarsa.
"Amatullah na neme ki sosai bayan da na sama tabbacin cewar kin ɓace watau kin gudu daga cikin gidanku, kin bar gaban iyayen da danginki kin shiga duniya. Na ba za mutane ta yadda na ba da aikin nemanki a ko'ina sai dai har zuwa wannan lokacin babu wanda ya zo min da wani labari game da ke. Tun ranar da na fara ganinki a ciki wannan tashar ki na tallan kunu na ji cewar kin kwanta min a cikin raina, na ƙudurce cewar komai runtsi komai tsanani sai na cimma buri akan ki sai dai ke ce mace ta farko da kika fara karya alƙadarina da kuma ikirarin da nake yi wa kaina na cewa duk abin da na sa a gaba da niyyar mallakarsa babu makawa sai na same ko da kuwa nisan da yake tsakanina da shi ya kai tafiyar dake tsakanin nan inda muke zuwa cikin birnin sin. Tabbas a zahiri ni malamin addini ne a idanun duniya, ilmina ya jawo min girmamawa da mutuntawa daga wajen mutane da yawa wanda ko da a cikin mafarki ma ban taɓa tunanin zan ina saka kafata a inda suke ba balle har su ba ni wannan girman da mutuntawa, a idanun mutanen ƙasar nan ni mutum ne mai gudun duniya da kuma ruɗin da yake cikinta ni mutum ne kamili da duk wani abun cikin duniya bai dame ni ba balle ya ɗaɗani da ƙasa. Duk da kasancewa ta ba ɗan siyasa ba ne kuma ba ni da haɗi da gwamnatin da ayyukan da take yi amma ganin kimata da darajata da duniya take hakan ya jawo min kusanci da gwamnoni bila adadin ta yadda nake iya ganawa da su a duk sa'ilin da nake so, babu wata buƙatar da zan je da ita gabansu ba tare da sun kawar min da ita ba".
Ya tsagaita tare da yin wanin gatsa mai warin da ya tilasta mini ɗauke numfashina na wucen gadi idanunsa suna ta ƙoƙarin rufe wa amma ya na tilasta buɗe su tare da ci gaba da zance daga inda ya dakata.
"A zahiri ni malamin addini ne wanda ya ke kiyaye dokokin da ya shimfiɗa kuma ya yi hani da a aikata su, sai dai a baɗili ni ɗin tantarin manemin mata ne sai dai duk cikin wannan duniyar babu wanda ya san hakan don ni idan zan nema yarinya ba na zuwa inda aka san muryarta balle kuma fuskana, na fi mu'amala da matan ƙasashen waje mussamman ƙasar Ghana, Senegal da kuma Kenya sa bosa gudun matsala da tashin zance, sai kuma matayen can kugu su ma sai lokaci zuwa lokaci. Ke ce mace ta farko da na fara ƙyalla idanuna akan ta har na ji sha'awar kasancewa tare da ita a nan arewancin Najeriya, haka nan ke ce mace ta farko da na yi buri a kanta daga ƙarshe kuma ban same ta ba, a yadda na tsara ranar da ayi walimar yaye ku daga islamiyya a ranar zan kwanta da ke sannan na cusa miki tsoro da razani tare da fargaba a cikin ranki ta yadda ko bakin bindiga aka sanya miki a goshinki ba za ki taɓa ambaton sunana ba ko da kuwa maganar ta tashi asiri yana neman watsewa. Kwatsam sai kuma wannan abin mamakin ya faru".
Ta katse shi"wani abun mamaki ke nan?".
Ya kafe ni da