Bakar Fura Book Compelet

Author :  Fadila Lamido Category :  Read Hausa Novels

Chapter   16 / 34

45K to 48K   out of 101.2K words

yayin da take binsa
abaya tana share hawaye.

Har cikin gidan suka shiga yayin daya doshi wani babban kofa da akwatinta ahannun,
duk da cewa ma'aikata nata miko hannu yana girgiza kai.

Cikin wani katun falo suka bayyana yayin da taji ya ya bude murya yana Kiran Meenat.

******

Dirowa Meenat tayi daga gado, tana zare ido tare da kallon Islam tana fadin nashiga Uku,
kamar Yaya Haydar ne ke kira na, ko Baffah ne??

A'a kamar dai Yaya Haydar din ne.

Cikin zaro ido Meenat tace bantabajin ya Kira sunana ba, kefa Islam yana Kiran sunan
ki??

Kafin tabada amsa suka sakejin wani Kiran wannan karon duk su biyun ya Kira Meenat
Islam"

Kusan atare suka amsa tare da saurin fitowa.

Akwatin ya mikawa Islam dake gaba sannan ya kauce Aysha ta bayyana yana fadin, ga
bakuwa, kuje da ita dakin ku tai wanka taci abinci.

Amsawa sukayi, yayin da ya kalli Aysha yace ki bisu, kiyi wanka kici abinci.

Wucewa tayi kawai kamar yadda yace binta yayi da kallo har yanzun fushi take dan haka
yadanyi murmushi sannan yace nayi farin ciki da zuwan ki, cikin harcen fullacin.

Juyowa tayi tadan mai wani irin kallo wadda yasa shi ya sake sakin murmushi.

*********

Misalin 09:30pm Islam ta shigo tace muje Yaya na Kiran ki.

Wanni irin kallo taiwa islam cikin rashin fahimta.

Suna ko mgn taita mata ganin dai taki ganewa ta fito zuwa falon Haydar tana fadin, Yaya

inata mgn bata kulani.

Lumshe ido yayi tare da fadin bata jinki ne ki kamo hannunta kawai.

Ai har kamo hannun nata nayi taki.

Kawar da kansa yayi yai murmushi sannan ya juya yace, " kin iya french"

Meenat dai tanayi kadan kadan.

Kice mata tai mata french zata amsa ta.

Juyawa Islam tayi zuwa can saika Meenat da Ayaha, Aysha na shigowa Meenat ta fice, kallo
yaitabin Aysha dashi tsayon lakaci.

Itako zama tayi ta juyo masa baya tsayon lakaci yana kallon bayanta, zuwa can ya mike ya
dawo kusa da ita yana fadin"

Har yanzun kina fushi?, Aysha dan namiki fada kike fushi, har yanzun kina nan da halin ki
ko?

Hawaye ta fara sharewa can kasa da murya tace bakayi murna da ganina ba.

Inji waye ya gaye ya gaya miki?, Nayi farin ciki da ganin ki fiye da yadda kikai farin ciki da
ganina Aysha, nafi son ace nine nabiki ba kece kika biyoni ba, sabo da darajarki ta 'ya mace, ni
namiji ne dan nabiki ba wani abu bane, yanzun me kike tunani idan Kakarki ta fahimci haka??

Shiru Aysha tayi kwalla tap idonta.

Cigaba yayi da cewa nayi farin ciki da ganin ki, kin girma Aysha, amman farincin bashi zai
hana nagaya miki gaskiya ba, Ina son kisani cewa meson ka shine yake gaya maka gaskiya, kin
rigani kamo hanya ne kawai amman har yanzun kina zuciyata, yanzun mubar wannan mgnr Ina
Ummi na?, Kina ganin ta?
Batare data kalleshi ba tace muna haduwa a hanya.

Innawo fah?

Itama haka.

Har yanzun baki shiga gidan??

Kaita daga.

Baki Zaki bude inji muryan ki.

Ahankali tace ban sake shiga ba.

Wani irin kallo yake mata na kasan ido, cikn ransa yake yaba hallitan ta, Allah yayi mata sura
me kyau, da daukan hankali, tayi wankan ta, ta canja kaya, sai dai suma irin dinkin dazon din ne
duk sun kamata, dan karamin gyalene kawai tasa akanta ko dan kwali babu sai bakin sumsrta
yake hangowa yana kyalli
Kallonta da yayi na tsayon lokaci sosai ya saukar mishi da kasala irin wadda be tabajin
taba, cikin ransa ya raya inama ace matarsa ce ta aure suke zaune tare adaidai wannan
lokacin, idon sa ya sake kaiwa kan kirjinta ganin su cike tam yasashi saurin lasan leben sa
batare daya shirya ba, cikin ransa yake Kara tabbatarwa lallai Aysha itace matar daya dace ya
aura, duk da cewa abaya ba soyayya sukayi ba, amman yanzun ya tabbatarwa kansa cewa
yana son Aysha, haka itama ya tabbatar soyayya ce ta kawota wadda ada suke gani kamar
kauna ce.

Acikin ransa yaci gaba da cewa, yanzun haka take yawo a Cameroon, nonuna luntsum
lumtsum, kawar da kansa yayi zuwa can ya juyo idon sa cike da kishi yace"

Samarin ki nawa?

Juyowa tayi ta kalleshi, can kasa tace, "da yawa"

Da yawa ko?, har kina saurin fada?, ai daman nasan zasuyi yawa, tunda kina yawo ahaka,
kin gim katuwa dake kina yawo Kai ba dan kwali Koda dama can haka kike, baki damu da
suturta jikin ki ba, anan bazan yadda da wannan ba.

Cikin sauri ta sake juyo mishi baya akaro na biyu.

Mikewa yayi ya dawo gabanta tare da mika hannun sa ya roko nata, yatsunta ya rike yana
murzawa, karon farko arayuwar sa daya hakan taro dan haka yai saurin lumshe ido tare da
sauke ajiyan zuciya.

Ahankali yake murza hannun ta wadda zoben sa yake Kai, cikin matsanancin farin ciki yace,
" Aysha kin hadu, kin nuna min kauna, bazan taba mantawa dake ba arayuta, kina da kirki
Ayaha kina da nutsuwa ga kamon Kai, gakuma tarin ilimi, tunda muka rabo nake tunanin ki, ban
iya mgn da kowacce mace ba saike Aysha, nayi zamana ne kawai saboda Ummi ta nuna
zamana anan shine farin cikin ta, nasan Ummi tana son in rabo dake kamar yadda yan gidan ku
keson ki rabo Dani, Kuma haryau bandenajin abun da nakeji akanki ba kullum karuwama
yakeyi, dan haka naki dawowa kawai.

Hawaye Aysha ta share da hannunta daya cikin kasa da murya tace nima wlh Yaya ban
daina ba, Umma nata fada bana kula kuwa nikadai nasan abun da nakeji.

Hada kansa yayi dana Aysha yace nina fahimta Aysha, yanzun muyi tunani kina ganin
zamuyi aure?, iyayen mu zasu bari kuwa?

Kawar da kanta tayi ta share hawaye tana fadin bansani ba Yaya Aliyu��

Lumshe idon sa yayi sannan ya bude tare da share mata hawayen yana fadin, kidaina
kuka, insha Allahu zamuyi aure, Allah ne ya daura mana kaunar juna batare da yayi shawara
damu ba. Da yardan sa zamuyi aure insha Allahu dan ni Ina tunanin indai ban sameki ba
bazanyi aure ba, kefa Aysha zakiyi aure ki barni??
Kukane ya kwacewa Aysha dan haka tai saurin fadawa jikin sa, saurin rungumeta yayi tsam
ajikin sa tayon lokaci sannan ya shiga lallashinta daker ya iya yakeceta ajikinsa domin ji yake
kamar su dauwama ahaka.

Kije ki kwanta Aysha dare yayi. hannunta ya riko ya kaita har bakin dakin su Meenat saida
yaga shiganta sannan ya juya zuwa dakin sa.

Gado ya fada, yayin da yakejin tamkar Aysha ta fama masa ciwon dake karkashin zuciyar
sa, wani irin masifar sonta yakeji yana bin duk wani sassan jikin sa, wadda yakejin tamkar idan
aka hanasa aurenta zai iya mutuwa, gawani irin masifar tausayin Ayshan daya saukar masa,
ganin irin yadda ta sadaukar da rayuwarta takamo hanya, jikawai take ayanzun bashi da wani
babban buri daya wuce yaga ya mallaketa, tsintan kansa yayi da zubar da hawaye dan yasan
akwai babban aiki agaban sa, bayaga haka yau daya da ya hada jikinsa dana Ayaha duk yana
jinsa abirkice dan haka ya kwanta kawai yai rufda ciki yana cire kwallar dake taruwa gefen idon
sa.


****



Washegari da Safe, Aliyu ne zaune gaban Baffah yayin da Momy take gefen Baffah.

Cikin daure fuska Baffa ke fadin.

Kasan dai Ina da mutuncina ko?, Mutane suna ganina da daraja, nayi nayi dakai kayi aure
kaki, Ina lallabaka dan banson in takura maka, ko na hanaka aure ne??

Leben na kasa ya lasa sannan yace a'a.

Toh akan me zaka dinga lebo yaran mutane kana kawo min cikin gida?

Momy Aliyu ya kalla sannan yace wacce yariya na kawo?

Baffah ne yace ni zaka kalla ka tambaya yariya da kazo da ita jiya, ina ka samota ko hausa
bataji......








*️BA'KAR FURA️*
_A true life story_

*Na*
_Fadeela Lamido_


PEN WRITERS ASSOCIATION✍️

episode 30- 31

Dagowa yayi cike da kwarin guiwa yace Baffah matar aure ce ita, wannan yariyar tana da
aurenta, matar abokinace daga Cameroon suke, ita da Mijinta, tafiya ce takamashi zuwa garin
dabesan Ina zai sauka ba, gshi anan din ma batasan kowa ba, asalima bata hausa, shine ya
nemi da in kawota gidan mu ta zauna nawani lokaci kafin ya dawo, cikin baccin rai ya sake
cewa inda nemanta nake ai bazan kawota gidanmu ba, Kuma cikin kannaina Baffah, nadauka
cewar Ina da damar da zankawo wadda naso.

Ajiyan zuciya Baffah yayi, cike da gamsuwa yace, " nafahimta Haydar, kana da damar shigo
da duk wadda kaso kuwa domin gidan mahaifin kane, saidai inaga ba laifi bane dan naga
kamar zaka karkace natuhume ka, Kuma bayani yana da dadi, dole ne hankalina ya tashi ace
yau na samu labarin ka sauki mace bana miji ba, batare da wani bayani ba, ya dace ace da
abokin ka ya kawo matarsa ka kawoshi mugaisa, sannan ka sanar Mana cewa zaibar matarsa
anan, kamar yadda kai bayani yanzun, dan haka nan gaba ka gyara wannan kuskure ne.

Kansa akasa ya amsa da toh yayin da Baffah yace wane sunan yariyar??

Muryan Aliyu adakushe yace, " Sunanta Humaira"

Allah sarki, toh Allah ya dawo da mijin nata lafiya.

Dakai ya amsa sannan ya mike yayi sallama ya wuce Office.

Ajiyan zuciya yaketa saukewa ajijjere, wani na korar wani, yayin da yake bakin
cikin turkeshin da Baffah yayi tabbas yasan Momy ce ta zogoshi dan haka yaji abun nakara bata
masa rai, kenan dan iska suka maidani, irin wannan tunanin yaita yi yayin da yakejin ransa na
dada baci.

*******


Aisha zaune kusa da Islam, waige kawai Aysha take yau bataga Aliyu ba, hankalinta ne ya
fara tashi sai raba ido take, tun safe take sarai da ganin sa, gashi yanzun har sha daya, cikin
ranta ta fara tunanin gida Mama Umma acen bangaren Kuma ga Daddy ta duk tabarosu ta
tahonan da kudin data dade tana tarawa gashi yanzun har yanzun bataga Aliyu ba, wata
zuciyar ce tace mata yanzun idan be dawo ba fah Yaya zakiyi, ki koma gida?, hawaye taji ya
zubo mata sharrr, Hannu tasa ta share sannan tace duk acikin ranta, idan kin samu kudin motar
Ina zakibi kihau motar? kinsan hanyar tashan ? Me zakicewa masu mutar?, yin wannan tunanin
hawaye ya fara ziraro mata babu kaukautawa, Meenat ce ta kula tabajin kukanta kasa kasa
waigawa tayi ta kalleta cikin mamaki tace da Islam kuka take

Juyowa Islam tayi ta kalleta tare da tafata tana fadin kiyi hakuri baiwar Allah.

Meenat kuwa fadi take menene?

Islam ce tace ai kinsan baji take ba French Zaki mata.

Akace miki wani iyawa nayi?, ni bansan yadda zan lallasheta ba.


Islam ce ta saki bayan ta koma bakin gado ta zauna tana fadin, mudai mun shiga uku, ya
hadamu da aiki ya wuce aiki abun sa, ni wlh abun nan haushi yake bani, ace kaita mgn da
mutum besan me kake cewa ba.

Ayaha ko shashekar kuka take taree da Kiran sunan Aliyu, sunan kawai suke iya fahimta.

Meenat ce tace niman ya Haydar fa take bakijin tana cewa Aliyu ba, Islam kice mata yaje aiki
anjima zai dawo.

Cike da fada Islam tace ke meya hana kice mata, gaki kusa da ita.

Ai bajina take ba, Meenat ta bata amsa.

Mikewa Islam tayi tana fadin, toh ni Jim nawa take ne?, Kofa ta nufa tana fadin wlh ni dakin
Momy zanje inyi bacci na.

Dan Allah karki tafi kibarni da ita, bansan ya zanyi ba, ficewa Islam tayi, yayin da
Meenat ta kalli Aysha sannan itama ta fice adakin.

Gun Momy suka Isa kallon su haka yasa tace Yaya dai?

Momy kuka fa take, tana fulani ni bangane me take cewa in Banda Kiran ya Haydar.

Aiki ya sameku, saiku koma ku lallasheta Kar abokin Mijinta ya dawo yaci ubanku, dan
nikam karma kununa nasani, gara daku Niko idan ya wullo min wannan idon nasa, ba dai mgn
zaiyi ba amman akwai kallon raini.

Batare da sun fahimci inda tasa gaba Islam tace, " Wlh Momy bazamu iya ba, nidai gaskiya
nagaji.

Cikin sigan lallashi Momy tace kunga kuje ku zauna adakin, ko bakuce mata komai ba yafi
dai ace an barta ita kadai.

Da haka ta lalabesu suka koma.


Misalin karfe 4:30 Aliyu ya dawo gida, masifar kosawa yayi ya dawo sabo da Aysha kawai,
yana tunanin ko Yaya ta kwana, kawai ya iya daurewa ya barta ne dan Kar a fahimci akwai wani
abu a tsakanin su.

Kai tsaye dakin sa ya wuce bayan yama Momy dake falo sannu, cikin sauri sauri ya
shiga wanka, fitowa yayi yana tsane ruwan dake kansa, sannan ya shiga shiryawa, kananan
kaya yasa tare da fesa turare, kokarin fita yake yaga Aysha idonta a kunbure.

Murmushi yayi idonsa cikin nata, yana me tsareta da ido sosai yace ya dai naga kamar
kinci kuka kin koshi"

Kawar dakai tayi cikin sunkuyar da kanta kasa.

Meya faru ne?, nidai nasan Aysha jaruma ce an zanaki ma idon ki be kun bura haka ba,
gaya min waye ya bata miki rai.

Lumshe ido tayi hawaye suka zobo ahankali tace tunani nayi.

Motsowa yayi daf da ita yana fadin, " tunanin me?

Ka barni anan bani da kudin komawa gida, Kuma gashi

16 / 34