KIRJIN MAI HANKALI BOOK 2 COMPLETE HAUSA NOVELS PDF BY MX.txt

Author :  ms xoxo Category :  Tknovels

Chapter   8 / 40

21K to 24K   out of 119.4K words

suka faru a baya, amma ko daya daga cikinsu bai yi mata kama da dalilin da zai sa Hajiya Rumanah ta nemi hallakawa ba.

"Dole ne in samu amsar tambayoyi na," ta furta a hankali, amma da ƙuduri mai karfi. "Ba zan bar wannan lamari haka ba."

Duk da cewa sun tsira daga wannan haɗari, hakan bai nufin cewa sun gama da barazana ba. Har yanzu akwai Hajiya Rumanah a can, mai cike da makirci da sharrinta. Kuma har yanzu ba su san menene ainihin dalilinta na yin haka ba.

Hajiya Zaytunah ta matse hannun Nabeeha, sannan ta dube su Bala da Gora.

"Babu komai, Allah yana tare da mu. Yadda ya kubutar da mu daga sansanin yan fashi. Da yardar Allah zai karasa warware duk wani tuggu da makirci, sharri da ma sihiri da ake aikatawa da yardar Allah. Komai nisan dare gari zai waye..Allah zai bayyana gaskiya.. Kuma shi sharri dan aike ne..idan ka turashi karka rufe kofa zai dawo maka..."

_1-KALBIM:MAMUH GEE_

_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_

_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_

_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_

_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_

_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_

_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_

_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_

*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*

*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACCOUNT NAME/SUNAN DAKE ASUSUN BANKI: MARYAM SANI GUMMI*

*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
              _🧳👩‍❤️‍👨🌺_

*_The Vault Of His Secrets_*

_®️NANA HAFSATU (MX)_

_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_

*_BOOK TWO_*


_PAGE: 12_


Suna isa wani wuri da ke da nisa da inda aka tsare su, inda Bala da Gora suka tanadi wani tsohon gida mai matukar kango. A nan suka tsaya domin su huta, kuma su tattauna gaba ɗaya a kan matakin da ya kamata su ɗauka.

Hajiya Zaytunah ta kalli su Bala da Gora, zuciyarta na tafasa da mamaki da kuma fushi. Duk da cewa sun kubuta daga sansanin yan fashin suna dai cikin dajin. har yanzu ba ta iya fahimtar dalilin da yasa Hajiya Rumanah za ta nemi hallakata ba...

“Bala, me yasa? Me nayi mata da har ta tsaneni haka ita wadda ta turo ku?”

Bala ya yi shiru na ɗan lokaci, yana nazarin yadda zai bayyana gaskiyar. Gora ya jefa masa harara, yana son ya yi magana kawai. A karshe, Bala ya numfasa sannan ya ce,

“Akwai wata magana da na ji daga bakin shugabanmu kafin a kawo ku. Yana cewa Hajiya Rumanah tana tsoron cewa idan kika ci gaba da rayuwa, to akwai wani babbar SIRRI da zai tonu.”

Hajiya Zaytunah ta runtse ido, zuciyarta na kara harbawa da sauri. SIRRI i? Wane irin SIRRI ne hakan?

Nabeeha, wadda ke zaune a kusa da ita, ta dafa hannunta.

“Ammi, ko da wasa ban taba tunanin cewa yar uwarki ta jini za ta iya yin haka ba... shine dalilin daya sa bamu san su ba kenan? ”

Hajiya Zaytunah ta girgiza kai.

“Ni ma haka. Amma yanzu dole ne mu san komai... Dalilai da yawa Nabeeha. Amma kwata kwata bana Saka rumanah aciki. Nasan akwai zazaafar gaba da take yi akai na..Amma bansan ta tsananta haka ba"

Bala ya kalli Hajiya Zaytunah kai tsaye.

"Hajiya, kin taɓa jin wani abu game da wata mata da ta bata a baya?"

Hajiya Zaytunah ta cika da mamaki.

"Yarinya? Wacece kuma?"

Gora ne ya amsa da wata irin murya kamar yana kokarin kauce wa wata masifa. "

A cewar shugabanmu, akwai wani SIRRI da ke tsakanin ku da Alhaji Uzairu wanda ya shafi wata mata da ta bata shekaru da suka wuce. Kuma ana zargin cewa idan kika ci gaba da rayuwa, akwai yiwuwar gaskiya ta bayyana."

Hajiya Zaytunah ta runtse ido, zuciyarta na dukan uku-uku. Yarinya? Ko dai babbar mace...Hmm Me ya faru? Sai dai wani abu yana dawowa cikin tunaninta, tsohuwar rayuwarta a gidan Alhaji Uzairu. Shekaru da suka wuce, akwai abubuwa da suka faru da ba ta taba tunanin za su iya dawowa gare ta ba.

Nabeeha ta kalli Ammin ta da damuwa.

"Ammi, ko akwai wani abu da kike tunawa?"

Hajiya Zaytunah ta dago kai, idanunta na cike da ruɗani.

"Ban da tabbas... amma ina jin cewa akwai wata babbar magana da ban sani ba."

"Shin wannan wane SIRRI ne haka ammi?" Hammad ya tanbayi mahaifiyar sa yana jujjuya zancen a fatar bakin sa...

"Tarin SIRRI ka ne da yawa Hammad. Wanda ni kaina bazan iya gaya maka takamaimai yadda suke ba. Amman nasan akwai boyayyen lamarin dake faruwa Wanda yasa ta hauhawa haka"

"Kaico rayuwar duniya kenan. Da ya yi kokarin kashe mahaifinnsa ko mahaifiyar sa. Yan uwa su cinye gadon marayu.. Sannan dangi su nemi kashe dayan su saboda abunda suka qudirar na daga dukiya da sauran su" gora ya fada yana furzar da iskar bakinsa.

🎀🎀

A cikin dakin shakatawarta, Hajiya Rumanah tana tafiya a zage-zage, zuciyarta cike da tsana da fushi. Ta kasa zama, ta kasa natsuwa. Labarin da ta samu a safiyar yau ya dagula mata lissafi, ya ruguza duk wata kwanciyar hankali da take da ita.

"Suka tsira?😂!" Ta furta cikin matuƙar mamaki da takaici, tana watsa kwanon shayi da ke gabanta. "Su suka tsira?! Me kuke nufi da hakan?"

A gefe, Hajiya Karama da Ladi suna tsaye cikin nutsuwa, suna kallonta da mamaki. Sun san cewa yau Hajiya Rumanah tana cikin wata irin damuwa da ba ta taɓa shiga ba.

"Wallahi ba zan taba bari su tsira ba! Ba zan bari wannan masifar ta cigaba ba!"

Ta ja tsaki mai karfi, ta dafe kanta kamar wacce ke jin zafi kwakwalwarta. "Me yasa ita ce kullum ke ci min buri?!"

Hajiya Karama ta dan rankwafa. "Hajiya, ki kwantar da hankalinki. Me zai hana mu sake daukar mataki?"

Hajiya Rumanah ta juyo da mugun kallo.

"Mataki? Mataki?! Me kika san game da mataki? Kin san tun daga ina wannan masifar ta fara?"

Ta ja kujera ta zauna, amma har yanzu jikinta yana bari saboda takaici. Ta dubi su da idanuwan da suka cika da tsana.

"Kullum ita ce matsalata tun farkon rayuwata! Mahaifiyarta ta aure min mahaifi! Babana wanda ya fi kowa so, mahaifiyarta ce.. Tun daga ranar muka dena zaman lafiya."

Ladi ta waro ido. "Anya kuwa?"

"Eh! Zahiri! Da mahaifiyarta ta zo, sai mahaifiyata ta koma kaskiya! Komai ya canza, babana baya shiri da mahaifiyataa, sai dai ita!"

Ta numfasa da karfi, kamar wacce ke jin zuciyarta tana kuna.

"Mahaifiyar ta. Shegiya la'ananniya data haifo mana dangin jaraba da kulafici. Kanin mahaifina ne mahaifin ta. Bayan rasuwar sa sai mahaifiyar ta aure babanmu..a baya bakuga mutuncin da ake ba. Gidanmu daya ashe ashe jira take dama tana sonsam mijinta na rasu ta aure babanmu. Kunji cin amana daya?"

Hajiya Karama ta dafe baki. "To amma menene hakan ya shafe ki?"

Hajiya Rumanah ta yi dariyar takaici. "Me yasa ba zai shafe ni ba?! Dole ne nai kishi, dole ne na tsane su! Mahaifiyarta ta aure min mahaifi, ita kuma ta aure min miji!"

Ta runtse ido, ta kaɗa kanta da sauri kamar wacce ke jin wani abu mai zafi a kanta.

"Na rasa saurayi na saboda ita! Alhaji Uzairu ni zai aura a baya, amma sai gashi ita ya aura. Ni da nake jin shi ne kad’ai nawa, amma sai aka ɗauke shi aka miƙa mata!"

Ladi ta dan girgiza kai. "To yanzu ai duk ya wuce."

"Ya wuce?!" Hajiya Rumanah ta dauke mata kafa, ta watsa mata harara. "Kika ce ya wuce? Ai wannan shine babbar matsalar! Tun da na haifi Muhammad, na dauki alkawarin cewa shi zai fi kowa a gidannan. Sai gashi yanzu, dan cikina, jinina, shi ma yana bibiyar ‘yar Zaytunah?! Wacce iriyar bakar lukutar masifar kaddara ce wannan?"

Ta tashi tsaye da sauri, ta fara tafiya a cikin dakin, tana girgiza kai da takaici.

"Na rasa uba a hannunta. Na rasa miji a hannunta. Kuma yanzu har da dana? Har da Muhammad? Ku duba fa! Muhammad yana so ya auri ‘yar waccan munafukar? Wannan ai cin fuska ne! Baiwa ne aka raina!"

Hajiya Karama ta numfasa, tana kokarin kwantar da ita. "To ki yi hakuri. Muhammad ba zai aure ta ba."

"Da gaske kike?" Hajiya Rumanah ta watsa mata wani kallo mai cike da hauka. "Da gaske kike? Idan ban dauki mataki ba, Muhammad zai aure ta! Zai zama surikin Zaytunah, ni kuwa me zan zama?! Wai ni ce za a kira da uwar surikin yarinyar da mahaifiyarta ta kwace min rayuwa?"

Ta dafe KIRJIN ta, zuciyarta na bugawa da sauri. Tsananta, haushi, kishi, bakin ciki,duk sun taru suka mamaye ta.

"Wallahi bazan yarda ba. Bazan taba yarda ba! Ba za ta ci gaba da samun nasara a kaina ba!"

Ta dauki waya, zuciyarta na tafasa. "Dole a nemo su, kuma a wannan karon ba zan yarda a yi wasa ba. Idan har suka ci gaba da rayuwa, to hakan yana nufin cewa ni na gaza. Kuma bazan yarda da hakan ba!"

Sai a lokacin ta tuna yadda labarin ya zo gare ta. Akwai wanda ya sanar da ita cewa su Hajiya Zaytunah sun tsira daga hannun Gora da Bala. Wata zuciyarta na gaya mata cewa wani daga cikin mutanenta ne ya yi sakaci.

Ta kalli Hajiya Karama da Ladi da idanuwanta da suka yi jajir.

"Ku saurara! Ba zan yarda da shirme ba. Duk wanda ya saba umarnina, zai gamu da fushina!"

Ta matse wayarta a hannunta, zuciyarta tana tafarfasa. "Na tsani Zaytunah! Na tsani iyalanta! Kuma ko da wane hali, ba zan bar Muhammad ya aure Nabeeha ba! Ko da kuwa hakan na nufin... dole ne in dauki babban mataki!"

Ladi ta kalli Hajiya Karama da mamaki. "Kin fahimci inda zaytunah ke shirin dosa?"

Hajiya Karama ta jinjina kai, ta lumshe ido. "Eh... Kuma ina jin tsoron hakan."

Hajiya Rumanah ta ja numfashi, idanuwanta na dauke da mugun ƙuduri. "Wannan karon, Zaytunah ba za ta tsira ba."

Hajiya Rumanah ta zura ido cikin wayarta, zuciyarta na tafasa da tsana da bakin ciki. Ta san cewa idan har ta zauna kawai tana magana ba tare da ta dauki mataki ba, to hakan na iya zama dalilin da zai sa komai ya rushe mata. Dole ne ta dauki matakin da zai tabbatar da cewa wannan masifa ta kare nan take.

Ta latsa lambar daya daga cikin abokan huldarta a boye, tana jiran a dauka. Da zarar an daga, ta numfasa sannan ta furta cikin wata murya da ke cike da hadari,

“Ina son ku nemo min su. Ku kama su, amma a wannan karon, ba na son kuskure.”

A dayan bangaren, muryar wani namiji mai karfi ta amsa. "Kiyi hakuri hajiya"

Hajiya Rumanah ta cije lebenta. "Kun yi sakaci ne! Kuma wallahi ba zan yarda da hakan ba. Ku nemo su, a kawo min su da rayuwarsu, ko kuma ku tabbatar da cewa ba za su kara zama a doron kasa ba!"

"Za a yi aiki, Hajiya."

Ta kashe wayar tana mai huci. Idanunta sun kada suka yi jajir kamar wacce ke shirin fashewa da kuka saboda takaici.


Hajiya Karama da Ladi suna zaune a gefe, suna kallonta da damuwa. Hajiya Karama ta yi gyaran murya.

"Hajiya, kin tabbata wannan ne mafita? Balle kuma yanzu ana cewa Major General Dawud yana kokarin gano inda suke..."

Kafin ta karasa, Hajiya Rumanah ta juyo da wawan tsawa.

"Kada ki sake ambaton sunan wannan mutumin! Kada ki kuskura ki ce min yana kokarin gano su! Ko da kuwa zai shiga tsakaninmu, wallahi ba zan bari ya hana ni cimma burina ba."

Ladi ta hadiye yawu, ta dafe habarta. "Hajiya, amma ai su Major General ba kanwar lasa ba ne... idan suka sa baki a wannan al’amari, to kuwa zamu shiga matsala."

Hajiya Rumanah ta busar da iska mai karfi.

"Ni ce Rumanah! Ni ce uwar wannan gida! Me kuke tunani? Ku na zaton zan bar wata matsiyata da yaranta su cinye min duniya a ido?! Na rasa uba a hannun su! Na rasa miji a hannun su! Kuma yanzu ina da niyyar rasa dana? Ba zan taba bari hakan ta faru ba! Ba zan bari Muhammad ya auri waccan yarinyar ba!"

Ta koma kusa da Hajiya Karama da Ladi, ta kafa musu ido.

"Ku saurara, wannan karon ba zan tsaya da hannaye a kunne ba. Dole ne a dauki mataki. Idan har ba za a iya hallaka su gaba daya ba, to sai an ga yadda za a wargaza su. Sai an raba Nabeeha da Muhammad, koda kuwa hakan na nufin a bata ta!. Maganar dana yanke kenan dazu ban sanar muku na"

Ladi ta zaro ido cikin tsoro. "Hajiya! Kina nufin..."

"Kwarai kuwa! Idan har aka ci gaba da barin Nabeeha a matsayin budurwa, Muhammad zai dage sai ya aure ta. Amma idan aka bata ta, to ba zai kara kallo a kanta ba!"

Hajiya Karama ta girgiza kai. "Amma Hajiya, wannan ai..."

"Shiru!" Hajiya Rumanah ta katse ta da tsawa. "Babu wani abu da zai hana ni cimma burina. Ba na fatan ganin wannan matsala ta ci gaba! Idan har aka bar Zaytunah da yaranta su cigaba da rayuwa, wata rana su ne za su zama shugabanni, ni kuma in koma bakin ciki! Ni fa ba raini na ke ba!"

Ta dafe goshinta, tana jin zuciyarta na tafarfasa. Ta riga ta gama yanke shawara. Dole ne ta dauki mataki kafin lokaci ya kure mata.

"Ku jira. Zaku ga yadda zan sauya wannan al’amari. Idan har akwai wanda zai ci gaba da rayuwa a cikin wannan gida, to tabbas ba Zaytunah da yaranta ba!"

Ta daga wayarta, ta kira wani sabon mutum. Lokacin da aka daga wayar, ta furta,

"Kana buƙatar aiki?"

A dayan bangaren, wata muguwar dariya ce ta amsa mata.

"Hajiya Rumanah, ke dai kin san me kike so. Ba ki da wasa da mugunta. Ina sauraronki."

Shin Hajiya Rumanah za ta iya cimma mugun nufinta? Ko kuwa zata gamu da fushin Major General Dawud da mutanensa? Kuma shin Muhammad zai gano cewa mahaifiyarsa ce ke kokarin ruguza masa rayuwa?

Tirqashi🤭

_1-KALBIM:MAMUH GEE_

_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_

_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_

_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_

_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_

_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_

_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_

_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_

*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*

*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
              _🧳👩‍❤️‍👨🌺_

*_The Vault Of His Secrets_*

_®️NANA HAFSATU (MX)_

_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_

*_BOOK TWO_*


_PAGE: 13_


Hajiya Rumanah ta kashe wayar tare da wani murmushin mugunta. Idanunta sun cika da ƙuduri, kudurin ganin cewa babu wata hanya da za ta bari su Hajiya Zaytunah su tsira.

Hajiya Karama da Ladi sun kalle ta da mamaki, har yanzu sun kasa yarda da irin wannan matakin da take shirin ɗauka.

"Hajiya, ko kin tabbata wannan ne mafi dacewa?" Hajiya Karama ta tambaya cikin nutsuwa.

Hajiya Rumanah ta juyo da wani mugun kallo. "Da me kike nufi? Me kike tunani? Wannan karon ba na wasa! Babu wani 'hakuri' ko 'ji da mutane' a cikin lamarin nan!"

Ta ɗauki kofin shayi da ke gabanta, ta kafa kai, amma ba ta gama ba ta watsar da shi gefe. "Dole ne suyi nadamar zuwa duniya. Dole ne su fuskanci hukunci!" Baki daya a hautsine take..ta birkice tamkar mahaukaciya..

Ta ɗauki wayarta ta sake latsa wata lamba. Bayan an ɗaga, ta yi shiru na ƴan dakiku kafin ta ce,

"Dan Allah, A yanzu ina son ku sanya ido kan su Hajiya Zaytunah da yaranta. Ba na son a sake yin sakaci irin wanda aka yi da farko."

Muryar namijin a daya bangaren ta ce: "Ba matsala, Hajiya. Kawai ki bamu umarni."

"Dole ne ku kawo min wani abu da zai ruguza rayuwarsu! Idan har Nabeeha ta rasa mutuncinta, Muhammad zai ji kunyar kallon ta! Kuma idan hakan ta faru, da hannunsa zai gujeta!"

Hajiya Karama ta yi saurin kallonta. "Hajiya, wannan ai babban zunubi ne. Ko kin manta cewa Muhammad da kansa zai iya gano hakan kuma ya tsane ki?"

Hajiya Rumanah ta yi dariyar takaici. "Ke da kike tunani kamar mai hankali, tunani nawa kika taba yi da ya yi tasiri? Idan har hakan ya faru, ba za a san ni da hannu a ciki ba!" Duk fa tare muke shirya abubuwan nan da ku..kada ku manta dai kishiyar kuce tare kuke a zaune. Kuma mijin ku yafi kaunarta kamar ransa. Kawai dai saboda ku ba danku bane zai auri yar ta shisya abun baya damun ku. Allah ya kyauta"

"To idan kuwa haka ne, me zai hana mu bi hanyar da ta fi sauki?" Ladi ta tambaya, tana neman hanya mafi dacewa da zata iya hana Muhammad auren Nabeeha ba tare da tashe-tashen hankula ba.

Hajiya Rumanah ta girgiza kai. "Ba zan tsaya jiran lokaci ba. Ba zan ƙyale ta ta auri ɗana ba! Babu wata dabara da ta fi wannan! Idan kuwa hakan bai samu ba, to sai dai a kawar da ita gaba ɗaya!"

Hajiya Karama ta shiga tunani. "Amma fa Hajiya, idan har za a aiwatar da hakan, dole ne a tsara komai da kyau." Ta fada a sanyaye. Don kasurguman mugaye ne suma na kata'i. Amman a zahirin gaskia suna matukar tsoron hajia rumanah Kuma shakkarta. Komai tace binta sukeyi tamkar uwar data tsugunna ta haife su..

Hajiya Rumanah ta ja tsaki. "Ke dai ku jira. Ku gani yadda zan aikata hakan ba tare da an iya gano ni ba."

A zuciyarta, tana jin wani irin sanyi. Tana jin cewa wannan ne mafi dacewa. Wannan ne abin da zai saka ta samu nasara. Wannan ne zai tabbatar da cewa Zaytunah da Nabeeha ba su taba ruguza mata rayuwa ba.

"Za ku gani. Zan tabbatar da cewa babu wata hanya da za su sake tsira!"

Shin Hajiya Rumanah za ta iya aiwatar da shirinta? Ko kuwa wannan ne zai zama dalilin da zai kai ta ga halakar da kanta? Kuma shin Muhammad zai gano gaskiyar abin da mahaifiyar sa take aikatawa? 🤭

🎀🎀

Hajiya Zaytunah ta kasa motsi. Kamar wacce aka yi wa dukan gwiwa, ta zube a kasa, zuciyarta na harbawa da sauri. Idanunta sun kada suka yi ja, hawayen bakin ciki na cika su.

“Rumanah?” Ta furta a hankali, tamkar wacce ba ta jin abin da ta fada.

Rumanah? Yar uwarta ta jini. Yar yayan mahaifina. Matar Yaya Amiru . Aminiya ta tun muna yara. A rana daya aka haife mu, aka taso da mu tamkar yan biyu. A duk lokacin da aka tambaya wace ce Rumanah, sai a ce “wannan ce Zaytunah,wannan Rumanah.” Sun raba dariya, sun raba kuka, sun raba SIRRI ka har da burinsu na

8 / 40