da karfi ba, amma Hajiya Hawwa Maijiddah ta san cewa hakan ya fi komai nuna tsananin fushinsa. A karo na farko cikin shekaru da suka yi tare, ta fahimci cewa tana gab da rasa amanarsa gaba daya.
Ya nufi dakin sa na aiki, inda ya zauna a kan kujerarsa yana sake nazarin sakonnin da ya gani. Bai so ya dauki hukunci cikin fushi, amma dole ne ya san gaskiyar al’amari kafin lamarin ya fi kamari.
Ya sake duba lambobin da Hajiya Hawwa Maijiddah ta tura wa saƙonni. Lambar da ba ta da suna ta fi daukar hankalinsa. A matsayinsa na soja mai kwarewa da bincike, ba zai bar wannan lamari haka nan ba.
Major General Dawud ya dan jinkirta kafin ya kira Captain deen, domin ya san cewa idan ya dauki wannan mataki, komai zai sauya. Wannan ba matsala ce ta iyali kawai ba, matsala ce ta tsaro—wacce dole sai an dauki matakin gaggawa.
Ya latsa kiran, yana sauraron karar ringi. A lokaci guda, yana ta faman dannawa cikin wayarsa domin gano wata hanya da zai iya bin diddigin lambar da Hajiya Hawwa Maijiddah ta tura wa sakonnin sirri.
"Sir!" Muryar Captain Deen ta karade kunnensa, cike da girmamawa.
"Deen, ina bukatar bincike cikin gaggawa. Akwai lambar waya da zan tura maka yanzu—dole ne ka gano wa take da ita da kuma inda take aiki. Hakanan, ina bukatar ka bincika ko akwai wani shiri da ake kullawa da SIRRIN gidan nan."
"An gama, Sir!" Deen ya amsa ba tare da bata lokaci ba. "Zan tura bayanai cikin kankanin lokaci."
Major General Dawud ya katse kiran, sannan ya aika da lambar wayar. Yana gama hakan, sai ya lumshe idanuwansa, yana kokarin nazarin duk abin da ke faruwa.
Ya san cewa Hajiya Hawwa Maijiddah ba ita kadai ce ke da masaniyar SIRRIN Zaytunah da ‘ya’yanta ba. Idan har ta samu bayanai da yawa haka, hakan na nufin akwai wanda ke mata bayanai daga cikin gidan ko kuma daga wajen sa. Wannan ya kara masa damuwa.
Bai dauki lokaci mai tsawo ba, Captain Deen ya sake kiran sa.
"Sir, mun fara samun bayani akan lambar da aka tura sakonnin nan."
"Muna sauraron ka."
"Lambar tana da alaka da wata mace da ake kira Hajiya Rumanah. Matar da ke da dangantaka da wasu mutane masu tasiri a birnin mawii da Fubu. Tana kasuwanci, amma kuma ana kyautata zaton tana da alaka da wasu mutane da ke tattara bayanai na SIRRI."
Major General Dawud ya lumshe ido, yana jin yadda zuciyarsa ta kara tafasa.
"Kana nufin akwai yiwuwar Hajiya Rumanah na tattara bayanai akan Zaytunah da iyalanta?"
"Hakan yayi kama da gaskiya, Sir. Kuma abu mafi hadari shine, tana da alaka da wata mata, Hajiya Zaytunah... Gwaggo Zainabu... "
Dawud ya dan runtse ido. Wannan batu yana kara rikicewa. Gwaggo Zainabu? Me take da niyyar yi da Zaytunah? Kuma me yasa Hajiya Hawwa Maijiddah ke kokarin tona SIRRIN gidan?
Dole ne a dauki mataki cikin gaggawa.
"Deen, ina bukatar ka ci gaba da bincike cikin nutsuwa. Kada a bari wani ya gane muna kokarin gano gaskiya."
"An gama, Sir!"
Bayan kiran ya kare, Major General Dawud ya dauki lokaci yana nazari. Yanzu ya tabbatar da cewa Hajiya Hawwa Maijiddah na da alaka da Hajiya Rumanah, kuma hakan na iya nufin cewa tana da wani shiri da bata bayyana masa ba.
Ya mike tsaye a hankali, yana tafiya zuwa dakin da ya bar Hajiya Hawwa Maijiddah. Lokacin da ya isa, ya tarar da ita zaune akan gado, amma a bayyane take cewa hankalinta a tashe yake.
Ba tare da bata lokaci ba, ya zauna a gefen kujerar dake kusa da ita, yana kallonta kai tsaye.
"Ki gaya min gaskiya, Hawwa. Me kike nema?"
Tayi shiru. Ta ji nauyin furta komai, domin ta san cewa duk abin da zata fada, zai iya kara tsananta lamarin.
"Me yasa kike tura bayanai akan Zaytunah da iyalanta? Wace alaka kike da Hajiya Rumanah?"
A wannan lokacin, jikinta ya fara rawa. Idanunta suka kada, sai ta dan ja numfashi kafin tace:
"Dawud, ni ba nufina na cutar da kai bane. Ni dai kawai ina kokarin kare martabarka ne."
"Kare martabata?" Ya maimaita, yana kallonta da mamaki. "Ta yaya yin cin amana zai kare martabata?"
Hajiya Hawwa Maijiddah ta sunkuyar da kanta. "Ina jin tsoro. Ina tsoron cewa wata rana, Zaytunah da ‘ya’yanta za su kwace maka hankalinka har ka manta da ni da ‘ya’yanmu."
A wannan lokacin, Dawud ya yi shiru. Wani irin takaici da ba zai iya misaltawa ba ya lullube shi. Ashe saboda kishin duniya ne yasa Hajiya Hawwa Maijiddah ke aikata haka? Tamkar ya sharara mata uban Mari ya lakada mata duka yakeji. Cike da takaici yache,
"Ke kin san cewa tun farko ba ke kika kawo Zaytunah gidan nan ba. Kin san cewa mahaifiyata ce ta bukaci hakan. Ni na tsaya domin ganin cewa babu wanda zai cutar da ita, saboda sanin cewa ba laifinta bane aka jefa ta cikin wannan hali."
Ya girgiza kai. "Kuma ki sani, idan har ina da amana, babu wanda zai iya kwace martabarki a idona sai dai ke da kanki."
Hajiya Hawwa Maijiddah ta dan rusuna, zuciyarta na tafasa da tunani.
"Kiyi kokarin tunani, Hawwa. Idan har kika ci gaba da wannan makircin, ba ke kadai zai shafa ba. Idan aka gano cewa ke kika tona SIRRIN gidan nan, kin san me hakan ke nufi?"
Ta runtse ido, tana jin yadda maganganunsa ke sauka akanta kamar toka mai zafi.
"Da na fi so ki zo ki gaya min matsalarki, ba ki shiga wannan lamarin ba. Amma yanzu dole ne a dauki mataki. Kuma dole ne ki daina duk wani alaka da Hajiya Rumanah.
Bayan barin dakin, Major General Dawud ya nufi ofishinsa. Ya kira Captain Deen a waya. Domin ya kyale hajia hauwa Maijidda ne batare da ya sake mata wata barazanar ba so yake ya gama gano dukkanin kullalliyar da suke shiryawa itada mutanenta na cikin waya...
"Deen, akwai bukatar a ci gaba da sanya ido akan Hajiya Rumanah. Kuma ina so a san takamaiman abin da take nema da wannan bayanan."
"An gama, Sir!"
Yana katse kiran, ya mike tsaye yana nazari. Wani sabon shiri zai dauka. Domin yanzu ya fahimci cewa akwai wata babbar makarkashiya da ake kokarin kullawa a kan Zaytunah da iyalanta. Kuma ba zai bari hakan ya faru ba.
Ba tare da bata lokaci ba, ya fara tsara matakin gaba—wanda zai tabbatar da cewa ba wanda zai iya cutar da Zaytunah da ‘ya’yanta, ko da kuwa hakan na nufin yin abin da bai taba yi ba a rayuwarsa.
ADVERT👇
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
(THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME)
(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)
INA MA'ABOTA TURARE!
Shin kuna son gida mai ƙamshi da nutsuwa? Kaya masu ɗaukar hankalin kowa? YERWA INCENSE AND MORE ta kawo muku kayayyakin turaruka masu kyau, ingantattu, da tsada mai rahusa!
🌟 Mene ne za ku samu?
Turarukan wuta don gida, kaya, da tsugunno.
Khumrahs masu kamshi irin na Borno, Chadi, da Sudan.
Oil perfumes masu daɗin kamshi mai ɗorewa.
Turaren wanka, mopping, da wanki don dukkan sassan gida.
Man gashi mai gyara da fesa kamshi mai dadi.
Kayayyakin gyaran jiki na musamman don lafiya da ƙamshi mai ɗorewa.
📍 Adireshi:
Kano, amma muna tura kayayyakin mu duk fadin Najeriya da ƙetare.
📞 Tuntuɓe mu:
WhatsApp ko kira: 08095215215 / 09044191709 / 09134848107
Instagram: @yerwaincense_and_more
Facebook: @yerwacollection
Twitter:Hafsaaat00
🌐 Don ƙarin bayani da hotunan kayayyakin mu: Ku ziyarta mu a TikTok:
@besturarenwutainkano
https://www.tiktok.com/@besturarenwutainkano?_t=ZM-8s89xrbgS3x&_r=1
🎉 DON RAGI NA MUSAMMAN: Idan za ku siya, ku faɗi cewa daga ZAFAFA ne!
🌹 Ku more gida da jiki mai kamshi, nutsuwa, da farin ciki. Sai dai kayan turaren YERWA INCENSE AND MORE!
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:33_
Daren ya yi shiru, sai iska mai laushi da ke kadawa cikin lambun gidan. Wutar fitilun da ke zagaye da falon shakatawa sun haskaka fuskar Captain Fawaaz Dawud, wanda ke tsaye a cikin duhu, yana kallon sama kamar yana nazarin taurari.
A zuciyarsa, yana jin wani irin nauyi da bai taba jin irinsa ba. Nabeeha da iyalanta za su bar garin zuwa wani lokaci.. Wannan yana nufin cewa ba zai sake ganinta ba har sai Allah ya kawo wata dama.
Ya lumshe ido na wani lokaci, kafin ya juyo ya kalli hanyar da take tahowa. A kwance fuskar Dr. Nabeeha Uzairu Muhammad take, ba tare da wata damuwa ba. Amma idan aka kalli cikin idanuwanta, sai a ga wani irin soyayya da ke boye a zuciyarta, soyayyar da ta kasa furtawa da bakinta.
Bata gama karasowa ba, Fawaaz ya ji wani abu na taso masa daga zuciyarsa. Kafin ya ankara, sai da ya tsugunna a gabanta, yana kokarin saukar da idanuwansa cikin nata. He kneeled down on his knees .. begging for her love 🥹
Nabeeha ta tsaya cak, tana kallonsa da mamaki. Idanunta suka zaro da dan razana.
"Yaa fawaaz?"
Ya kasa magana na wasu dakiku. Hannunsa ya dan taba cinyarsa, yana jin yadda gwiwoyinsa suka daskare akan simintin.
"Nabeeha," ya furta da murya mai sanyi, amma wacce ke cike da nauyi. "Ba zan iya barinki ki tafi ba tare da kin san gaskiyar zuciyata ba."
Zuciyarta ta buga da karfi. "Gaskiya?" Ta furta a hankali.
Fawaaz ya saki wata ajiyar zuciya, yana kokarin danne nauyin da ke kansa. "Yes. I love you, Nabeeha. Ina sonki fiye da yadda kike tunani."
Hawaye ya cika idanuwansa. Duk da miskilancinsa, ya san cewa babu wata dabara da zai iya amfani da ita a wannan lokaci. Wannan ba fagen yin taurare bane, ba lokaci bane da zai boye soyayyarsa a karkashin kamun kai.
"Kiyi hakuri," ya ci gaba da magana, muryarsa na rawa. "Na jima da fahimtar cewa ke ce kadai mace da zuciyata take bukata, amma na ki furta hakan."🤭
Ya runtse idanuwansa kamar mai jin radadi. "Na ki bari ki san yadda kike da muhimmanci a rayuwata. Amma a yau, ba zan bari ki tafi ba tare da kin san cewa ina matukar son ki ba."
Nabeeha ta saki numfashi, zuciyarta na kokarin daukar nauyin kalmomin da ta ji. Ba ta taba tunanin cewa Fawaaz, mutumin da ke da kamun kai da miskilanci, zai iya furta irin wadannan kalmomi ba.
"Yaa fawaaz… ka tabbata da abinda kake fada?" Ta tambaya cikin rawar murya.
Ya bude idanuwansa a hankali, yana kallonta da soyayya mai cike da tsafta.
"Yes, Nabeeha. I am sure. I have never been more sure about anything in my life."
Ta dauke kai a hankali, hawaye na taruwa a gefen idanuwanta. "Amma me yasa yanzu, Yaa Fawaaz? Me yasa sai a daren da zan tafi?"
Yayi murmushi, murmushin da ya fi kama da radadi fiye da jin dadi. "Saboda na ki amincewa da zuciyata tun farko. Saboda na dade ina kokarin danne soyayyarki a raina, amma sai gashi yanzu tana neman tarwatsa zuciyata."
Ya kara matsowa kusa da ita, yana kallonta da wani irin yanayi da ya sanya ta kasa dauke idonta daga nasa.
"Nabeeha," ya sake furta sunanta, yana shafar hancinsa da hannunsa. "Ba na so ki tafi ba tare da kin san cewa babu wanda yake son ki kamar yadda nake son ki ba. Ko da kuwa ba zan taba samun ki ba, na fi so ki tafi da sanin gaskiyar zuciyata."
Hawaye ya gangaro daga gefen idanuwansa.
"I love you, Nabeeha."
Ta dan rusuna, zuciyarta cike da shauki da soyayya. Bata san lokacin da hawaye ya wanke fuskarta ba.
"Na jima ina jin hakan, Ya Fawaaz. Amma ba na son yin kuskure. Ka yi min alkawari cewa ba ka da wata mace da kake so kamar yadda kake so na."
Ya daga hannayensa sama kamar yana yin rantsuwa. "I swear by Allah, ke kadai nake so, Nabeeha."
Ta shafi fuskarta da tafin hannunta, tana kokarin boye jin dadinta. "Na amince da kai, Yaa Fawaaz."
Wani irin sanyi ya sauka a zuciyarsa. Ya lumshe idanuwansa na wani lokaci, kafin ya bude su a hankali.
"Thank you, Nabeeha. Thank you for trusting me."
Suka tsaya suna kallon juna, kowannensu yana jin irin soyayyar da ba su taba bayyanawa da fadar magana ba. Daren nan ya dauke su a cikin shaukin da ba za su taba mantawa da shi ba.
Iskar dare ta ci gaba da kadawa cikin lambun gidan, tana tayar da sassanyar ƙamshin furannin da ke kewaye da su. Fawaaz har yanzu yana tsugunne a gaban Nabeeha, yana kallonta da idanuwansa masu cike da so da buƙatar ta fahimce shi.
She was standing still, her heart pounding wildly in her chest. Never had she imagined that Captain Fawaaz Dawud, the ever-mysterious, ever-distant man, would kneel before her and pour out his heart like this.🥹
Hannayensa sun yi sanyi a gefensa, yana kallonta da idanuwansa masu tsananin zurfi. "Nabeeha," he whispered, his voice laced with raw emotion. "I can’t let you go without telling you what’s in my heart."
A cikin zuciyarta, tana jin kamar zata daina numfashi.
"Yaa Fawaaz..." Ta kira sunansa da murya mai sanyi, idanuwanta cike da jin ƙauna da tsoro. "Why now? Why tell me this on the night I’m leaving?"
Yayi shiru na wasu dakiku, kafin ya saki wata ajiyar zuciya mai nauyi.
"Because I have been a fool," he admitted. "Because for too long, I let my pride and my fears stop me from saying what my heart has always known—I love you, Nabeeha. I love you more than I ever thought possible."
Hawayen da take ƙoƙarin hana su zuba sun gangaro a kumatunta.
"Fawaaz, you don’t know what you’re asking of me."
Ya girgiza kai a hankali, yana kallonta da kulawa. "I know exactly what I’m asking. I am asking you to believe me. To know that I have never felt this way about anyone before. And I don’t think I ever will."
Zuciyarta ta buga da ƙarfi. Tana jin cewa idan har zata amince da kowa a duniya, to Fawaaz ne.
"But what if fate separates us? Idan kaddarar mu bata haduwa bace ba fa?" Ta tambaya da murya mai sanyi.
Fawaaz ya ɗan saki wani murmushi mai cike da zafi. "Then I will fight for us. I will find you. I will prove to you that what we have is real. Ina matukar kaunar ki"
Ajiyar zuciya ta sauke, kafin ta ɗaga hannunta ta kama nasa. Wannan shi ne karo na farko da ta taɓa yin hakan, kuma jin sa a tafin hannunta ya sanyaya zuciyarta fiye da duk wani abu da ta taɓa ji.
"I won’t make promises, Yaa Fawaaz," she whispered. "But if we are meant to be, I believe fate will bring us together again."
He closed his eyes for a moment, as if letting her words sink deep into his soul. Then, slowly, he nodded.
"That’s enough for me, Nabeeha. That’s all I need to hear."
She smiled through her tears. "Take care of yourself, Yaa Fawaaz."
A hankali, ta janye hannunta daga nasa, sannan ta juya. She walked away without looking back—because she knew that if she did, her heart would never let her go.
Fawaaz remained on his knees, watching her disappear into the night. His heart ached with longing, but deep down, he knew one thing—what they shared was not something time or distance could ever break.🥹🤭
Fawaaz ya ci gaba da kallon Nabeeha har sai da ta bace cikin duhun dare. Wani irin sanyi da daci suka gauraya a zuciyarsa, yana jin kamar ba zai iya motsawa ba.
Ajiyar zuciya ya sauke, ya runtse idanuwansa na ɗan lokaci, yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi. "Ko da kuwa za ki tafi, Nabeeha," ya furta a hankali, "na riga na ajiye soyayyarki a zuciyata."
A can gefe, Nabeeha ta tsaya a bakin kofa, tana kallon sama. Ta lumshe ido, tana jin kalmomin Fawaaz na ci gaba da karade zuciyarta.
"I love you, Nabeeha."
Wani irin shauƙi ya ziyarci zuciyarta. Bai kamata ta yi tunanin cewa wannan rabuwa ce ta har abada ba, saboda zuciyarta ta riga ta gamsu da cewa Fawaaz yana sonta da gaske. Amma har yanzu, akwai abubuwa da yawa da ba ta fahimta ba.
Ta dan runtse ido, tana jin yadda zuciyarta ke bugawa. "Idan kaddara ta so, Fawaaz," ta furta a hankali, "to wata rana, za mu sake haduwa."
A can bayan ta, Fawaaz yana tsaye yana kallonta daga nesa, ba tare da ta sani ba. Bai san lokacin da ya runtse ido ba, yana jin wani nauyi yana danne zuciyarsa.
"I will wait for that day, Nabeeha," ya furta da wata murya mai sanyi. "No matter how long it takes."
Daren yana da shiru, amma zuciyoyinsu na cike da kalmomin da ba su fada ba. Wannan ba dare ne na rabuwa ba, dare ne na alkawari, na fata, da kuma soyayyar da lokaci ba zai iya rushewa ba.
ADVERT👇
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
(THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME)
(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)
INA MA'ABOTA TURARE!
Shin kuna son gida mai ƙamshi da nutsuwa? Kaya masu ɗaukar hankalin kowa? YERWA INCENSE AND MORE ta kawo muku kayayyakin turaruka masu kyau, ingantattu, da tsada mai rahusa!
🌟 Mene ne za ku samu?
Turarukan wuta don gida, kaya, da tsugunno.
Khumrahs masu kamshi irin na Borno, Chadi, da Sudan.
Oil perfumes masu daɗin kamshi mai ɗorewa.
Turaren wanka, mopping, da wanki don dukkan sassan gida.
Man gashi mai gyara da fesa kamshi mai dadi.
Kayayyakin gyaran jiki na musamman don lafiya da ƙamshi mai ɗorewa.
📍 Adireshi:
Kano, amma muna tura kayayyakin mu duk fadin Najeriya da ƙetare.
📞 Tuntuɓe mu:
WhatsApp ko kira: 08095215215 / 09044191709 / 09134848107
Instagram: @yerwaincense_and_more
Facebook: @yerwacollection
Twitter:Hafsaaat00
🌐 Don ƙarin bayani da hotunan kayayyakin mu: Ku ziyarta mu a TikTok:
@besturarenwutainkano
https://www.tiktok.com/@besturarenwutainkano?_t=ZM-8s89xrbgS3x&_r=1
🎉 DON RAGI NA MUSAMMAN: Idan za ku siya, ku faɗi cewa daga ZAFAFA ne!
🌹 Ku more gida da jiki mai kamshi, nutsuwa, da farin ciki. Sai dai kayan turaren YERWA INCENSE AND MORE!
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:34_
Daren ya yi nisa, iska tana kadawa a hankali, tana haifar da wani irin shiru mai cike da natsuwa da zurfin tunani. Fawaaz har yanzu yana tsaye a inda ya tsaya, hannayensa a cikin aljihunsa, zuciyarsa cike da tunani. Bai san tsawon lokacin da ya tsaya a wurin ba, amma abu ɗaya yake ji azuciyarsa ta makale a daren nan, a kalmomin Nabeeha, a yadda hawaye suka cika idonta lokacin da take fadin,
"Idan kaddara ta so, Fawaaz, to wata rana, za mu sake haɗuwa."
Ya sauke ajiyar zuciya, yana jin wani abu na fizgarsa daga ciki. Tun farkon saninsa da ita, bai taɓa tsammanin cewa wata rana zai iya tsugunawa a gaban