KIRJIN MAI HANKALI BOOK 2 COMPLETE HAUSA NOVELS PDF BY MX.txt

Author :  ms xoxo Category :  Tknovels

Chapter   27 / 40

78K to 81K   out of 119.4K words

ruwana!"

Duk parlorn ya cika da hayaniya, yayin da kowacce ke ƙoƙarin wanke kanta. Amma daga Alhaji Uzairu har Alhaji Amiru, babu wanda ya damu da jin bahasi.

Gwaggo Zainabu, wadda tun farko ke zaune shiru, ta dafe kai tana kallonsu da takaici. Tana jin kamar zuciyarta za ta fashe. Idanun ta sun ciko da hawaye.

A nan, Alhaji Amiru ya ɗaga hannu ya dakatar da hayaniyar, sannan ya dubi su da tsantsar ƙiyayya,

Gaba ɗayansu suka girgiza cikin matsanancin firgici. Babu wanda ya iya cewa komai, sai dai kuka da nadama. Amma ya riga ya kure musu.

Muhammad ya sunkuyar da kansa, yana jin wani irin bakin ciki a ransa. Yau ya ga wata fuskar mahaifiyarsa da bai taɓa zato ba. Yau komai ya gama tonuwa!

Gaba ɗaya falon ya dauki shiru na wani lokaci. Sai kukan Hajiya Ladi da Hajiya Karama ke tashi, suna durƙushe a ƙasa, suna roƙon Alhaji Uzairu da kada ya raba su da shi. Amma a yau, ba zai saurare su ba. Ya yi ajiyar zuciya, ya dubi su da kallon takaici, sannan ya ce da kakkausar murya,

"Kuka ɓata mini aure na, kuka raba ni da iyalina, kuka hana ni jin daɗin rayuwa na tsawon shekaru! To yau kun ga sakamakon abinda kuka aikata! A fitar mini da su daga gidana. Na sake ku Kuma saki uku uku!"

Jin haka yasa Hajiya Rumanah ta zabura da sauri, ta dubi shi da idanunta cike da hawaye. Tana neman mafita, amma babu ko ɗaya.

"Yaya Uzairu, ka saurareni! Ni ba ruwana! Ni fa su ne suka jefa ni cikin wannan fitinar! Dan Allah kabawa Yaya Amiru hakuri"

Ta nuna Hajiya Karama da Hajiya Ladi da yatsa, tana kallonsu da tsantsar ƙiyayya. Su kuwa suka yi saurin juyowa suna fadin:

"Karya take! Ita ce ta ja mu! Ita ce ta kitsa komai! Mu fa ba mu da hannu!"

Sai dai babu wanda ke son jin uzurinsu. Muhammad yana zaune a gefe, idonsa jajir, yana kallon mahaifiyarsa da matan kanin babansa suna zagin juna. A zuciyarsa, akwai bakin ciki da takaici. Mahaifiyarsa da yake ji da ita, ita ce jagorar wannan zalunci? Bai iya gaskata hakan ba, amma abun yana a bayyane.

Ya juya yana kallon Alhaji Amiru, wanda ke tsaye yana kallon su da ɗarɗar. Ya girgiza kai cikin takaici, sannan ya ce:

"Tun da kun ce ba ku da hannu a cikin wannan lamarin, to menene wannan?"

Ya ɗaga hannu ya nuna bokan da aka daure da ankwa, wanda ya tsaya a gefe yana kallon su da murmushin raini.

"Shin bokan ma ne ya ɓullo da kansa? Ko kuwa wani ya tura shi?"

Gaba ɗayansu sun toshe baki, sun kasa cewa komai. A yau, komai ya fito fili.

"Bari na baku labari!" Bokan ya furta da wata murya mai nauyi, yana kallonsu da raini. "Wadannan matan nan da kuke gani, su suka zo wajena, suka nemi a raba Zaytunah da mijinta. Suka nemi a tozarta rayuwarta, suka hana ta dawowa. Kuma suka ɗauka cewa za su ci nasara har abada. To yau, kuzo ku fuskanci sakamakon abinda kuka aikata!"

Hajiya Ladi da Hajiya Karama suka zabura da sauri suna girgiza kai.

"Wallahi ba mu da hannu!"

"Wannan boka karya yake! Bamu san shi ba!"

Hajiya Rumanah ma ta yi saurin cewa,

"Karya yake! Wannan sharrin ne ake son ɗaura mana!"

Sai dai babu wanda ya saurare su.

Alhaji Uzairu ya yi shiru na ‘yan mintuna, yana kallonsu da idanunsa jajir, yana tunanin rayuwarsa, da irin zaluncin da aka yi masa. Duk tsawon shekarun da ya shafe yana zargin Zaytunah, da tunanin cewa ita ce mai laifi, ya fahimci cewa ya yi babban kuskure.

"Kuka raba ni da iyalina," ya faɗa cikin wata murya mai tsanani. "Kuka raba ni da ‘ya’yana. Kuka saka na rayu cikin ruɗu da baƙin ciki. Yau kuma kuna son ku kare kanku da ƙarya? Ai ba zan yafe ba! Kullum ina addu’a Allah ya tona asiri, kuma yau Allah ya tona!"

Ya juyo ya kalli Alhaji Amiru da Major General Dawud, waɗanda suka tsaya suna kallon abin da ke faruwa.

"Wallahi duk yanda kuka ga dama, ku yi da su. Ni na rabu da su har abada!"

Ya juyo ga matansa, ya ɗaga murya:

"Na sake ku uku, saki uku-uku! Ku fice daga gidana!"

A take suka zabura, suka zube a ƙasa suna kuka, amma babu wanda ke son jin uzurinsu.

Gwaggo Zainabu, wadda tun farko ke zaune shiru tana kallonsu da takaici, ta dafe kai tana jin kamar zuciyarta za ta fashe.

"Ku tafi ku bar mu da rayuwarmu lafiya," Alhaji Amiru ya faɗa, yana juyawa ba tare da ya sake kallon su ba.

Hajiya Rumanah ta dubi ɗanta Muhammad, tana neman taimako a idonsa, amma ya ɗauke kansa gefe. Bai san me zai yi ba. Ya girgiza kai kawai, yana jin kamar zuciyarsa ta fashe da takaici.

A haka aka kori su daga gidan zuwa court.. Rayuwarsu ta rushe a take. Asirinsu ya tonu, aure ya ƙare, ƙiyayya ta girma. A yau, duniya ta sauya musu fuska.

Muhammad ya yi tsaki alokacin daya karasa kallon faifon bidiyon wajen. Ya danna dakatawa. Yana cije lebensa hadi da busa numfashi mai dumi daga bakinsa. Ransa baki daya a dagule yake. Wannan abubuwa da mahaifiyar sa ta aikata don kwa itace shugabar komai baki daya ya hargitsa masa duk wani lissafin kansa.... Ita tayi abun amma baki daya shi yake jin kunya!!!

Ya cigaba da kalla yana jujjuya kai cike da tsantsar takaici marar misaltuwa....

ADVERT👇

YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE

(THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME)
(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)

INA MA'ABOTA TURARE!
Shin kuna son gida mai ƙamshi da nutsuwa? Kaya masu ɗaukar hankalin kowa? YERWA INCENSE AND MORE ta kawo muku kayayyakin turaruka masu kyau, ingantattu, da tsada mai rahusa!

🌟 Mene ne za ku samu?

Turarukan wuta don gida, kaya, da tsugunno.

Khumrahs masu kamshi irin na Borno, Chadi, da Sudan.

Oil perfumes masu daɗin kamshi mai ɗorewa.

Turaren wanka, mopping, da wanki don dukkan sassan gida.

Man gashi mai gyara da fesa kamshi mai dadi.

Kayayyakin gyaran jiki na musamman don lafiya da ƙamshi mai ɗorewa.


📍 Adireshi:

Kano, amma muna tura kayayyakin mu duk fadin Najeriya da ƙetare.


📞 Tuntuɓe mu:

WhatsApp ko kira: 08095215215 / 09044191709 / 09134848107

Instagram: @yerwaincense_and_more

Facebook: @yerwacollection

Twitter:Hafsaaat00




🌐 Don ƙarin bayani da hotunan kayayyakin mu: Ku ziyarta mu a TikTok:
@besturarenwutainkano
https://www.tiktok.com/@besturarenwutainkano?_t=ZM-8s89xrbgS3x&_r=1

🎉 DON RAGI NA MUSAMMAN: Idan za ku siya, ku faɗi cewa daga ZAFAFA ne!

🌹 Ku more gida da jiki mai kamshi, nutsuwa, da farin ciki. Sai dai kayan turaren YERWA INCENSE AND MORE!

*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_

_🧳👩‍❤️‍👨🌺_

*_The Vault Of His Secrets_*


_®️NANA HAFSATU (MX)_


_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_


*_BOOK TWO_*


_PAGE:44_





Hajiya Rumanah, Hajiya Ladi, da Hajiya Karama suna durƙushe a ƙasa, kuka ya cika falon. Sun rasa yadda za su yi. Fuskokin su sun cika da hawaye, amma babu wanda ya nuna tausayi a gare su.

Muhammad ya dubi mahaifiyarsa da takaici. A zuciyarsa yana ƙoƙarin fahimtar yadda zata iya shiga irin wannan mugun nufi, amma babu amsar da ke da daɗi. Mahaifiyarsa ce, amma ta aikata abin da ba zai iya gafartawa ba.

Alhaji Amiru ya girgiza kai cikin takaici. "Ku fice daga gidana kafin na ƙara da hukunci mafi muni!"

Hajiya Karama da Hajiya Ladi sun zabura suna rarrafe suna roƙon afuwa.

"Don Allah, Uzairu! Don girman Allah, ka yi mana rai!"

"Wallahi ba mu da laifi! Hajiya Rumanah ce ta ja mu!"

Ita kuwa Rumanah ta zabura cikin zafin rai.

"Ku daina mini sharri! Ai ku kuka fara! Ku kuka ce za a hana Zaytunah dawowa! Ni fa ba ruwana!"

A take suka hau musayar zargi a tsakaninsu. Kowacce tana ƙoƙarin wanke kanta, amma babu wanda ya yarda. Sun ruguza rayuwar wasu, yau kuma rayuwarsu ce take rushewa.

"Ya Isa!" Alhaji Uzairu ya daka tsawa. "Ba zan saurari wata ƙarya ba! Na ce ku fice daga gidana!"

Babu yadda suka iya. Da kyar suka tattara tarkacensu suna kuka, suka bar gidan kamar waɗanda aka yankewa hukuncin kisa.
....

Muhammad ya tsaya a gefe yana kallon mahaifiyarsa tana barin gidan da tarin nadama. Bai san abin da zai ji ba. Bai san ko zai iya gafarta mata ba. Yana da zafi a zuciyarsa, amma ya san cewa dole ne ya cigaba da rayuwarsa.

"Yaya zaka yi da ita?" Alhaji Amiru ya tambaye shi.

Muhammad ya girgiza kai. "Ba zan iya cewa komai ba. Ita ta jefa kanta cikin wannan bala’in. Ba zan iya yanke hukunci akanta ba, amma gaskiya ta fito. Dole ne ta fuskanci sakamakon muguntarta."

Sai ya juya ya bar falon, zuciyarsa cike da tunani.

..

Bayan fitarsu, falon ya dauki shiru. Alhaji Uzairu ya zauna, yana dafe kansa da tafukan hannunsa. A yanzu, komai ya bayyana. An tona asirin mugunta, amma har yanzu yana jin nauyin zuciya.

"Shekaru da dama..." ya furta a hankali. "Shekaru da dama ina tunanin Zaytunah ce ta rabu da ni, ashe ni aka yaudara?"

Gwaggo Zainabu ta girgiza kai cikin tausayi. "Hakika kun shiga jarabawa, Uzairu. Amma yanzu dai komai ya fito fili. Kuma ina fata ka gane gaskiya."

"Gaskiya ta fito," ya ce cikin wata irin murya mai cike da rauni. "Amma me zan yi da rayuwata yanzu?"

Sai ya lumshe ido, zuciyarsa cike da nadama.

..

A yanzu, Alhaji Uzairu ya san cewa dole ne ya nemi Zaytunah. Amma ina za a ganta? Shin za ta yafe masa bayan duk abin da ya faru? Ya san cewa komai ba zai dawo da sauƙi ba.

Alhaji Amiru ya dube shi, ya ce: "Abin da ya rage gare ka shi ne ka nemi ‘ya’yanka. Ka nemi Zaytunah, ka nemi gafara."

Uzairu ya ɗaga kai ya kalle shi, yana jin kamar duniya ta sauya. Bai san da wane ido zai kalli ‘ya’yansa ba. Duk da haka, ya san dole ne ya nemi su.

A can nesa, wata rana, wata sabuwar rayuwa za ta fara. Amma yanzu, ya rage ga Uzairu da yadda zai fuskanci abin da ya shuka...

Muhammad ya girgiza kai lokacin daya Kalli wajen ta faifon bidiyon da yake gani yaja dogon tsaki yana mai sake furzar da iska mai nauyi daga bakinsa.. ya cigaba da kalla.. yana saurara,

Kwana biyu bayan abin da ya faru, Alhaji Uzairu ya kasa samun sukuni. Yana jin tamkar rayuwarsa ta faɗa cikin duhu. Zaytunah ce macen da ya fi so, amma saboda sharrin matansa ya zarge ta, ya bar ta..

Bayan duk wannan shekarun, yanzu ya san gaskiya. Amma ya rasa yadda zai fara. Ya zauna a cikin falonsa, yana duban hoton da ya rage masa daga aurensu—hoton da ke nuna Zaytunah tana murmushi da Nabeeha ƙarama a bayanta.

Ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi. "Dole ne in nemi Zaytunah," ya furta a fili. "Ko da kuwa ba za ta yafe mini ba, dole ne in roƙe ta gafara."

Da farko, Alhaji Uzairu ya ziyarci Alhaji Amiru. Sun zauna cikin falonsa mai girma, Uzairu yana fuskantar ɗan’uwansa da tsantsar nadama a idanunsa.

"Na tafka kuskure, Yaya Amiru," ya furta da wata irin murya mai rauni. "Na tafka babban kuskure da ba zan iya gafarta wa kaina ba. Amma dole ne in nemi Zaytunah. Ko da kuwa ba za ta yafe mini ba, zan roƙe ta gafara."

Alhaji Amiru ya jinjina kai. "Hakika kayi babban kuskure, Uzairu. Amma ba kai kaɗai ba, ni ma ina da laifi. Lokacin da Zaytunah ta ɓace, na yi tunanin cewa kawai ta tafi ne, ba tare da neman zurfafa bincike ba. Bai kamata na bar lamarin haka ba."

"Kana tunanin za ta karɓe ni?" Uzairu ya tambaya, idonsa cike da damuwa.

"Ba zan iya cewa komai ba," Amiru ya amsa. "Amma abu ɗaya da na sani shi ne, dole ka nemi ta. Idan ka samu gafararta, hakan zai fi maka kwanciyar hankali fiye da komai."

GANAWA DA MAJOR GENERAL DAWUD

Bayan tattaunawa da Alhaji Amiru, Uzairu ya yanke shawarar cewa dole ne ya je wajen Major General Dawud, don kuwa shi ne mutumin da zai iya taimaka masa ya san inda Zaytunah take.

Ya isa gidan Major General Dawud cikin matsanancin damuwa. Bayan an sanar da shi zuwan Alhaji Uzairu, Major General Dawud ya amince da ganinsa.

A cikin babban falon da ya kasance mai cike da ƙamshi da ɗaukar hankali, Uzairu ya zauna yana jiran fitowar Major General Dawud. Cikin ‘yan mintuna, Dawud ya fito sanye da farin riga da wando na shan iska, yana daure fuska kamar yadda ya saba.

"Ina wuni, Major General," Uzairu ya furta cikin ladabi.

"Lafiya lau," Dawud ya amsa, yana kallonsa da idanu masu cike da tambaya. "Meye ya kawo ka?"

Uzairu ya yi ajiyar zuciya, ya sunkuyar da kansa. "Na zo ne domin neman gafara. Ba daga gare ka ba, amma daga gare ta. Dole ne in ganta, in roƙe ta gafara. Ko da ba za ta yafe mini ba, in nemi ‘ya’yana."

Major General Dawud bai ce komai ba na wani lokaci. Sai daga baya ya numfasa, ya gyara zamansa.

"Zaytunah ta shafe shekaru da dama cikin damuwa. Baka san irin wahalar da ta sha ba. Kawai kana so ka je ka roƙe ta gafara, sai komai ya wuce?"

Uzairu ya girgiza kai. "Ba haka nake nufi ba. Ina jin nauyin abin da ya faru. Ina son in nemi su, in roƙe su gafara, kuma in mayar da ‘ya’yana gare ni."

Major General Dawud ya yi shiru, yana nazari. Bayan wasu mintuna, ya ɗaga kai ya ce:

"Idan har da gaske kake, to dole ka jira. Na fahimci cewa kai ma baka san cewa ana cutar da Zaytunah ba. Amma hakan ba yana nufin cewa komai zai dawo kamar da ba. Zan fara tattaunawa da ita. Idan ta amince da ganinka, sai in sanar da kai."

Uzairu ya ɗaga kai, zuciyarsa tana cike da begen samun dama. "Nagode. Ko da kuwa ba za ta yafe mini ba, zan gode idan na ganta."

A cikin kwanakin da suka biyo baya, Major General Dawud ya tattauna da Hajiya Zaytunah game da bukatar Alhaji Uzairu na ganinta. A farko, ta yi shiru na dogon lokaci, tana nazarin abinda ya dace.

"Bayan shekaru da dama, yanzu ne yake tunanin ganina?" Ta furta a hankali.

Dawud ya kalle ta da kulawa. "Na san cewa ba abu ne mai sauƙi ba. Amma ina ganin yana cikin nadama. Yana son ‘ya’yansa, kuma yana son ya nemi gafararki."

Zaytunah ta jinjina kai, zuciyarta cike da tunani.

Bayan dogon tunani, ta ɗaga kai. "To, zan gan shi. Amma ba don in karɓe shi ba. Zan ji abin da zai ce."

Ranar da aka shirya ganawar, Alhaji Uzairu ya kasance cikin rawar jiki. Yana fargabar yadda za a karɓe shi, amma ya san cewa dole ne ya fuskanci sakamakon abin da ya aikata.

A lokacin da ya shiga falon da aka tanada don ganawar, zuciyarsa ta kusan bugawa da sauri. Ganin Zaytunah a zaune a gefen kujera, tana kallonsa da idanu masu cike da kamewa, ya ji tamkar an caka masa wuka a zuciya.

Ya durƙusa a gabanta, idonsa cike da hawaye.

"Zaytunah, na tafka babban kuskure. Na tafka laifi da ba zan iya gafarta wa kaina ba. Na yarda da ƙarya, na bar ku cikin wahala, Banyi kokari ba wajen fahimtar gaskiya. Na zo gare ki ba don in roƙi ki ki dawo ba, amma don in roƙi ki gafarta mini. Domin zuciyata ba za ta samu sukuni ba idan baki yafe mini ba."

Zaytunah ta dubi shi, idonta cike da nauyin tunani. Tana iya ganin nadama a fuskarsa. Tana iya jin ƙaryar da aka yi masa, amma hakan ba yana nufin cewa komai zai dawo da sauƙi ba.

Ta sauke ajiyar zuciya. "Uzairu, zan iya yafe maka, amma ba zan iya mantawa da abin da ya faru ba. Rayuwata ta lalace saboda laifin da baka sani ba. Amma ba zan hana ka ganin ‘ya’yanka ba."

Uzairu ya ji kamar zuciyarsa ta tsinke da farin ciki. "Nagode! Wallahi nagode! Ko da ba za ki dawo gare ni ba, hakan ya isa mini."

A wannan rana, duk da cewa ba a mayar da komai kamar da ba, an yi mataki na farko zuwa ga zaman lafiya. An share gaban baya, an bar gaba a hannu Allah. Kuma a yanzu, duk wanda ya aikata laifi, yana fuskantar sakamakonsa.

Kamar yadda kowa ya ce… akwai sauran rina a kaba.

Bayan ganawar su, zuciyar Zaytunah ta cika da ruɗani. A tsawon shekarun da suka gabata, ta koya yadda za ta rayu ba tare da Uzairu ba. Ta saba da kasancewa uwa guda ga Nabeeha da Hammad. Amma yanzu, ga shi ya dawo, yana roƙon gafara.

A daren ranar, tana zaune a ɗakin ta, idonta yana kallo amma ba ta ganin komai. Tunaninta ya tafi can baya, lokacin da take matar Uzairu, da irin son da yake mata kafin a raba su. Tana tunanin yadda rayuwarta ta canza bayan fitarta daga gidansa.

Major General Dawud ya shigo, ya zauna kusa da ita. "Zaytunah," ya kira sunanta a hankali.

Ta ɗaga kai, tana kallonsa da idanun da suka bayyana gajiyarta.

"Ba zan ce ki yafe masa ba," ya ce da natsuwa. "Ba zan ce ki manta da abin da ya faru ba. Amma ina so ki yi tunani akan kanki. Shin har abada za ki riƙe wannan zafin a zuciyarki?"

Zaytunah ta numfasa. "Ban sani ba," ta furta a hankali. "Ban san ko zan iya ba."

"To ki bari lokaci ya nuna," ya ce mata. "Amma kada ki ƙi yarda da zuciyarki. Idan har za ki samu sauƙin zuciya da yafiya, to ki yi. Idan kuma ba za ki iya ba, babu wanda zai matsa miki."

Zaytunah ta jinjina kai, tana nazari.

Bayan ganawarsa da Zaytunah, Uzairu ya koma gidansa, amma ba ya jin daɗin zama a can. Gidan ya yi shiru, ba matansa, ba ‘ya’yansa. Komai ya sauya.

Ranar da ta biyo baya, ya zauna cikin falonsa, yana kallon sararin sama daga tagar da ke gefen ɗakin. Rayuwarsa ta canza gaba ɗaya. Duk abin da ya gina ya rushe.

Bai san da wane ido zai kalli Nabeeha da Hammad ba. Bai san ko za su karɓe shi ba.

Alhaji Amiru ya zo masa ziyarar dare, suka zauna tare a babban falo.

"Ya kake ji?" Amiru ya tambaye shi.

Uzairu ya yi dariyar takaici. "Ina jin tamkar mutum da aka cire masa zuciya."

Amiru ya ɗan saki ajiyar zuciya. "Uzairu, an ce komai yana da dalili. Wataƙila haka Allah ya tsara. Amma yanzu da ka san gaskiya, mene ne matakin da za ka ɗauka?"

Uzairu ya lumshe ido. "Zan jira. Zan jira har sai lokacin da suka shirya. Ina fatan wata rana ‘ya’yana za su yarda da ni."

Amiru ya jinjina kai. "Hakan shine mafi alheri."

A bangaren Nabeeha da Hammad, su ma sun

27 / 40