DR SADEEQ COMPLETE HAUSA NOVELS BY NARNAH KANWAR SOJA.txt

Author :  Nana Kanwar Soja Category :  Hausa Read

Chapter   36 / 48

105K to 108K   out of 141.3K words

ta damƙe hannunta cikin rawar murna ta ce:


“Indo! Zan koma BOARDING SCHOOL! THE REGENT SECONDARY SCHOOL — BOARDING FOR GIRLS ONLY! Daddy ne ya kawo shawara. Yanzu haka za a fara min registration. Na samu transfer! Kinga yanzu ina SS1 ke nan!”


Indo ta tsaya cak. Kallon idanunta ya canza, zuciyarta ta matse kamar za ta fashe tace da murya mai rauni:


“Ilham shine kike murna? zaki barni? Don Allah kar kitafi… Kar ki barni ne kadai kece kawata, ke ce mai bani shawara… ke ce yar uwata. Ilham please… don Allah kar ki tafi ki barni.”


Kallon Ilham ya canza nan take. Murnar da take yi ta tsaya, ta rungume Indo sosai tana shafa bayanta.


“No Indo… ban shirya rabuwa dake ba wallahi. Amma saurari bayani na.”Ta zaro wani form daga jakkarta, ta ce:


“Gashi nan Form nawa. Amma yana da biya biyu. Daya na registration ne Ki kaiwa Brother Sadeeq… ki ce ke kike so ku koma school ɗaya da ni boarding.”


Indo ta sake girgiza kai tana kuka kadan:


“Ni? Ni na koma boarding?”


Ilham ta share mata hawaye ta ce:


“Eh Indo. Rayuwar boarding za ta gyara mana komai. Zamu tashi tare, mu kwanta tare, mu yi karatu tare, mu yi rayuwar mu tare. Ba zan tafi in bar ki cikin damuwa, cikin tunani… ba zan taba yi miki hakan ba.”


Ta kamo hannun Indo sosai kamar kada ta zame.


“Karki ce zamu rabu. Zamu tafi mu biyu. Ni da ke. Zan gaya wa Daddy na, zai kawo maki ɗayan form naki Ina so ki tafi da wanan nawa guda ɗaya”


Indo ta kalli Ilham, zuciyarta na rawa cikin tsantsar dadi da tsoron rabuwa“Ilham… kina nufin… ba za ki barni ba?”


Ilham ta yi dariya ta ce:


“In bar keke Indo? Haba kawata! Ni ba zan iya ba. Ina haduwa da wani mutum kamar ke a makaranta sau biyu?”suka yi dariya kadan, suna harar juna da soyayya ta kawance.
Ilham ta kara cewa


“Yanzu ki shirya kawai… mu tafi REGENT tare. Ke da ni. Boarding life za ta gyara mana komai, ki gani.”
Indo ta lumshe ido, zuciyarta cike da natsuwa ta ce:“Na amince Ilham… Indai tare zamu tafi.”


Ilham ta kwashe da dariya ta rungume ta:
“Yesss! Yi murmushi mana Indo… kawai mu tafi mu canza rayuwar mu!”




Indo ta runtse ido tana murza yatsunta a hankali, kamar wadda take boye tsoro a zuciya. Sai ta ce da Ilham cikin siririyar murya:


“Amma Ilham… ina tsoro. Ina tsoron Dr Sadeeq ya ce bai yarda ba. Shi yanzu ma fa jin ni yake tsana… ni ma banason ganin shi. Amma wallahi nafison na bar wannan gidan yanzu… na bar duk tunanin da yake damuna.”


Ilham ta kama hannunta sosai, ta matsa kusa da ita ta ce da kyau:


“Indo, listen to me… wannan ba matsala bace. Na san how to handle him.”Indo ta zaro ido:


“Yaya? Ni fa tsoron shi nake ji yanzu Ilham…”
Ilham ta yi murmushin dabara na ƙawaye masu wayo “To ki saurara ki ji yadda za ki samu Dr Sadeeq ya amince cikin sauki.”


Ta girgiza yatsa kamar malama, ta fara lissafi
Ilham ta ce“Dr daya ganeki kina roƙo, zai ɗauka kina shiririta ko kina gudunsa. Ki canza strategy.”. Ki rubuta masa short message mai taushi — ba dogo ba.Ilham ta ɗaga gira:


“Ki rubuta masa kamar haka:
“Ina so in koma boarding don karatu saboda na gaji da wannan tunanin da nake yi kullum. Karatu ya fara min wuya. Please, ka taimaka min don Allah.”


“Kada ki yi kuka. Kada ki zarge shi. Kada ki kawo komai. Ki barshi ya ji laifi kansa — wallahi zai amince!” Kada ki tura masa yanzu. Ki jira ya dawo gida “Dr idan yana gajiya… yana sauƙin yarda ki jira dare ko bayan sallar isha’i, lokacin da zuciyarsa ke sanyi.”Ilham ta yi dariya:


“Indo, lokacin da kika guje masa sai zuciyar namiji ya fara faduwa — yana tunanin yaya za ki guje shi? Nan ne yake saurin yarda da duk abinda kike so.”. Ki bari ni in fara masa magana sosai da Daddy na — mu hada masa pressure mai kyau.


“Daddy na yana da suna sosai kuma Kinga munmaƙobta ne duk matsallaci daya suke sallah Idan ya kira shi ya ce ‘yarinyar nan tana da kyau da karatu, ta dace da Regent’ wallahi Dr ba zai yi musu ba.”
Indo ta ji sanyi sosai, ta dafe kirjinta tana kallon ƙawarta.


“Ilham… kina nufin idan na bi wannan plan ɗin… zai yarda?”


Ilham ta dungura hancinta:


“I promise you Indo. He will. Kuma wallahi wannan boarding zai ma taimakeki ki rage damuwa, ki huta da wahalar su Mommy kullum. Ki koma inda zuciyarki zata huta.”


Indo ta nisa sosai, idanunta suka cika da kwanciyar hankali:


“Nagode Ilham… da gaske. Ni dai ina son in tafi.”Ilham ta rungume ta:


“To shikenan kawata. Da dare ki tura masa message ɗin. Let’s start your new life.”




Indo ta jingina da katangar gadonta, wayar hannunta tana rawa, zuciyarta bugawa kamar ana kirga mintuna. Dare yayi shiru, hasken lamp ɗinta kaɗai ke haskawa. Ta sha numfashi sau uku kafin ta rubuta:


“Dr, don Allah ina so in tafi boarding school. Ina son na mayar da hankalina kan karatu saboda tunanin da yake damuna kullum. Karatu yana min wahala yanzu.
Don Allah ka bani izini. Na gode.”


Da tsoro ta danna SEND.


Tana turawa sai jikinta yayi sanyi, ta rufe fuska da bargo a can part ɗin Dr Sadeeq…


Dr Sadeeq


Yana zaune a ƙarƙashin hasken farin lamp, cikin doguwar rigarsa mai laushi, yana shan coffee mai zafi a cikin kofi ɗin sak el-classic.
Laptop ɗinsa a buɗe — yana rubuta report din Daddy na company.


Sai kawai ya ji tiiiiikk! — sautin message


Ya ɗan kallewa kamar ba shi da niyyar buɗe shi yana ganin sunan “INDO 🌙💙”


Goguwar zuciyarsa ta tsaya na daƙiƙa ɗaya.
Hannu ya ɗan yi sanyi ya latsa message ɗin ya karanta
“BORDING SCHOOL…”


Sai jikinsa ya yi wani irin tsalle, zuciyarsa ta matse kamar an murɗa ta.
Ya ajiye kofin coffee din da sauri har ya buga kujerar.


“Boarding??”
Ya ambata cikin murya mai ƙasala da tashin hankali.


Ya sake karanta message ɗin, idonsa ya ɗan ɓoye zafin da ke tashi a zuciyarsa:


“…na gaji… tunani… karatu yana min wahala…”


Sai ya ji wani abu ya tsinke masa a kirji.
Yayi murmushi mai rauni, ba na farin ciki ba — na nauyi a ransa yana cewa:


“Indo… kina guduna ko? Ke bakya so mu zama kusa ne?”


Ya jingina da kujera, ya rintse idanuwansa yana furta, “Wayyo Indo… bazaki tafemin ba. Ki barni ni kaɗai yanzu?”


Hannu ya kai kan screen, yatsunsa na rawa, ya rubuta a hankali:


“Boarding ko, Indo?
Wayyo, kina nufin baki son zama kusa dani?
Baki son mu zama family ne?
Baki son ki… ki rike zuciyata kusa da taki?”sai kuma ya share — ya goge komai yayi nisa mai nauyi A ƙarshe ya rubuta:


“Indo, kina so ki tafi?
Ko kina so ki yi nisa da ni ne kawai?” ya tura mata


Da zarar ya tura ya jingina da kujerar, zuciyarsa cike da tashin hankali, jin kamar wani abu ya fara zame masa daga hannunsa.


Ya dafa goshinsa:


“Allah ya tsare min ke Indo… amma kar ki barni haka.”
A gefe guda Indo ta ga message ɗin…
Idonta ya ƙara faɗa…
Zuciyarta ta yi wani irin tsayawa…


Sai ta fara tunanin:
“Yanzu ya gane ina gudunsa?”


Cinikin dare ya fara armashi…




..........................................................................




8️⃣2️⃣

8️⃣1️⃣
💔❤️‍🔥DR SADEEQ ❤️‍🔥💔


BY


NARNAH ƘANWAR SOJA


BOOK 2
My 15novel comedy love and drama



https://chat.whatsapp.com/LDm6JQR1M3L5dOPu5dB0TM



THIS BOOK IS DEDICATED TO MY LOVELY BROTHER ABUBAKAR SADEEQ AND MY LOVELY SISTER AISHATU INDO.......




MORNING UPDATE



💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*





🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚


(🦚✊DEDICATION IS OUR STRON ✊🦚) Typing...📲




BUSSINES GROUP


👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/JjkU7xG4zcWIAvtWRgeFtT


BARKA AUNTY INDO MARUBUCIYAR SAWUN KEKE TA SAMU ƘARUWA HAIHUWA ALLAH YA RAYA MANA BABY GIRL AMEEN






TITLE
Love is a flame that burns bright, even in the darkest night
AFTER SOME DAY'S





Indo ta zauna kan gadonta, ta ji zuciyarta kamar an daure ta da ƙyalle. Ta ɗaga wayar a hankali, ta rubuta sako cikin rawar hannu:


“Please I need to go…
I like the school.
Thank you.”


Ta tura ta rufe idanuwanta, tana jin kamar tayi babban abu can Dr Sadeeq kuwa… Da zarar ya ji sautin piiing! sai ya kamo wayarsa da sauri.
Yana buɗewa, ya sauke idonsa kan sakonta.


“Please I need to go…”


Ya sake karanta “I like the school…”


Sai zuciyarsa ta matsu, ta yi wani irin nauyi mai tsanani.


Ya maimaita sakon.
Sau ɗaya… sau biyu har sau goma a jere.


Kamar mai neman wani sirri a kalmomin, ko zai ga kalmar“Don tafi daga gare ka ne.”ko “ka barni.” “Bana son ganin ka.”


Amma babu


Ya jingina da kujerar office ɗinsa, wayar a hannu, idonsa na raguwa cikin kunci da natsuwa da hannu ya shafi kansa a hankali.


“She wants to go…”


Ya ambata da murya mai rauni ya kuma sake kallon sakon na ƙarshe:
“thank you.”


Abinda yafi doke zuciyarsa shine wannan “thank you” ɗinkamar Indo na masa sallama ne har abada.


Sai ya runtse idanu yana jin wani abu ya tokare zuciyarsa, ya ɗaga wayar ya koma messages
Ya duba chat ya sake karanta sakon sau na goma sha ɗaya…
ba tare da ya rubuta komai ba.


Ya kasa rubuta komai


Domin a zuciyarsa kalma biyu ke masa yawo:
“Indo is leaving me…”


Ya jingina da tebur ɗin, ya lumshe ido, murya ta shaƙe cikin zuciyarsa:


“Please Indo… kar ki barni haka" ya kashe wayarsa.
Ya jingina kai, yana barin shiru ya cika dakin.


Darenta ya lalace.
Ranar Indo kuma ta fara sabon tunani.




A ɓANGAREN ILHAM kuwa…


Da ta koma gida, zuciyarta cike da damuwar Indo, ta same Daddynta a falo yana kallon news.
Ta zauna a gefensa, ta ɗan janyo numfashi sannan tace:


“Daddy… akwai magana.” ya kalle ta da murmushin kulawa “What is it my princess?”


Ilham ta fara ba shi labarin Indo — yadda take rayuwa a gidan Kaka, yadda take da ƙwarin hali amma tana da rauni, yadda ta rame saboda damuwa, yadda take muradin boarding domin samun sauyi da natsuwar zuciya.


Ta ƙara da cewa:


“Daddy, please… Indo is my only friend.
Ni kuma bana so a raba mu.
Ka taimaka a karɓa mana form ɗin nata mu tafi tare.”


Daddy ya yi shiru, yana sauraren ta sosai.
Ya jinjina kai a hankali, ya ce:


“Hmm… I understand now.
Kin faɗa min komai, kuma gaskiya yarinyar tana bukatar sauyin muhalli.
Don haka… babu damuwa.”


Idon Ilham ya faɗaɗa cikin murna Daddy ya sake cewa:


“Da safe idan na haɗu da Dr Sadeeq zan yi masa magana.
I’ll handle everything


Ilham ta miƙe da sauri ta rungume shi:


“Thank you Daddy! Wallahi you’re the best!”
ta yi tsalle tana dariya kamar ƴar ƙarama.


A zuciyarta kuwa:


“Indo will be so happy…
Mu biyu – one school, one hostel, one life.”


Kwanciya tayi da murmushin nasara —
ta san gobe Indo ba zata yi kuka ba… zata yi murna.




Suna fitowa daga masallaci da asuba, iska mai sanyi na tafe a hankali, Daddy ya kalla Dr. SADEEQ da murmushi mai tarin nutsuwa.
“Dr. Sadeeq, akwai wata magana da nake son mu yi kafin ka shiga gida"


Dr. SADEEQ ya tsaya, ya ɗan ɗaga gira, saboda Daddy ba ya yawan yin irin wannan maganar sai abin ya da muhimmanci.


Dr. SADEEQ:
“To Alhaji, me ya faru?”Daddy ya ja numfashi
“Indo… ta yi magana. Tana matuƙar son karatu. Kuma ta ce tace maka… ka taimaka mata. Har ta ba Ilham labari gaba ɗaya.”


A nan Dr. SADEEQ ya zaro ido kaɗan cikin mamaki
“Indo ta gaya muku duk haka?”


Daddy ya jinjina kai.


“Eh, ba komai bane ai. Ni dai na ce a karɓo mata form. Ita da Ilham za su tafi tare. Kai ma ka shirya, zan so mu yi maganar sosai game da lamarinta.”


Dr. SADEEQ ya yi shiru na tsawon sakanni biyu, yana kallon gabansa kamar yana nazari. A zuciyarsa ya ce “Ashe Indo ta damu har haka? Ashe tana ɗauka ni ba zan taimaka mata bane?”


Sai ya ɗago kai da murmushin da ba kowa yake gani ba
“Alhaji , wallahi tunda Indo ce… babu wani abu da ba zan yi ba. Zan taimaka mata har inda ƙarfina ya iya kaiwa. Kuma na yi mamaki kawai saboda bata taɓa gayamin haka da kanta ba.”


Daddy ya fashe da dariya mai sanyi
“To ai yaran zamani. Wasu sai sun ji kwarin gwiwa kafin su fadi abin da ke zuciyarsu. Ka tsaya ka ji magana, ba sai an yi hayaniya ba. Ni dai ina goyon bayanka, ina goyon bayan karatunta… ku shirya kawai.”


Dr SADEEQ ya saki wani murmushi mai cike da jin daɗi.


Dr SADEEQ:
“Insha Allah Alhaji . Zan shirya komai yau.”


Suka ci gaba da tafiya gidan, kowannensu cikin tunani—Daddy cikin farin cikin hangen gaba, Dr SADEEQ kuma cikin mamaki, da wani sabon yanayi da bai taba ji ba tun da ya fara sanin Indo.
@@@@@@@@@@@@@@@@






Zuciyar Dr. SADEEQ dai ta ɗauki nauyi sosai. Bayan su Daddy sun yi tafiya gida, ya nemi Kamal a gefe, ya zauna da shi cikin natsuwa:
“Kamal… wallahi ba komai. Alhamdulillah, zata samu sauki yanzu. Ni kuma zan tabbatar na sauke amanar da Allah ya bani. Zan kula da ita yadda ya kamata, har sai ta kai ga abin da ya dace da ita.”


Kamal ya ɗan jinjina kai, ya fahimci irin damuwar Dr. SADEEQ da irin soyayyar da yake ɗauka ga Indo.
“Allah ya taimaka maka, Dr. Sadeeq. Ka san kai ne kadai ke da ikon sauke amanar da Allah ya ba ka. Amma kada ka yi gaggawa, ka ba ta lokaci, kada ka matsa mata… in ba haka ba zata tsananta.”


Dr. SADEEQ ya ɗaga hannunsa ya dan shafa fuska, ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi
“Na sani Kamal… zan yi hankali. Amma zuciyata tana cikin farin ciki, saboda a yanzu na fahimci cewa ba zan bar ta cikin wahala ba. Allah ya sa ni mai adalci gare ta.”


Kamal ya jinjina kai, ya danna kafadarsa cikin goyon baya:
“Yau ka fara aiki mai girma. Ka tuna, hakuri da kulawa za su zama makami mafi ƙarfi.”


Dr. SADEEQ ya zauna a waje kadan, yana tunani, zuciyarsa cike da sabon buri. Wannan lokaci ne da ya fahimci cewa, soyayya da amanar da Allah ya bashi za su haɗu don kare Indo daga duk wani abu da zai cutar da ita.








8️⃣3️⃣





💔❤️‍🔥DR SADEEQ ❤️‍🔥💔


BY


NARNAH ƘANWAR SOJA


BOOK 2
My 15novel comedy love and drama



https://chat.whatsapp.com/LDm6JQR1M3L5dOPu5dB0TM



THIS BOOK IS DEDICATED TO MY LOVELY BROTHER ABUBAKAR SADEEQ AND MY LOVELY SISTER AISHATU INDO.......




MORNING UPDATE



💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*





🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚


(🦚✊DEDICATION IS OUR STRON ✊🦚) Typing...📲




BUSSINES GROUP


👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/JjkU7xG4zcWIAvtWRgeFtT


BARKA AUNTY INDO MARUBUCIYAR SAWUN KEKE TA SAMU ƘARUWA HAIHUWA ALLAH YA RAYA MANA BABY GIRL AMEEN






TITLE
Love is a flame that burns bright, even in the darkest night






Bayan Dr SADEEQ ya gama shirye-shiryen Boarding School na Indo, sai aka shiga lokacin iftar. Gidan ya cika da natsuwa da annashuwa. Kowa ya zauna a dining, ciki har da Indo da Kaka.


Kan tebur an tanadi kayan abinci masu daɗi: ferfeson kaji da kayan lambu, dankalin turawa da miya mai kyau, kayan marmari iri-iri kamar ayaba, abarba, da lemun tsami, da kuma busassun kayan itatuwa da aka shiryawa musamman don Ramadan.


Indo ta zauna a gefen Kaka, tana kallon abincin da aka shirya. A ranta, ta yi murmushi, tana jin dadin yadda gidan ke cike da kulawa da natsuwa, kuma tana godewa Allah da saukin da ta samu.


Kaka kuwa tana murmushi, tana mai cewa:
“Indo, ki yi amfani da wannan lokacin, ki karu da ilimi, ki ci gaba da koyo da natsuwa. Allah ya albarkaci azuminmu.”


Indo ta gyara kujera ta, ta ɗauki cokali, tana fara cin kayan iftar cikin ladabi da natsuwa. Ta ji daɗin kayan abincin, musamman ferfeson kajin da aka yi da kyau, da kayan marmari masu ɗanɗano mai daɗi.


Duk gidan na cikin farin ciki da annashuwa, kowa na gaisuwa da juna, suna jin dadin haɗin kai da natsuwa na watan Ramadan.




Indo tana zaune a gefen Kaka, tana jin dadin abincin iftar. Duk da cewa tana dan jin ciwon ƙasa da safe, yanzu tana jin sauƙi sosai. Ta ɗan ɗaga idanunta, ta ga Kaka tana kallonta cikin kulawa, tana murmushi.


A gefe kuma, Dr SADEEQ yana zaune a gefen tebur, yana lura da duk wanda ke abincin. Idanun sa suna kallon Indo ba kai tsaye ba, amma cikin kulawa, yana tabbatar da cewa tana jin daɗi kuma lafiya. Ba zai so ta san yana kallonta ba, don yana son ganin ta kasance cikin natsuwa da farin ciki.


Indo tana ɗan jin shaukin abinci, ta fara cin ferfeson kajin da aka dafa da kyau, tana ɗan ɗanɗana kayan marmarin da aka kawo a lokaci guda, zuciyarta na cike da tunanin Boarding School da sabon mataki da zata fara. Amma jin dadin gidan da natsuwa ya taimaka mata ta rage damuwa.


Kaka ta lura da yanayin ta, ta ce:
“Indo, ki ci abincin ki lafiya. Ki kara ƙarfin jiki domin Ramadan, Allah zai albarkaci azuminmu.”


Indo ta gyada kai, ta ɗan murmushi, tana jin daɗin kulawar Kaka. Ta ɗan ɗanɗana lemun tsami, sai ta lura da Dr SADEEQ yana kallonta a hankali, idonsa cike da kulawa amma ba tare da ya nuna sosai ba. Wannan abu ya sa zuciyarta ta ɗan narke, amma ta kasa furta komai, tana mai tsoron yayi fushi idan ta yi magana fiye da kima.


A gefe daya, yaran gidan suna ta

36 / 48