Gudun Aure Book 3 Binta Umar Abbale

Author :  Binta Umar Abbale Category :  Read Hausa Novels

Chapter   63 / 73

186K to 189K   out of 217.6K words

ban bi shi ba na yi zamana ina nazarin yadda abubuwa suke canzawaa daga wannan sai wannan zuciyata tana gaya mini kudi ta kar'ba masu kauri a hannunsa domin ta 'karu tunda dama neman hanyar da za ta dinga samun kudi take yi.
Ita kuwa wadda ta rasu tana yi ne da dukiyarta bata neman kwabonsa ita nata salon kenan tunda tana da arziki. Ita kuwa Hauwa na tabbatar da cewa ta yi hakane domin 'karuwarta.
Da yamma muna kicin tare da Hadiza muna shirin abu bude ba'ki suka shigo..
Na bar ta a kicin din goye da Hassan ya yi bacci na fito falon na same su a zaune Inna Uwani ta d'auki Usaini yana saman cinyarta da abin wasansa a hannu.
Na d'an saki fuskata ina yi musu barka da zuwa na zauna kujerar dake kallonsu yaran gabad'ayansu suka shigo Khalil twins da Minal wurina suka rugo a guje k'ananun shi kuma Khalil din yana ta dariya kafin ya d'an risina yana fad'in." Mama ina yini?"
Na amsa da kulawa ni ma ina dariya na ce." Kai ya na ga duk ka yi zuru-zuru azimin nan fa bai wajaba a kan ka ba."
Ya sa dariya yana fad'in." Ko bai wajaba a kaina ba ba zan asha ko daya ba Mama.
Minal tana ta'ba mini cinyata ta ce." Mama ni kin ga haka na yi." Ta had'a yatsunta biyar ta d'ora d'aya a kai."
Na bude baki cikin mamaki ina fad'in." Da gaske." Karaf Usai ta buge hannun tana cewa." Ma'karyaciya ko daya ba ta yi ba wallahi." Cikin wasa ta yi maganar don har tana dariya ma.
Abinka da yarinta ita kuma Minal din sai ta fashe da kuka tunda dama dangwalolo ce. Nan da nan Hauwa ta 'bata fuskarta na ji lokacin da ta ja tsaki mai tsayi.
Ina Uwani na fad'in." Ke kam Usaina kin fiye saurin hannu wallahi menene abin duka Kuma?"
Khalil da sauri ya ce." Ba dukanta ta yi ba fa Inna."
Hauwa ta harareshi tana fad'in." Ba mu da ido ko kaine kake da Ido don ubanka zaman da suka yi a can ma kenan ba dukanta take yi ba."
Ya yi shiru yana yin fuskarsa ya canza.
Na ce." Ai saurin hannu gare ta na gaya mata kuma 'kanwarta ce."
A d'an sanyaye ta ce." Ban doke ki ba ko Minal?"
Sai ta d'aga kanta. Tsakanin yara ba a shiga Usai din ta sanya hannu tana goge mata fuska.
Daga haka na ce." Ku je dakinku ku zauna kafin mu gama gaisawa..
Suka kama hannunta suka bar wajan.
Cikin kulawa na fara gaishe da Inna Uwani itama ta amsa a d'an sake ta yi mini ta'aziyya tare da jajanta mini rashin da aka yi. Haka itama Hauwan mun gaisa babu yabo babu fallasa ta yi mini gaisuwa kafin ta dubi Khalil tana d'an harararsa ta furta." Ba ni ledar kayan nan?"
Na dube shi da sauri wata babbar leda ce da ya shigo da ita sai ya ajiyeta gefan kujera. Ya d'auka ya mika mata ta kar'ba kafin ta kalle ni tana fad'in." Babansu ne ya bada kudi aka saya musu 'yan kanti wurin Sadiya wannan shekaran ta kawo kaya sosai ai baki mance ta ba ko?"


Na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biyani hakkina ba

Na gyada kaina a nutse ina fad'in." Ban mance ta ba." Sai ta mi'ko mini tana ce wa." Na ga sun yi kyau sosai set takwas ne kowanesu hud'u."
Na kar'ba na ajiye a gefena ina fad'in." To madallah."
Suka amsa tare kafin ta cigaba da cewa." Takalma ne kawai babu sizi d'insu a wurinta shine ban ce ta aiko ba amma gabad'aya yaran an saya musu da mayafai sauran suna wurin telansu yadda ya ce cikin satin nan zai kawo."
Na ce." To shikkenan wannan na Hasan da Usaini ne kenan?" Ta gyad'a kanta na ce." Ina na su Hassana?" Sai ta d'an diririce kafin ta ce." Yana can gida zan aiko miki da su gobe ko kuma an jima da daddare.
Shiru na yi ban ce komai ba. Hadiza ta fito daga kicin da yaron a bayanta cike da walwala a fuskarta ta zauna suna gaisawa. Inna Uwani ta yi caraf ta ce." Wannan kamar 'yar uwar nan taki ko?"
Na ce." E, itace Hadiza ba?" Sai ta ri'ke bakinta tana fad'in." Itace ta lalace haka sai ka ce wadda take d'auke da siga ko kanjamau!"
Maganar ta dake ni sosai cikin fad'uwar gaba na kalleta bakina sai ya yi nauyi na kasa ce mata komai.
Hadiza cikin gaggawa ta tashi ta bar wajan domin itama da alama maganar da Inna Uwanin ta yi akanta ba ta yi mata dad'i ba.
K'asa na yi da kaina zuciyata na hantsilewa akwai dalilan da suka sanya nake d'agawa matar nan 'kafa ba wai don tana uwar kishiyata ba ina kallonta kamar Hajja tunda ciki daya suke amma an kusa kaiwa matakin da zan fara mayar mata da raddi a duk lokacin da ta yi mini wani rashin hankalin.
Ya sauko ya same mu a zaune a falon ya zauna gefana yana kallon Inna Uwani da ta k'irkiri yi wa Usaini wasa har da yi masa rawa tana dariya shima yaron yana yi. Hakan kuwa ya yi masa dad'i sosai aka ce wai mai d'a wawa sai ya shiga washe bakinsa tana fadin." Yara duk sun yi wayo kamar ba biyu ba sun yi kyau uwarsu na da kafar nono mai kyau."
Ya ce." Haka aka yi goyon 'yan uwansu ma." Ta miko mini yaron tana fad'in." Ai ban mance ba. Ubangiji Allah Ya raya mana su domin su zama cikon addinin musulunci duniya kuma ta amfana da su."
Ya dinga amsawa da Amin ya rabbi Inna Uwani Ina godiya sosai."
Suka tashi tafiya bakina ya mutu kwarai dangane da salon da suka shigo da shi. Da k'yar na ce su gaida gida ya tashi ya bi bayansu kafadarsa sa'be da yaron.
Ina nan zaune ya dawo ya zauna cikin walwala a ganinsa mun fahimci juna tunda gashi har ya sakko ya gan mu kuma yaronsa na hannu Inna Uwani tana yi masa wasa wannan ne dalilin da ya assasa masa annasuwa da farinciki bai san da cewa wani sabon salo ba ne.
Na zazzage kayan yaran ina dubawa. Eh rigunan manya ne kuma sun yi kyau sosai zan iya kar'ba na yi musu amfani da shi tunda an riga an saya na su Hassana ne ban ga ni ba. Na juya ina tambayarsa "Ta kawo mini kayan su Hassan ban ga na su Hassana ba?"
Ya dube ni da kulawa yana fad'in." A a ba ta had'o da su ba ne?"
Na ce." Eh" Sai ya dan yi jim kafin ya nutsu yana kallona ya furta." Ki bar mata su su yi sallah a hannunta idan hutun makaranta ya 'kare sai su dawo gabad'aya jiya ta fara gaya mini cewa tana son yaran su yi mata hutu.''
Girgiza kaina na yi tare da cewa." A a, yaranta dai ka kai mata su amma nawa yaran su dawo gidansu ba ni son abinda zai daga mini hankali a yanzu dai cikin ibada muke abinda ba zai yiwu ba ne.''
Ya d'an 'bata rai yana fad'in." Ke dai duk ta inda aka biyo miki ba a yi miki gwaninta Amina menene lefin nan da can kuma duk gidana ne akwai buk'atar a ko'ina yarana su sake su kuma yi sabo, ki yi hakuri ki bar mata su hutu kawai ta buk'aci da su yi a hannunta sai su dawo, ki duba kawaicin da ta yi miki a kan nata yaran mana."
Na sake girgiza kaina a karo na biyu na furta." Na gaya maka fa ba zai yiwu ba ai ni ban buk'aci zaman yaranta ala dole a tare da ni ba. Kai ka kawo mini su kuma ba zan hana su zama ba tunda gidan ubansu ne. Maslaha anan shine ka kwashi yaranta a kai mata tunda zahiri ana shiga hakkinta alamu sun nuna kad'aici ya isheta hayaniyar yara take buk'ata. Kowa ya rike nasa shine zance na gaskiya."
"Kamar yadda na isa na bata umarni ta bi ke ma haka za ki bi. Na gama yanke magana yara za su yi hutu gidan Hauwa idan sun 'kare su dawo ku cigaba da zama gabad'aya tuntuni yaranta dake suka saba kuma suna kaunarki babu wani dalili da zai sanya ni raba su dake saboda suna sonki itama ta yarda da hakan."
Yana gama fad'in haka ya d'ora mini yaron saman cinyata ya kama hanyar samansa yana magana." Idan Hakan bai yi miki ba ni ma sai ki raba ni biyu ki d'auki b'angaran da kike so a jikina sai ki bata rabin tunda duk a kaina kuke wannan 'kiyayyar junan idan na mutu kowa zai huta ai."
Na dinga kallonsa har sai da ya gama hawa steps na daina hangensa na dawo da kallona kan yaron da yake ta zura hannunsa cikin rigata nono yake nema. Babu kuwa halin ba shi domin tunda suka fara wayo nake had'a musu kamu irin wanda Sultan ya sha yana kan matakinsu balle yanzu da ake yin azimi ba ni yarda su tsotse ni da tsotsan jaraba.
Bai sauko ba sai daf da za a sha ruwa mun gama aiki Hadiza na gyara kicin din muka dinga jin kuka a falon na fito da saurin gaske. wanda ya yi daidai da saukowarsa Minal ke kuka tare da Sultan Hauwa ta turo mai aikinta Ladidi wai su tafi tare. Sauran sun yi cirko-cirko. Kuka fa sosai Minal ta ri'ke hannunsa tana fad'in." Baba ba kaine ka ce mu zauna a can ba sai Mama ta dawo, to ina za mu je ai nan ne gidanmu Ladidi za ta d'auke mu."
Sultan da tafiyarsa ta yi k'wari sosai ya taho da d'an gudu ya rige gefan rigar uban yana kuka ya sunkuya ya d'auke shi yana kallon Khalil ya ce." Je ka dauro alwala lokacin sallah ya yi." Yaron ya juya da sauri ya bar wajan.
Sai ya dubi Ladidin yana fad'in." Je ki abin ki idan an jima zan shigo da yaran."
Ta risina da sauri kafin ta juya ta kama hanyar fita.
Khalil ya fito da alwala sai ya dire Sultan din a kasa ya ce." Ri'ke hannunsa muje massalacin tare."
Ya yi gaba da sauri su kuma suka bi bayansa..
Na dube su Usaina ta ri'ke hannun Minal din tana zaune dirshen 'kasan ties amma kukan ya tsagaita. Na ce." Ya isa haka ta shi kuje ku yi alwala a yi sallah sai a ci abinci ko?'
Ta daga mini kai tana sakin ajiyar zuciya ta tashi 'yan uwan suka tasa 'keyarta zuwa dakinsu.
Daga ni har ita Hadizan cikin damuwa muke amma ni na yi kokarin ganin na kawar da tawa damuwar domin samar mata da kwanciyar hankali. Ba wani abu ba ne yake nukurkusarta face maganganun da Inna Uwani ta gaya mata d'azu. Bud'e baki ma da 'kyar ta iya saboda damuwa. Babu komai ai rayuwace duk wanda ya yi wa kaddarar wani dariya watarana Ubangiji shima zai jarrabe shi da abinda zai zama abin nuni da zind'e a idanun jama'a. A fakaice na d'an dinga jan hankalinta da wayo da rarrashi ta ci abinci tana ta nuku-nuku da hawayen dake ma'kale a kwarmin idonta.
Tunda yau ma din a gidanta zai kwana ban tsammaci sake dawowarsa ba mussaman tunda ga irin rabuwar da muka yi wajan goma da ashirin muna falo muna kallo gabad'aya har da yaran ba su kwanta ba. Ya shigo ri'ke da hannun Sultan yana ta sauke ajiyar zuciya yaro idonsa ya yi jawur da kumburi almar ya ci kuka ya k'oshi. Khalil dake biye a bayansu Fadi." Yake yi ga ta can Usai din je ka."
Ya kuwa tafi wajenta da sauri yana sauke numfashi. Na dubi Khalil din ina fad'in." Me ya same shi?"
'yar dariya ya yi kafin ya ce." Wai ba zai kwana a can ba shine yake ta ihu yana kiran Usaina."
Abin ya ba ni dariya da tausayi. Na d'an janyo hannunsa ya taso ya tsaya kusa da ni tare da dora hannunsa saman cinyata na ce." Anan kai ma zaka kwana ko Sultan?"
Ya d'aga kansa. Na furta." Ashe kwanciyar dole kuke yi a can din ko Khalil?''
Shiru ya yi bai ce komai ba sai ma ya yi k'asa da kansa.
Hadiza ta mike tana fad'in." Bari a gyara musu shimfid'a." Ta nufi d'akin nasu da sauri.
Na ce su tashi su bita su canza kaya sannan duk su yi alwala kafin su kwanta.
Duk abinda ake yi yana tsaye yana kallonmu bakinsa ya mutu da alama ya rasa abinda zai ce. Bayan shigowarsu na dubi Khalil Ina fad'in" D'auko Usaini ka biyo ni dashi d'aki." Dama Hasan yana ri'ke a hannuna na tashi da shi a kafa'data kai tsaye bedroom dina na nufa ba tare da na sake kallon wajan da yake tsaye ba, a haka yara za su yi hutu a wajanta na kwanaki suna yi kamar za su mutu saboda kuka ashe da babu kowa a gidan ha'kuri kawai suka yi suka zauna tunda yanzu na dawo kuma sun nuna mata basu san wata ba bayan ni. Da nata da nawan gabad'aya don ni sai nake ganin twins ma sai su zauna a hannunta ba tare da koke-koke ba nata ba su zauna ba Minal dai da Sultan sun tsaneta wallahi abin har mamaki yake ba ni. Ita Minal yadda take bala'in sona shine abinda yake sanya mini sanyin jiki shi kansa Uban na lura da yadda jikinsa ya mutu abin ya fi karfinsa Hauwa ta haifar mini yara Allah mai iko......✍️
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK*
*V-VIP AREWAPEN*
*07084653262*
*169*
To ban san abinda ya kasance a tsakaninsu ba washe gari dai da misalin sha d'aya da wani abun Ladidi mai aikinta ta kawo musu kayansu kaf na can wanda suka yi amfani da shi bayan tafiyata kano da kayan sallar tasu da suke a hannunta pants takalmansu da kayan kitso abin wuya da hannu kowanne da na shi da alama duk ta had'a ta yi order din wurin Sadiyar gabad'aya girkina ne a ranar bai shigo ba sai bayan magriba tukkuna ya buk'aci abin bud'e baki na hada masa babu wata sakewa don sai nake ganin kamar akwai abinda ya boye mini. Kunun tsamiya muka yi da k'osai yadda ya kusa shanye dogon jug hakan ya tabbatar mini da cewa kunun ya yi masa dad'i k'osan ma ya ci fiye da biyar saboda sakin manya muka yi. Ya sha zo'bon dana had'a daidai gwargwado ya kammala yana godiya ga Allah kafin ya dawo da hankalinsa gare ni
Na yi shiru ina sauraransa." Akan maganar da muka yi dake kwanakin baya kin ce kina buk'atar a musanya miki wannan kamfanin ko?"
Na gyad'a kaina a nutse na furta." E, idan zai yiwu ba wai na raina kyautar ba ne kawai dai na fi gane business din da nake yi ina ganin idan na sake samun wani reshen anan za a samu alheri."
Ya ce." Shine dalilin da ya sanya ai na sake tambayarki tuntuni nake ta shawara a kan hakan kyautar za ta koma kan Hauwa tunda ni ba ni so a tashi kamfanin ko babu komai kadara ce mai girma da ta kafu tunda a 'kalla da kafa kamfanin zuwa yanzu ya haura shekara goma sha shida duk yanzu muna kan aikin fad'ad'a waninsa ammana akwai buk'atar shi d'in a cigaba da aiki da shi. Na mallakawa Hauwa shi ke kuma akwai tallan wasu tsoffin shaguna da aka yi mini cikin kasuwar wuse din idan mun kammala da masu shi zan sanya ma'aikata su rushe tare da sabunta shi zuwa plaza din kamar yadda ki ka buk'ata a k'alla dai za a iya samun shaguna sha biyu 'kasa shida sama shida a hankali idan Ubangiji Allah Ya sanyawa abin albarka sai ki yi wadda ta fi wannan din ko?''
Na ce." Hakane na gode sosai Allah Ya saka da alhari ya kara arziki ya kuma jikan iyaye."
Ya dinga amsa cike da jin dadi yana jifana da wani irin kallo wanda na gama fahimtar ko na menene.
A daran kam na kar'be shi sosai kuma na yi kokarin ganin na yi masa bajinta wajan ganin na bashi farinciki yanayin yadda na tallafe shi ya k'ara dilmayar dashi cikin yanayi na shau'ki da sambatu irin wanda ba a tonawa wannan lamarin ai ba zai fasu ba idan da rai da lafiya a jikin gangar jiki.
Kwanaki biyu bayan wannan su Baba Tabawa suka dawo murna a wurin yara ba a cewa komai tsalle mussaman Sultan ya rirriketa tana dariya itama ta rungumeshi bakinta kamar gonar audiga gabad'aya sun canza da wata iriyar nutsuwa alamu ibadar da suka gudanar ta samu karb'uwa a wurin Ubangiji domin fes suka dawo da wani annuri na mussaman a tattare da su.
Dawowarsu ta sake bud'e wani sabon babi na farinciki a gidan ya kasance koyaushe cikin wasa da dariya da juna mussaman da bikin sallar ya gabato Mairo ta tsefewa yara kitso an wanke tas Taburni itace makitsiya Lad'ifa mai lalle saura kwana uku sallah ta zo ta yini tana yi wa yara washe gari ta dawo ta yi mini tare da Hadiza aikuwa tasha kudi wurin maigidan mussaman da ya ga na yaran ja da ba'ki ya fito sosai ya dinga duba kafafun nasu yana murmushi ta had'a kayanta ta tafi cike da farinciki dubu dari biyu kudin lalle kawai duk da Hajiya Maryam ta saba yi mata kyauta amma wannan ta yi mata bazata domin duk zuwan da take yi mini lallen ni nake sallamarta yau sai ga shi rabonta a ya rantse, ta samu kudi da turaruka da sabulai na hada mata da gyale mai kyau.
A daran mai dinkinsu ya aiko da shi kowanne k'alla gudu leces biyu a tamfa daya sai shadda daya wadda ta ci uban aiki abin mamaki har da na masu aiki set biyu Hadiza kuma aka yi mata uku manyan atamfofi. Sai na 'kara mata da lece daga cikin kayana dake d'inke wanda ban sanya ba. Takalmi na bata set biyu masu tsayin dunduniya duk sabbi da abin wuya da hannu.
gaskiya babu lefi ya yi kara ya kuma nuna halin dattako domin

63 / 73