Author : Binta Umar Abbale Category : Read Hausa Novels
mota suka tafi tukkuna muka koma cikin gidan.
Anti Yagana ta koma d'aki ta kwanta jiran dawowar Sukairaju kamar yadda maigidan ya fad'a.
Na bi shi saman na same shi a kwance.
Na zauna a d'an sanyaye ina fad'in." Ina kwana?''
Ya tashi zaune yana amsa da kulawa tare da tsira mini ido. Tun jiya yawan kallon nan da yake yi mini ya fara damuna."
Na ce." Ji ki ya yi sau'ki ko?"
Ya gyad'a kansa yana fadin." Alhamdulillahi, na ji sau'ki ina godiya."
A tak'aice na furta." Me za ka ci yanzu?"
"Shayi kawai zan sha idan da hali a yi mini farfesun kifi bakina babu test ko daya."
Na ce." Da hali mana da kaina ma zan yi maka sai ka had'a da bread ko?"
A tak'aice ya ce." Amma fara had'a mini tea din."
Na tashi na sauka kasa kicin na nufa Baba Tabawa tana ta gyare-gyare tare da wanke kwanunan da aka yi karin kummalo na hada duk abinda zai buk'ata na kai masa.
Na sake komawa kicin din Baba tana fad'in na bari ta yi na ce mata a a kawai ta bari ta huta jiki da jini tun asuba take tashi tunda aka yi rasuwar nan ga hidima da Sultan dama wani lokacin yana hannun inna uwani ko Gwaggo.
Farfensun ya yi masa dad'i sosai kuma ya sha da yawa ya hada da bread har da gyasa Yana fad'in." Ya yi mini dad'i sosai na gode."
Na ce." Sai shan magani?"
Ya gyad'a kansa yana dan murmushi na dinga cirowa ina bashi daya bayan d'aya ya sha. Sannan ya kwanta yana. yi mini godiya.
Sai wajan sha biyu muka yi sallama da anti Yagana wai ita da ta zo gaisuwa har sai da ya bata kudi bayan sanyawa da ya yi a kaita. Tare muka fito har da shi muka yi mata rakiya Sukairaju ya d'auketa a mota tana d'ago mana hannu.
Gidan ya kasance shiru kowa ya watse gabad'aya ma area ta yi tsit kamar ba a yi wata hada-hada ta jama'a ba tunda zahirin gaskiya ta samu mutane wannan kuma yana da ala'ka da su waye mazajen da ta aura da kuma fannin kasuwancinta sai danginsu daga can jos din da suka dinga zuwa.
Tun da ya yi sallar azuhur ya kwanta sai daf da la'asar tukkuna na tashe shi. Ya tashi kuwa da kuzari sosai ya ce zai yi wanka na ce a a tunda la'asar ce babu kyau haka annabi ya ce. Kuma gashi ba shi da lafiya.
Yana d'an murmushi ya ce." Ban ta'ba jin wannan hadisin ba Amina, sannan a ina aka ce idan mutum ba shi da lafiya ya daina wanka, ba zan iya ba gaskiya."
Na b'ata rai ina fad'in." Wallahi haka aka ce babu kyàu wankan daf da la'asar da bacci. Sannan kuma duk mai zazza'bi bayan son ruwa sai ka ga ciwon ya sake tsananta ka manta jiya kana zubawa jikinka ruwa ya rikice."
Ya ce." Kwarai kuwa hakane amma ai yau gabad'aya ban yi wankan ba fa tun safe kin ga kuwa babu lefi don na yi yanzu, tunda na ji sau'ki gaskiya."
Na ce." Kadai bari sai da daddare idan za ka kwanta."
Bai ce komai ba ya nufi toilet din ba bi shi a baya sai naga yana burush ina tsaye ina kallonsa ya gama ya daura alwala ya fito.
To a daran ranar can gidan Hajiya Maryam dai ba su rintsa ba duk da an cire rumfuna kuma maigidan ya sallami kowa amma su anti Yabi ba su tafi ba. Ita Nabila dama ta ci alwashin zama domin ta cigaba da kula da yaran. Anti Yabi Saliha da Rukky da shi Bashir din suka zauna wai sai an yi bakwai sai gidan ya kasance sai su kadai da masu aiki Taburni da Mairo sai yara Khalil Twins da Minal da suke hannun Mairo domin itace jigon kula da su shi Khalil yana tare da Adam tare suke kwana dakinsu daya itama Nusaiba tana nan ba ta tafi ba tukkuna.
Talatainin dare wajan biyu da yan mintina duk sun yi bacci Bashir ya kusa kansa d'akin da suke kwance wanda ya kasance nan ne bedroom din Maryam din matattarar sirrinta anan suke ta dabdalarsu. Anti Yabi da Saliha sun yi washar da su a makad'ed'an gadonta suna ta bacci yayin da Nabila ke kwance kasan kafet ita kuma Rukky na can kan wata shirgegiyar kujera dake can gefa bacci ya shammceta ta bar wayarta a kunne tana yi kallo take yi wata'kila baccin ya cimmata.
A kan Nabila ya tsaya yana fad'in." Ta shi, ke anti Nabila."
Ta tashi zumbur ta ganshi a tsaye dogare a kanta ta ce." Baka da hankali za ka shigo mana a wannan daran wai Bashir me yake damunka ne?"
Ya ce." Na gaya miki tun muna sheda juna ku sallame ni na ware, idan ba haka ba wallahi sai na yi muku illah."
Ta mutsika idonta sosai tana fad'in.'' Dame zan sallama ka Bashir na rantse da girman Allah zan yi magan..... Ba ta kàrasa ba ya fille 'yar k'aramar askar da take hannunsa mai bala'in kaifi ya yi mata bille a kumatu gefan idonta. Cikin tsananin kid'ima da tashin hankali ta kurma ihu! jini ya mamayeta fuska tunda askar ta shiga sosai kuma ta samu tsokar kumatu.
Gabad'aya suka tashi zaune.
Ya dinga bin su daya bayan d'aya yana fad'in." Illa zan yi muku na rantse da girman Allah idan ba ku fito da abinda yake rabo na ba kun ba ni, shegu yan iska taron tsintsiya babu shara, wallahi zan tsinke miki yatsun hannunki anti Yabi."
Ya dumfareta a zabure yana rangaji da askar a hannunsa mai la'kanin gayawa jini na wuce.... Suka yi tsuru-tsuru ganin yadda fuskar Nabila ta yi gaja-gaja da jini tana ta kuka.
Anti Yabi ta nuna masa kusa da ita tana fad'in." Zo ka zauna nan kusa da ni Bashir mu yi magana ka ji ko, kada ka sake illata kowa a cikinmu mu din 'yan uwanka ne.''
Ya yi rangaji yana wani abu da hannu kafin ya dumfareta a karo na biyu yana fad'in." Ku ba ni abinda yake hakkina kawai na tafi tunda dama kun sallamawa duniya ni.....✍️
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t
🌲🌳🌿☘️
*TALLAH!*
*DA MAGANI A GONAR YARO!!*
*08089965176*
*07084653262*
*Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.*
*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*
*07084653262 ko*
*08089965176*
*SIYAN NAGARI!!!!!!*
*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*
**Gudun aure paid book complete 2k akan telegram. Normal Gruop wsp 1k via 0542382124... Binta Umar gtbank.*
*07084653262*
*122*
Da farko har ya zauna kusa da ita kamar yadda ta buk'ata sai kuma ya tashi zumbur ya fara d'urawa Rukky ashariya yana fad'in ta daina kallonsa. Anti Yabi ta dinga jan hannunsa tana zaunar dashi yana fizgewa tare da ko'karin zuwa inda Rukky take domin dama can sakuwarsa ce kuma abokiyar fadansa.
Da azama ta d'auki wayarta ta fice daga d'akin cikin tashin hankali don ganin kamar itama yana so ya yi mata lahani.
Yabi ta fara fadin." Babu komai na kudi a d'akin nan Bashir tun daran jiya mun binceke komai sai sutturunta kai kuma namiji ne me za ka yi da kayan mata. 'Yar ta Nusaiba ce ta kwashe duk abinda muke hankoro ta boye sai waccan munafukar Nabila itama tana daya daga cikin wad'anda suka san sirrinta amma saboda ba'kar mugunta ta'ki ba mu goyon baya. Da tun farko ta amince mana da duk haka ba ta faru ba ni kaina a cikin wannan nazarin nake ace an watse ba mu tashi da komai ba."
Nabila na kuka take fad'in." Anti Yabi ba kya ganin abinda ya yi mini lefi ma ki ke ba ni, kina ganin yadda ya yanka min kumatu amma duka baku da damuwa."
Saliha tace." Ke ma kin so haka ta faru Nabila tuntuni muke miki magana kina nuna ke ba ki san komai ba bayan na tabbatar da cewar mukkulin dirowar can yana hannunki mugunta ce ta sanya ki boyewa tunda gashi kina fad'in za ki zauna a gidan. Ina yaran suke da za ki ce zaki kula dasu duk sun zama samari. Su wad'anan 'kananun dole ubansu ya mayarwa da iyayensu Nusaiba kuma ba zama za ta yi ba itama gidanta zata koma, kina so mu tafi sai ki yi wad'aka da dukiya ko to ai duk cikinmu babu yaro mun fahimci me ki ke nufi ."
Yabi ta ce." Tunda abin ya fara zama haka Nabila ki fito da key din dirowar nan nasan anti Maryam a cike take ajiye sirrikanta wata'kila zamu samu gwalagwalanta a ciki da takardun shagunanta da ta mallaka sai mu d'auki wani abu daga ciki mu kasafta a tsakaninmu.."
Cike da damuwa da jin rad'adi ta furta." Ban san inda key din nan yake ba anti Yabi ko ku yarda ko kada ku yarda wallahi ni ma ban d'auka ba. Wayoyinta da ATM dinta suna hannun Nusaiba to key din ma yana wurinta ku je ku binkiceta.
Ya tashi yana rangaji da d'ura ashariya ya fita falon ya ritsa Ruky a zaune domin d'akinsu Mairo ma a rufe yake zage-zagen da yake yi ne ya tashe kaf har da yaran abinda ba su saba ji ba sai kuka. Adam da Salim suka tashi a firgice yayin da Bashir ya dinga bugun kofar d'akin da Nusaiba take kwance da yaranta. Itama a gigice ta tashi tana bud'e kofar ya yi ciki da ita ya ritsata. Salim da Adam suka bi shi d'akin. Itama Rukky ta koma d'aki a guje tana gaya musu gabad'aya suka fito a gigice
Lokacin har ya sa mata wu'ka a wuya wai ta bashi kud'i da mukkulin dirowa an ce komai yana hannunta.
Salim ya yi tsalle ya buga masa duka a bayansa tunda yana tsakiyar Nusaiban ya raba kafufunsa a kanta ya saita ta da wuka.
Gidan ya cika da koke-koke a guje-guje. Mairo da gudu ta ja yaran suka koma d'akin suka rufe. Salim ya d'agata ta shi da gaske ya gilla mata wukar a wuya har ya yi sheda ta matsa gefe tare da ri'ke ma'kogwaronta da ya fara d'an fitar da jini kad'an. D gaske yankar rago ya yi shirin yi mata. Jama'a 'kwaya bala'i ce.
Yaranta ihu kawai suke yi. Nabila ce kad'ai ta iya zuwa wurin da take amma su anti Yabi suna can sun rirri'ke Salim da ya shemar da Bashir din a kasa yana dukan hancinsa.
Da yake ba sosai yake kashe wayoyinsa idan zai kwanta ba. Cikin bacci muka ji kiran waya gabad'aya kusan a tare muka tashi zaune ni dashi ya d'auka da sauri yana sanyawa a kunnansa muka ji muryar Adam cikin rud'u da tsananin tashin hankali yana fad'in." Baba ka zo babu lafiya ka zo yanzu Bashir ne zai kashe anti Nusaiba."
Da wani irin hanzari ya sauka daga gadon na taso na biyo shi ya ce na koma. Har ga Allah na tsorata duk da gidansa cike da tsaro ina jin tsoro ya fita jin ana maganar kisa.
Na koma na zauna cikin tsananin tashin hankali da damuwa wace irin masifa ce wannan kuma.
Lokacin da ya shige gidan Bashir din ya samu nasarar ta shi yana ta kai wa Salim suka da wu'kar da take hannunsa 'karama ce amma kisa da illa take yi nan take. Ihu da koke ya cika gidan ita Nabila ga yanka a kumatu ga iskokai.
Da hanzari ya nufe shi duk da ya hangi abinda yake hannunsa. Amma da ya gama fahimtar bashi da wani kuzarin kirki irin na maza dalilin shaye-shayen da yake ya dakusar da garkuwar jikinsa sai ya nemi ma'karfafansa ya kai masa duka a k'irji kafin ya falla masa mari ya murd'e hannunsa da kyau ya k'wace wu'kar ya mi'kawa Salim ita ya kar'ba duk ya yi wujiga-wujiga ai yayi namijin kokari ma wai aka ce ranar naka sai naka tabbas da da tsautsayi yau Nusaiba zata ba'kunci lahira itama.
Ya ce da Adam maza ya fita ya kira masa Sukairaju da 'Dahuru sune majiya k'arfi sosai fadi yake kisan kai za ka yi mana a gida Bashir dama dan ta'adda ne."
Ya yi shiru yana ciccije baki. Ya dubi Nusaiba dake zaune a gefe yaranta biyu a kusa da ita tana share hawaye sai ya girgiza kansa cike da tsananin damuwa ya kalli Anti Yabi yana jin kamar itama ya falla mata mari, tuntuni ya fahimci bata da hankali gabad'ayansu babu na za'be itama Maryam din da yake shedarta ashe ba'kar macijiya ce.
Tun a d'akin Sukairaju da 'Dahuru suka fara tafkar Bashir ya hana su ya ce dai su caje jikinsa tsaf idan da wani makamin su fito dashi haka kuwa aka yi irin wannan wu'kar uku ce a soke a jikinsa sai daurikan wiwi da ganye ya ce su fita da shi.
Ya juya yana kallon Saliha ita din ya tambaya menene abinda ya faru. Ta fara kame-kame.
Nusaiba tana kuka ta ce." Ba haka ba ne wallahi baba tunda Momi ta rasu suke yi mata bincike d'aki wai tunda sun ji an ce ba su da gadonta. Sun 'ki tafiya ne tunda sun shirya halaka ni, anti Yabi duk abinda Momi ta yi muku da irin abinda za ku saka mata dashi kenan yau kwana uku da rasuwarta kuna rigima har da zubar da jini akan dukiyarta. Ba mu da iyaye wallahi domin ba zamu ta'ba nuna ku a matsayin iyayenmu ba."
Suka yi shiru anti Yabi ta yi kasa da kanta tana fad'in." Ba haka ba ne Nusaiba wallahi kada ki zarge mu domin rashin Maryam na kowane. Ba mu da yadda za mu yi da Bashir tunda ya zo yake daga mana hankali wai a raba gado a bashi rabonsa, amma mu ai mun fi buk'atar Maryam akan abinda ta tafi ta bari na dukiya."
Babu wanda ya ce mata komai, ya sake duban Nusaiba a karo na uku yana fadin." Ya aka yi har ya shigo ya yi miki Illa abinda nake so na ji kenan.
Tana kuka ta ce." Wai sai na bashi wayoyin Momi da atm din da kuma mukullin dirowar da take ajiye muhimman abubuwanta."
Ya gyad'a kansa cike da tsananin al'ajabi da mamaki, shi kaddararsa kenan abokinsa ya rasu ya bar shi da rikicin iyalinsa in ba haka ba shi a tarihin rayuwarsa da family dinsu wani abu na tashin hankali makamancin wannan bai ta'ba faruwa ba.
Ya kama hanyar fita yana fad'in." Zo mu je d'akin ki nuna mini dirowar.
Ta tashi da sauri tare da sanya yaranta a gaba ta bi bayansa su kuma suna tsaye cikin jin kunya Ruky ce kawai take tsugune gaban Nabila tana yi mata tofi.
Madaidaiciyar dirowa ce ta mussaman domin ba irin ta gado ba ce wannan maybe daban ta sanya aka yi mata.
Ya d'an ta'ba ya ji yanayin katakon yana da nauyi. Sukairaju ya kira a waya ya ce ya dawo. Ya fito falon Salim da Adam suna tsaye suna magana ya a kira Mairo. Adam ya dinga bubbuga kofar dakinsu tana fad'in." Wanene a cikin tsoro."
Sai da ta yi muryar Adam din tukkuna ta bude ta fito Taburni ta biyo bayanta duk sun gigice kuma a tsorace suke. Ya ce su had'o kan yaran kaf su biyo bayansa. Haka akayi kuwa yaran duk suka fito ganin Babansu ya sanya suka ruga wajansa suna kuka tunda a gabansu abin ya faru lokacin da Bashir din ke ko'karin kai wa Nusaiba duka ga fuskar Nabila da ta'bon yanka da jini."
Duk da Bashir din baya gidan Nusaiba kasa zama ta yi a gidan dalili ta tsorata ainun da 'yan uwan momin nasu. Salim da Adam ne kawai suka koma dakinsu ita kuma ta bi bayansa da yaranta tana kuka cikin tashin hankali ga wuyanta yana d'an yi mata zugi kad'an dole sai ta je asibiti.
littafin gudun aure na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba.
Haka muka kàrasa kwana cikin alhini da damuwa mai tsananin gaske.
Da safe da wuri Salim ya shigo ya biyo ni har d'aki ya gaishe ni amma bai yarda mun had'a ido ba ya ce mini asibiti za su je yanzu da Nusaiba na biyo shi falon sai na same su tare da maigidan a tsaye suna magana itama ta gaishe ni cikin jin nauyi na amsa tare da tambayarta jikin ta ce da sau'ki.
Sai