Author : Badiat Ibrahim Mrs Bukhari Category : Read Hausa Novels
da saukar
mana, yaranmu suka ci gaba da hayayyafa, suna kulawa damu. Audu yaga ranar ƴaƴa matan
daya wulaƙantani sabida haihuwarsu. Shagari kuma saida matarshi ta tatikeshi tas, sannan ta
nemi saki, dole ya saketa, rayuwa ta tagayyarashi, a sakamakon bijirema iyaye da yayi. Hindu
kullum cikin istingifari take, burinta ta kyautata mun. Su Zainaba da Mariya, sunyi aure, suma
dai wuyar suke ci. Wata ranar asabar, aka wayi gari da rasuwata."
Audu:
Ya jijjiga da mutuwar Shamsiyya, yayi kuka har saida ya kwanta ciwon da shima saida aka
kusan rasashi. Su Shatu ba'a maganar tashin hankalin da suka shiga ma. Haka suka dage suka
gina masallaci da sunan ladan ya dinga isa kabarin mahaifiyarsu, masallaci lafiyayye suka gina,
mai kyau. Audu yana zuwa kai ziyara kabarin Shamsiyya akai akai. Rayuwa kenan. Haƙiƙa
wannan labarin akwai ɗumbun darasi mai tarin yawa. Shamsiyya taci ribar aure, tunda ta samu
yaran da suke mata adda'a ba dare ba rana. Ta samu mijin da yake raba dare yana roƙa mata
rahamar mahaliccinta, yana yi yana kuka. Haƙuri yayi a rayuwa, Allah ya datar damu. Inaima
mabiya wannan labarin, da iyalan malama Shamsiyya ta'aziyyar mahaifiyarsu Allah ya kafarta
mata. Anan na kawo ƙarshen labarinsu Shamsiyya.
Bari mu leka Saleri, gidansu Musina kuma:
MRS BUKHARI
[27/01, 11:04 am] BADI'T IBRAHIM: *_GAWURTATTU UKU2023_*
*_TALLAH TALLAH TALLA️️️️️_*
_A HAYYEH SAMAH MATAH_
*Ku shiga wannan link ɗin don zaɓar kaya masu rahusa*
https://chat.whatsapp.com/G6BmHCxso0rDZyWVQGgYYj
----------
No
07067964894
*_INA KUKE MATAN KWARAI MATAN DA SUKA AMSA SUNAN SU NA MATA A DUNIYA KU
GARZAYO KUZO M A C DON ZABEN NA KWARAI KI DAURA ASAN KIN DAURA SAI
ATAMFA DA LACE DA SHADDA, MATERIAL WITH SHOE'S AND BAG WITH JEWELRIES
DAGA MAMAN ANNUR COLLECTION._* *_ANAN KWALIYA ZATA MAIDA KUDINTA GAREKI, KIFITO ASAN KIN FITO KIN FASA
TARO SAI M.A.C AKAN FARASHI MAI RAHUSA SAYEN NAGARI MAIDA KUDI GIDA IYA
KUDIN KI IYA SHAGALINKI_*
*_TANA KANO TANA AIKAWA KO INA DA IKON ALLAH A CIKIN AMINCIN DA YARDAN
UBANGIJI_*
*_YAN UWA INA MASU SON SUYI SANA,A BASU DA JARI TOH GA DAMA TA SAMU,
INJI MAMAN ANUR DON ZAKU IYA DAUKAN KAYAN MU KU TALLATA KU DORA NAKU
RIBAN SAMA ZAMU AIKA MAKU KAYA GA MAISHI DA SUNAN KU A DUK INDA CUSTOMER
DIN KU YAKE BA TARE DA MUYI SAVING NO BASHI BA KUMA BA ZAISAN BA DAGA
WURIN KI KAYAN YA FITO BA TAKEN MU GASKIYA DA AMANA, MUM ANNUR
COLLECTION DA KARAMAR RIBA MUKA DOGARA SABODA NEMAN ALBARKA SAI KUN
ZO _*
[27/01, 11:04 am] BADI'T IBRAHIM: Gawurtattu uku,zasu buɗe aji na musamman da azumi,don
koyar da girke girke na musamman na azumi don kun san mu mata ƴan adone,wajen yin girki in
akace baki iya girki ba to tabbas mijinki fa kullum yana kan hanyar yawon restuarent, sannan
idanuwansa suna kan ƴammata saboda ya samu sarauniyar girki, kada ki bari a barki a baya
don gwangwaje me gidanki.
Domin nema ƙarin bayani,sai ku tuntuɓi waɗannan numbobin
07068606171
08104335144
08179523215
*GAWURTATTU UKU A SABUWAR SHEKARA TA 2023*
*_Ina kuke masoyan gawurtattu uku ga su ssun dawo muku da wasu sabbin labaransu a
wannan sabuwar shekarar, wannan karon salon gawurtacce ne, ku hanzarto kar ku sake ayi
babu ku._*
_Sun shirya tsaf a wannan karon don kawo muku labaran da zakuyi fahari da su, tafiyar mai zafi
ce sannan ta musamman._
*_Haziƙai kuma gawurtattu ukun sun shirya ne domin kawo muku gwarazan labaran da zaku yi
alfahari da su._*
*MATA IYAYEN GIJI*
_Mrs Bukhari_
*INDA BA ƘASA..!*
_Ummu Maheer_
*KARO ƊAYA...!*
_Ummu Affan_
_LITATTAFAN GABAƊAYA AKAN FARASHI MAI SAUƘI DA RAHUSA 1K_
1 500
2 700
3 1000
_Kai tsaye zaku tura kuɗinku ta wannan account number ɗin._
2212328303
RABIATU BASHIR
Zenith bank
_Don Allah wannan karon ba ma buƙatar katin waya, idan baka da account to kaje POS ka
bada 50 kob 100 a cikin kuɗin a turo ta account number please._
_Ƴan ƙasar Niger kai tsaye zaku turo ta nan._ 0706 860 6171
*DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI A TUNTUƁI ƊAYA DAGA CIKIN LAMBOBIN NAN.*
0810 433 4144
0817 952 3215
0706 860 6171
*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU UKU A SABUWAR SHEKARAR 2023
SABON SALO SABON TAKU.*
_TEAM GAWURTATTU UKU 2023_[08/04, 19:57] Mrs Bukhari: GAWURTATTU UKU
LAMBA TA ASHIRIN DA BAKWAI
MRS BUKHARI
SALERI:
Zufa ce ta shiga yanko musu dukkansu. Haƙiƙa sunsan sun cutar da Musina da yaranta. Kuma
haƙiƙa Idi gaskiya ya faɗa, Musina bata da wani amfanin da take ma Yawale, tunda ba rabon
kwana yake yi da'ita ba. Kuma ba ciyar da'ita yake yi ba. Bata da maraba da me zaman kai.
Jamilu ne ya daure yace. "Haba Idi bai dace kace hakan ba, ba daidai bane ka kashema Musina aurenta ba. Yawale
dai mahaifinku ne, kuma mijin musina ne, ni ina ganin ayi sulhu, tunda dai mun gane
kuskurenmu, shi kanshi Yawalen zai sauya." Jamilu na wajena yace.
"Kawu rabuwar ita muke fatan ta zama alkhairi in sha Allah, ya saketa kawai, ta tattare
kayanta mu baku iska." Ƙasimu yace.
"Nima ina bayan ƴan uwana, sakin dai muke nema. Ɗaya bayan ɗaya yarana duk suka ce
saki suke buƙata. Ni dai ina gefe ina jin bidiri, lallai yara ni'ima ne babba, duk uwar da take da
yara. Ta tsaya tsayin daka dan ganin ta basu tarbiyya mai kyau. In sha Allah gaba zata yi
dariya. Yawale yaƙi magana fur, sai su Jamilu ne suke ta ba da haƙuri. Daga baya Yawale yace. "Kuimun afuwa yarana, Musina ki gafarceni, tabbas ban cancanta inta riƙe igiyar aurenki
ba. Amman rabuwa dake zai iya zamemun sular lalacewa, domun kece filita madubi a
rayuwata. Amman in dai kin zaɓi yaranki akan aurenki, zan baki iska yanzu." Nafi minti uku
banyi ko tari ba. Idanun yarana sai yawo suke yi a jikina, dan duk sun kafa mun idanu. Sai naji
tausayinsu, da ganin nabi umarninsu.
Farin cikinsu shine nawa, dan sune uwa, uba, dangi a gareni. Dan haka ka sauwaƙe mun,
kaje ka rungumi yaranka da matarka abun soyuwa a gareka." Yawale yana hawaye yai mun
saki ɗaya. Wallahi sai naji na sauke nannauyan ajjiyar zuchiya, ji nake tamkar an sauke mun
wani ƙaton dutse a ƙirjina ne. Farin ciki ya ziyarceni. Yarana sukaita lallashina. Da yamma lis Idi
yasa ƙannenshi a gaba zuwa gidan Kattume dan ya ganta, su sanar mata halin da ake ciki.
Kattume:
"Kai Yaya Idi, a gaskiya naji daɗin hukuncin da kuka yanke sosai. Uwo wallahi tausayi take
bani. Tasha wahala sosai duk sabida mu. Amman Alhamdulillah gamu mun rayu, kuma muna
tsantsar jin sonta da tausayinta. Wallahi duk ɗan ragowar kuɗin cefane inna rage, Uwo nake
hidimtawa dashi, duk dan in bata farin ciki. Baba Kumatu kuma in sha Allah ƙarshenta ne yazo"
Sun jima suna tattaunawa, sannan suka jira mijinta ya dawo, dan suna son Kattume ta bisu, tayi
sallama da Uwo. Izinin binsu mijinta ya bata, yaronta na goye kawai ta goya suka tafi.
Saleri:
Yawale:
Jiki a mace mus Yawale ya shiga ɗakin Kumatu. Tattaunawa ya samu sunayi ita da yaranta.
Kumatu tabi kayan tsarabar da Idi ya ba Yawale da kallo.
"Malam sai yanzu ka shigo? Kayan hannunshi ka karɓa kai ka mance Idi Ɓarawone, kasan
ko sana'ar sata yake yi a birni? Ance fa harda mota yazo." Yawale ya zauna a ƙasa, ya ajjiye
kayan a gabanshi, ya dubi Kumatu yace.
"Kece kika haifi Ɓarawo Kumatu, Musina bata haifi ɓarawoba, amman ɗanki me yake yi inba
sara suka ba? Duk garinnan ansan ɗanki sara suka ne, tunda har zaga gari akayi dasu, yara na
jifansu, sakamakon nakasa ɗan mai gari da suka yi. Kumatu kin cutar dani gaskiya da yawa. Idi
yasa na saki Musina, wallahi kwarjinin yaranta ne yasa dole na saketa. Kema na sakeki saki
biyu, ki tattare ki koma gidanku.'" Hannu Kumatu tasa aka, taita kururuwa tana ihu.
"Yawale ni ka saka, bayan ka gama cinyemun ƙuruciyata? Ina zanje to? Narantse da Allah
babu inda zanje, zanyi zaman ƴaƴana, tsofai_tsofai dani, iyaye duk sun kwanta dama kace ka
sakeni." Yawale yace.
"Kamar yanda kika sa ƙuruciyar Musina ta ƙare ba tare da taji daɗin aure, da ɗaɗin miji ba
ba. Ai kukan kurciya jawabine, mai hankali yake ganewa. Kayan daya shigo dashi ya ɗiba ya
fice a ɗakin.
MUSINA:
Washe gari da sassafe Jamilu ya jibga mana kayanmu a mota. Haka na dinga bin maƙwabta ina
sallamarsu. Maƙwabta suka rakoni har gaban mota, suna ɗagamun hannu.
Kallon gidan da aka kawoni tun ina yarinya nake yi, gashi na bar gidan ina da girman
shekaruna. Tun ina hango gidan harna dena gani. Tunanina bai tsaya ba har saida muka iso
Azare. Nanma haka naita sallama da ƴan uwana. Sukaita taya ni murnar ganin Idi. Ina kuka
wiwi na rabu da dangina, muka nufi Jos. Tafiyar awa ɗaya da rabi muka yi, sai gamu a Jos garin
sanyi, garin dankalin turawa, da kayan lambu.
Mrs Bukhari
[08/04, 19:57] Mrs Bukhari: LAMBA TA ASHIRIN DA SHIDA
GAWURTATTU UKU
MRS BUKHARI
JOS:
"Musina, musina!! Wata mata ce take kiran ƴarta da babbar murya"
"Na'am Mama, yanzu zamu gama, Alawiyya nake jira. Ƙasimu yaƙi ya canja rigarshi mama"
Musina duk ita kaɗai tayi wannan maganar, mahaifiyarta Hadiza ta shigo ɗakin tace.
"Kun fiye nawa in dai zaku fita, ga kuɗin kitsonku ku biyu, wannan hamsin ɗin kuɗin askin
Ƙasimu ne. Ki kula dasu Musina, kuyi maza ku dawo, kunga gidan babu abunda muka yi." Tana
cikin maganane mahaifinsu Musina ya fito daga uwar ɗaki, cikin shirin zuwa aiki.
"Abban Musina yau da wuri zaka fita haka?" Kallon yaranshi yayi, ya musu murmushi, duk
suka zube suka gaisheshi cike da ladabi. Da fara'a ya amsa, tare da jin lafiyarsu ɗaya bayan
ɗaya. Saida yaga fitarsu ya dubi Hadiza yace.
"Ba kasuwa zani ba, yau shago sai dai Aminu ya buɗe, Bauchi nake son in gangara,
Amman bazan kwana ba a yau zan dawo. Shiru tayi tana dubanshi, sannan tace.
"To Allah ya tsare, buhun shinkafarmu ya ƙare. Wake da garin tuwo ya rage mana kawai.
Sai maganar gudunmawar da zan yi ma Fatima na biki, yanzu yarannan da sun dawo kitso,
zamu tafi lalle, gobe kuma in muka tafi gida, sai bayan biki zamu dawo. Ajjiyar zuchiya ya sauke
yace "Sau nawa zan faɗa miki ne Hadiza a dena bari sai abinci yayi ƙaranƙab za'a faɗamunne?
Wallahi bana jin daɗin hakan. Zan sa Aminu ya kawo buhu ɗaya a shago, ya kawo.
Gudummawar da zakiyi dubu ashirin ta isheki?"
"Abban Musina da wai dubu hamsin nake so, sabida kaga nice babba a gidan."
"To inna dawo zan baki, zan bada buhun shinkafa ki kaima su malam a ƙara a gara, Aminun
zai kawo miki dubu hamsin ɗin kawai, ni na tafi" Da adda'a ta bishi harya fice. Motarshi ya hau,
ya kama hanyar Bauchi. Cikin awa ɗaya da rabi ya shiga Bauchi. Azare ya nufa, daga nan ya
nufi Saleri. A gefen ƙofar gida ya ajjiye motar tashi, ya fito ya buɗe bayan motar, tsaraba ce ta
kayan marmari yayo, da shaddajin maza, da takalman maza. Saminu yana zaune a ƙofar gida a
cikin abokai. Zabura yayi da ganin Idi ya fito a cikin mota, yayi wani mugun fari, yana sanye
cikin kayan kamala,
"Yaya Idi kaine ka dawo, ko dai gizo kake yi mini? Murmushi Idi yayi yace.
"Nine Saminu, kira abokanka su shiga da kayannan ciki." Da sauri ya jiya, Idi kuma ya
girgiza kanshi, yana tuno sanda mahaifinshi a ingizoshi dai_dai inda yake, yayi mishi jina_jina.
Ya tafi ya bar mahaifiyarshi a cikin zulumin rayuwa yake yi ko mutuwa. Harsu Saminu suka
kammala shiga da kayan yana tsaye. "Yaya Idi mun gama shigarwa" Murmusawa yayi kawai, ya nufi cikin gidan bakinshi ɗauke
da sallama. Da Kulu ya soma cin karo, hannunta riƙe da kwanukan wanke wanke. Ihu tayi ta
watsar da kwanukan.
"Uwo kizo ga Yaya Idi ya dawo uwo"
Musina
Kamar a mafarki nake jiyo wannan kiran, da sauri muka taso dukkanmu muka fito. Kumatu da
su Sauma'iyya ma a guje suka fito. Mudi, Jamilu duk sunyo waje, su A'i uwar gulma harta iso
gaban Idi. Muna haɗa idanu na fashe da kukan jin daɗi. Shima hawayen naga yana zubarwa.
Kumatu kuma jikinta ne ya shiga ƙyarma. Su Zubaida da Alawiyya sun zagayeshi, shi kuma ya
riƙe hannayensu.
"Idi kaine yau a tafe, maraba lale" Inji Mudi kenan. Tsugunnawa yayi ya dinga gaishe da
iyayen nashi ɗaya bayan ɗaya. Kumatu a daburce ta amsa mishi gaisuwarshi. Ƙasimu ne ya
shigo a guje, dan da dukkan halama labarin dawowar Wanshi ta isar mishi. Juna suka rungume,
suna ta dariyar farin cikin ganin juna, juyawa nayi na koma ɗaki. Su Kulu ne suka shigo da Idi
ɗaki. Kafin kace me, abinci har daga maƙwabta akaita kawowa, gida ya cika fam, Idi ya kasa
samun keɓewa damu. Jamilu ne ya jashi suka tafi masallaci dan gabatar da sallar la'asar. Basu
shigo gidan ba, sai wajajen yamma sakaliya.
"Uwo ki shirya kayanki tsab, inason mu wuce da yammannan ne" Dubanshi nayi nace.
Ɗannan daga zuwanka, bazaka bari gobe muje Azare ba, suma su ganka ba? Sannan
bamu zauna munyi hira ba ma" Murmushi yayi mun.
"Hakane Uwo da yake na ɗokanta inga na ɗaukeki a gidannan ne, ina da gida a birni na
siya. Ƙasimu yace.
"Aure fa Yaya?" nima tambayar da nake son yi mishi kenan.
"Nayi Aure harda yarana uku. UWO, ƘASIMU, ALAWIYYA sai mahaifiyarsu Hadiza.
Mahaifinta shi ya zamemun uban gida, bayan korata da Baba yayi. Babban shagon hatsi ne
dashi, a ƙaramar kasuwar ƴan tifa, ana kiran shagon da suna shagon ɗan Aljanna. To ganin
gaskiya da amanar dana riƙe mishi ne, yasa ya bani auren ƴarshi Hadiza, nima a hankali saina
buɗe shagon saida hatsin a kasuwar. A cikin wannan sana'ar na samu rufin asiri, na sai gida,
ina tuƙa ƴar motata. Uwo su sunyi Aure ne?" Kulu ce ta shiga bashi labarin abubbuwan da
sukaita faruwa bayan tafiyarshi, da halin da suke ciki a yanzu hakanma. Kuka ya dinga yi kamar
ƙaramin yaro.
"Uwo kiyi haƙuri nayi jinkirin zuwa, wallahi duk neman da nake yi, sabida ku nake yi,
shiyasa banzo da wuri ba, amman komai yazo ƙarshe, gabaki ɗayanku daku zan tafi, su Kulu
kaɗai zan bari anan tunda aure suke yi. Jamilu naji daɗin yanda kuka kula da Uwo kuka share
hawayenta. Amman tunda nine babba, ni zanfi so dukkanku, in tafi daku birni. In yaso in damina
tazo, saimu ɗungumo muzo muyi noma mu koma. Ni dama hatsi nake sayarwa, kaima Jamilu
haka. Sai mu sake buɗe wani shagon a kasuwa, kai da Mustapha ku dinga zama, ni kuma da
Ƙasimu saimu zauna a nawa shagon. Alawiyyata kuma, zan nema mata gurbin aiki a babban
asibitin juth, ita Zubaida kuma saita koma jami'ar Jos. Jamilu yace.
"Shikenan Yaya ni hakan yayi mun wallahi sosai, kuma ina da hatsi a rumbu mai yawan
gaske, sai a kira akori kura ta kwashe tas ku tafi dashi, amman bazan biku ba tukunna, saina
girbe amfanin gonana, sai in biyo sawunku. Ƙasimu yace.
"Yaya shawararka tayi kyau, gara mu tafi kawai, zanje inyi sallama da yarinyar da zan
Aura, dan inna tafi, sai lokacin bikin zan dawo, ana ɗaura Auren, sai in ajjiyeta in koma. Sai a
lokacin nayi magana.
"Kana da wajan da zaka ajjiyemu mu duka ne, ba zamu takurama mai ɗakinka ba kuma?
Kai kuma Ƙasimu ban yadda kayi aure, ka ajjiye matarka aƙauye ba, sai dai ka tawo da'ita" Idi
yace.
"Uwo kenan, takurawa kuma? Ina da ɗakin da zan ajjiyeku, babu damuwa in sha Allah,
sannan su Ƙasimu akwai shago a ƙofar gida, sai su dinga kwana a shagon, zansa a gina musu
makewayi a cikin shagon, tunda yana da girma. Uwo ai na isa da gidan nawa, kune kuma
gatana." Albarka na dinga sa mishi, ina share hawayena. A haka Yawale ya buɗe labule ya
same mu, shigowa yayi, su Jamilu da Mudi suka biyo bayanshi. A bakin gadon bono suka
zazzauna. Idi ya matsa kusansu, ya sake gaishe da su Mudi, sannan ya gaishe da Yawale. "Idi kaine a gari, ya gida ya iyalai?" Inji Yawale kenan.
"Lafiya lau