Dahuwar Kawo Book Compelet Ameera Adam

Author :  Ameera Adam Category :  Read Hausa Novels

Chapter   40 / 46

117K to 120K   out of 137.8K words

zafafe yana barin wurin, a daidai lokacin Nabila ta ƙarasa tana jin abin da yake faruwa. Inno tana shirin yin magana suka ji wani sabon kukan daga ƙofar shigowa. Salame 'yar gidan Larai ce ta ƙarasa cikin kuka, kowannesu fuska ɗauke da mamaki suka wurga mata tambaya.

"Lafiya Salame?"
Sai da ta share hawaye sannan ta ce, "Jamilu ne ya sake ni."
Kusan lokaci ɗaya suka ɗauki salati, cikin kumfar baki Yaya Inu ya ce.

"Uban me kika yi masa da zai sake ki a daren nan ga tsohon ciki a jikinki."
Salame ta ja majina ta ce, "Saboda ya sayo shayi ruwan bunu da awara zai sha, ni kuma na ji sha'awarsu na ɗauki ƙwaya biyu da shayin na sha. Shi ne kawai ya sake ni."
Ta ƙarasa maganar cikin kuka, takaici ya mamaye mutanen da suke tsaye. Yaya Inu a ƙufule ya ce.

"Shayin banza da wofi da har zai sake ki a kansa, wannan ai rashin hankali ne. Bai ga halin da kike ciki ba ne?"
Larai da ke tsaye ta saki murmushin takaici ta ce.

"Dama gwano ai ba ya taɓa jin warin jikinsa, yanzu mai gida har kana da bakin magana don an sako maka 'yarka, kuma a kan dalilin da bai taka kara ya karya ba? Ai na sha faɗa maka, wannan auri sakin da kake yi ba zai haifar mana da samun ɗa mai ido ba, domin kai ma uba ne kuma duk abin da ka yi wa 'yar wani sai an yi wa ta ka. Idan ba ka manta ba fa, Raliya a kan ƙosai ka sake ta. Mariya kuma a kan man shanu, ga Abu kuma a kan kai yara almajiranci. Ni ma da kake zaune da ni saboda na zama kujera ce, duk tarkacen yaran da ake tafiya a bar maka ni nake riƙe su. Ka ga yanzu kai ma kana da zaurawa uku kenan a gida, wannan kaɗai ya isa ya zame maka izina..."
A fusace ya katse ta. "Larai ni za ki yi wa rashin mutumci a gaban mutane?"
Baba Ibrahim ya ce, "A duk maganganun Larai babu cin mutumci, sai zallar gaskiyar da har yau ka gagara gane ta Yaya Inu, ya kamata ka dawo cikin hayyacinka. Aure-auren da kake yi ya yi yawa wallahi, yanzu ko wuƙa aka saka mini ba zan iya lissafa adadin mata nawa ka aura ba. Ka gyara zamantakewarka da iyalinka, sai ka ga Allah Ya daidaita lamuranka. Duk da dama aure da mutuwa yana wurinsa, amma ka sani akwai jarabtar da Allah yake yi wa bawa a kan abin da yake aikatawa."

Mai Yasin da ke gefe ya zuba wa Salame da kuka idanu yana lashe baki, saboda fara ce tas kamar Yaya Inu sai dai 'yar ƙibar mahaifiyarta da ta ɗauko.
'Yanzu wannan danƙwaleliyar aka saki, ai kuwa wannan mijin nata an yi sakarai.'
Malam ya furta a cikin ransa.

"To tsohon munafuki, ai babu kuɗin kowa a cikin auren da nake yi, kuma babu ƙaton da yake ciyar mini da su idan sun dawo gida. Ke shige gida muje." Yaya Inu ya ƙarasa maganar yana tasa ƙeyar Salame shi ma ya shige ciki, daga haka kowa ya watse.

CIKIN DARE

Tun da Mai Yasin ya ci karo da Salame ya kasa zaune ya kasa tsaye, haka kawai ya ji wani abu yana fisgarsa a kanta. Duk da tana yanayin kama da Laraba amma ta fi Labara zama cikakkiyar mace 'yar duma-duma kamar yadda yake muradi, Inno da ke gefensa ta miƙe za ta yi masa sallama ta ce.
"To Malam ni zan wuce ɗaki ko akwai abin da kake buƙata a yanzu?"
Wani munin Inno ya gani saboda yadda Salame ta mamaye zuciyarsa, haushinta ya kama shi don haka ya ɗan yi tsaki a hankali ya ce.
"Babu komai za ki iya tafiya!"
Inno ta yi mamakin yanayin furucin da ya yi mata, ganin haka ya sa Mai Yasin ya wayance da cewa.

"Raina ne duk a ɓace wallahi, a ce ka saki mace da tsohon ciki wannan ai hauka ne."
A fili Inno ta saki ajiyar zuciya cikin jin daɗi, don yadda Mai Yasin yake nuna wa zuri'arta kulawa abin yana burge ta.

"Lamarin babu daɗi dai sam malam, ni bari na wuce sai da safe."

Mai Yasin ya amsa mata yana alla-alla ta fice, shi kaɗai ya dinga zarya a ɗaki yana tunanin yadda zai ɓullowa halin da yake ciki. Wata dabara ce ta faɗo masa ya saki murmushi mai sauti, kamar wanda aka yi wa dole haka Mai Yasin ya zauna tunkur har ƙarfe biyun dare ta cika. Daga shi sai gajeren wando ya zare sakatar ƙofa ya nufi sashen Yaya Inu, wannan ne zuwansa na farko sashen don haka cikin sanɗa ya kama gajeriyar katangar ya dira. Sakatar ƙofar ya zare ya bar ƙofar a buɗe saboda koda rana ta ƙwace masa ba zai sha wahalar guduwa ba.

Da yake da ɗan hasken farin wata, cikin sanɗa ya dinga bin ɗakuna yana leƙe, sai dai idan ya zura kai ba ya iya hango komai ta ciki. A haka har ya nufi ɗakin da Yaya Inu yake kwance ya shiga, domin jikinsa ya ba shi a nan Salame take a kwance. Tun dag bakin ƙofa Mai Yasin ya kwanta ya fara jan jiki a hankali, don kada a ji motsinsa a haka har ya haye kan katifar da Yaya Inu yake kwance.
Cikin bacci Yaya Inu ya ji ana shafa masa jiki, da ɗan magagin bacci ya ce.

"Hansatu ce!"
Jin muryar Yaya Inu ya sa ƙirjin Mai Yasin ya buga da ƙarfi, amma don kar ya yi saurin gano shi sai ya ce.
"Ummm."
Tsaki Yaya Inu ya yi ya ce, "Ke dai kin cika jabara Hansatu, don masifa na ce miki zazzaɓi ne a jikina amma saboda ƙalata sai kin zo kin tsotse ragowar ruwan jikina."
Mai Yasin ya yi shiru ya cigaba da kai hannun yana laluben Yaya Inu, shiru Yaya Inu ya yi yana mamakin yadda Hansatu ta iya irin waɗannan abubuwan don bai taɓa jin haka daga gare ta ba. Don haka sai abin ya birge shi duk da yana jin zazzaɓin jikinsa, ya shiga mayarwa da Mai Yasin martani yana faɗin.

"Ke dai Hansatu wannan jarabar Allah Ya yaye miki, duk halin da mutum yake ciki ba za ki..."
Maganar Yaya Inu ta maƙale, ƙirjinsa ya buga da ƙarfi jin ya shafo gashin baki da gemu buzu-buzu, sai kuma ya kai hannu ya shafo kai ya ji wayam babu gashi sai ma wani sulɓi da ya ji kan yana yi kamar bayan sulba. Mai Yasin kusan mutuwar tsaye ya yi, Yaya Inu ya yi kukan kura ya ce.
"Ƙundun uba, jama'a kwarto a ɗakina zai haike mini."


A yi mini afuwa da rashin update kwana biyu, na shiga rububi amma yanzu na dawo free.

07062062624
Ummou Aslam Bint Adam
[01/01, 17:08] Ameera Adam: *GIDAN LIKITOCI*

©®AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITERS ASSO...*

Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.

*MARUBUCIYAR:*
MARWAN
JARIRI
ASEELA
BAƘAR DAULA
AN YA BAIWA CE?
ƊAN BA ƘARA...
SHU'UMAR MASARAUTA
DUBU JIKAR MAI CARBI
UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA
YAWON SALLAR HAJIYA IYA
ZAUJATU JINNUL-ASHIQ
SANADIN RAGON LAYYA

https://youtube.com/@ameerahaadam9365?si=xyR-pHK5EjkLjQnd

Don Allah duk wanda ya ci karo da wannan page ɗin, ya taimaka ya yi mana Subscribe a youtube channel ɗinmu.👆🏻👆🏻👆🏻

SHAFI NA TARA


A madadin Mai Yasin ya saki Yaya Inu ya yi ta kansa, sai ma ya sake ƙanƙame shi ta baya ya maƙale murya cikin ƙarfin hali ya ce.

"Haba Mai gida me kake son mayar da ni?"

Sororo Yaya Inu ya yi jin abin da Mai Yasin ya faɗa, sai ya fara zargin ko dai shi ne bai shafo daidai ba, ko kuma hannuwansa ne suke yi masa gizo. Don haka ya sake lalubo Mai Yasin ya ji ƙasunbarsa ta masa ƙabe-ƙabe, ya shafa gefen cinyarsa ya ji gajeren wando. A zafafe cikin zafin nama, ya kai masa naushi a fuska yana faɗin, "Mai gidan ubanka, ɗan iskan kwarto. Jama'a a kawo ɗauki." Ganin da gaske asirin Mai Yasin yana shirin tonuwa, ya sa shi fita a guje; shi ma Yaya Inu ya rufa masa baya. Sai da suka je tsakar gida Yaya Inu ya fisgo gajeren wandon Mai yasin, saboda babu riga a jikinsa idan ba haka ya yi ba zai iya kama shi har ya cim masa ba. Ganin dumu-dumu ya shiga hannu sai Mai Yasin ya zage iya ƙarfinsa ya barke wandon ya rabe biyu, ya fita a guje saboda tashin hankali a tsammaninsa sashen Inno ya nufa. Ba tare da ya ankara ba, ya haye katangar sashen Labaran ya dira. Cikin ɗakin ya faɗa a guje jikinsa har karkarwa yake yi, yana jin sa a kan katifa ya ja bargo ya rufa gumi yana keto masa.

Labaran ne ya fito daga zagayen wurin da suke tsugunno, sai da ya ajiye butar a ƙofar ɗaki sannan ya shiga ya buɗe randa ya sha ruwa, ya ƙarasa gefen gadon Rahinatu.
Murmushi ya saki a fili ganin mutum ya gangaro wurin kwanciyarsa, a tsammaninsa Rahinatu ce. Cike da shauƙin soyayya ya furta.
"Rahinatuwa kenan! Bari na gyara ki da kaina, don kada na katse miki bacci mai daɗi." Ya ƙarasa maganar cikin tattausan lafazi mai haɗe da soyayya, sannan ya saka hannu ya gyara hannun Mai Yasin da gumi ya gama wanke shi, ya yi mamaki sosai da ya ji hannun kamar ba na Rahina ba saboda ita mace ce mai ƙiba sosai. Da yake ɗakin babu haske sai ya bar abin a ransa ya raɓa ta gefe ya kwanta, sauke hannunsa da zai yi a gefen Rahinatu ya ji ana karkarwa ga gumi ya jiƙe shi. Ƙirjinsa ne ya buga da ƙarfi, a sanyaye ya ce.

"Rahinatu lafiya kuwa? Me yake damunki na ji kamar kina rawar ɗari "

Daga can gaban Mai Yasin, Rahina ta ɗago tana ɗan yanutsa fuska ta ce, "Baby lafiya kake magana da tsohon daren nan?"
Da sauri Labaran ya zaro ido waje, saboda Mai Yasin a tsakiyarsu yake. Labaran shiru ya yi ya sake saɗaɗa hannu ta cikin bargo ya shafo ƙafar Mai Yasin ya ji, don ya tabbatar da ba aljani ne ya jawo masa hari ba. Saboda a fitar da ya yi fitsari a tsammaninsa indai ba aljani ba, babu wanda zai shigo masa ba tare da ya ji ƙarar buɗe ƙofa.
Ƙafar Mai yasin ya shafo ya ji 'yan yatsu irin na shi saɓanin kofato da ya yi tsammani, sai ya kai hannu ya shafo kansa. Mai Yasin ya maƙale murya ya ce, "Masoyi kada ka yarda da ita ni ce ainihin matarka."

Ware ido Rahinatu ta yi don sai a lokacin ta lura da mutum a kusa da ita, jin furucin Mai Yasin ya sa Labaran ya shafo ƙasunbarsa, ya lalubo ƙirjinsa sai ya ji shi wayam.

"Kai la'ananne sai na kashe ka, garsamemen ƙato a gefen Rahinatuna! weeeeeeeeee huuuuuuu."
Labaran ya furta a haukace haɗe da yin gurnanin da ya razana Mai Yasin, hakan ya sa ya bankaɗe bargo ya fita da gudu Labaran ya rufa masa baya. Cikin shammata Mai Yasin ya juyo ya yi masa mahangurɓa a fuska, cikin tsananin jin azaba ya zube a wurin. Rahinatu ta fito tana ihu da kururuwa, a haka Mai Yasin ya samu ya cire sakata ya fice. Ya fita kenan Yaya Inu ya sako kai cikin sashen Labaran, ya shiga wuri-wuri hannunsa ɗauke da barandami da kokara.
A haukace Labaran ya fisge daga hannun Rahinatu ya cakumi wuyan Yaya Inu yana faɗin, "Wallahi yau ko ni ko kai a gidan nan, tun da ka nemi gwada mini kwartanci." Yana faɗin haka ya kai wa Yaya Inu naushi a baki, jin zafin haka ya sa Yaya Inu ya watsar da kokarar hannunsa ya falla wa Labaran mari, nan take suka shiga kiciniya Rahinatu ban da ihu babu abin da take yi. Kafin wani lokaci tuni iyalan Yaya Inu sun cika sashen Labaran, da ƙyar aka raba su kowannensu yana mayar da numfashi.

"Kai Labaran idan ka bari na riƙe ka wallahi sai na sumar da kai, shashasha wanda bai san ciwon kansa ba."
Yaya Inu ya yi furucin yana buga tsalle, kamar zai ƙwace daga hannun su Bashar. Labaran ya ji wani takaici ya lulluɓe shi, don gani yake Yaya Inu ya gama cin tuwo a kansa, saboda maganar da yake yi masa kamar an dake shi ne kuma aka hana shi kuka. Ya zabura a hassale ya ce.

"Ka dai yi asara Inusa, ka ajiye riɗa-riɗan mata amma kana bibiyar matan wasu, wallahi idan gabaɗaya mutanen garin nan gatanka ne, sai na ɗauki haƙƙin iyalina da ka shiga har cikin turakar sunna kake ƙoƙarin aikata fasadi."
Shiru kowa ya yi, cike da mamaki Hansatu ta ce.

"Kai Labaran kana nufin bayan sashenmu kai ma an shigo maka? Yanzu fa ihun Mai gida ne ya taso mu."
Yaya Inu ya ɗago gajeren wandon Mai Yasin ya ce, "Wannan shi ne abin da na samu daga jikin kwarton, kuma wallahi sai na kai wa Mai gobe da nisa ya saka shi a bala'in da bai taɓa zato ba."
Sai a lokacin jikin Labaran ya yi sanyi, kunyar yayansa ta kama shi, suna shirin watsewa suka jiyo ihun Inno a ɓangarenta. Kamar haɗin baki lokaci ɗaya suka bi sashenta sai dai ƙofar a rufe suka same ta, Yaya Inu ne ya kama katangar ya dire sannan ya buɗe wa ragowar ƙofa. A tsaye suka samu Inno butar hannunta ta tuntsire a bakin ƙofa ruwan cikinta ya zube, Inno tana ganin su Yaya Inu ta riƙe su jiki yana rawa ta ce.

"Inusa wani ya shigo gidan nan, don yanzu haka na fita fitsari na ga giftawarsa da gudu. Babban tashin hankalin ma, gamo na yi domin zir ɗinsa haka yake ko bante babu." Ba su saurari jin ta bakin Inno ba suka fita da gudu suna haske-haske, Mai Yasin ya yi tsumu-tsumu a ɗaki yana saka kayansa, ya yi lakur a kan katifa yana mayar da numfashi. Sai da suka yi binciken duniya amma ba su gan shi ba, suna cikin haka Mai Yasin ya fito yana tambayarsu kamar bai san abin da ya faruba. Labaran ne ya yi masa bayani, bayan ya gama Yaya Inu ya ce.

"Ai na yi mai wuyar tun da na samu tufafinsa, zan sa Mai gobe da nisa ya yi mini aiki mai zafi a kansa. Dama abin da yake buƙata takalmi ko wani abu da aka samu daga jikin ɓarawo ko kwarto, wallahi daga wannan karon ba zai sake haurewa gidan wani ba."

Jin haka ya sa cikin Mai Yasin ya kaɗa, wani zazzafan gumi ya yanko masa. Ya ƙarasa gaban Yaya Inu ya riƙo hannunsa da ke karkarwa ya ce, "A'a Inusa ka bar mini komai a hannuna, ka san dai kamar yadda na faɗa muku zafin aikina ne ya sa ake kira na da Mai Yasin. To ni zan..."
Kallon da Yaya Inu ya shiga wurga masa ne ya sa shi katse kalamansa, don yadda ya ga yana kallonsa har sai da ya sa shi tsarguwa.
"Ka bar mini komai a hannuna, ni na san irin shige da ficen da nake yi a wurin malamai, don haka zan ji da shi."
Jiki a sanyaye kamar zakaran da ya shuri wuƙa, Mai Yasin ya ja jiki gefe. Yaya Inu ya fice yana muzurai, babu jimawa kowa ya watse.

Ganin duk irin gudun da Mai gari yake fallawa su Mahmud ba su daina bin sa ba, ya sa shi ɓarkewa da kuka yana gudu yana waigensu. Ba shi ya tsaya ba sai da ya ƙarasa tukubar tsiren Mai daban-daban, yana shiga rumfar a guje ya yi bayan su Haladu da ke zaune a kan benci. Zumbur! Suka miƙe, cikin damuwa Sallau ya ce.
"Subhanallah! Ranka shi daɗe lafiya kuwa? Me yake faruwa daga kai sai gajeren wando?" Kafin Mai gari ya bayar da amsa su Mahmud suka ƙarasa cikin runfar, ganinsu ya sa bakin Mai gari ya shiga karkarwa hannu yana rawa ya nuna su ya ce.

"Su... ne, wallahi ba... mutane ba ne. Ku taimaka..."

Bai ƙarasa maganar ba ya yanke jiki ya faɗi, cikin su Mahmud ya sake kaɗawa don Mudassir tuni ya fara hawaye, ya dubi Mahmud ya ce.
"Mahmud ka janyo mana masifa muna zaune ƙalau."
Sai ya sake ɓarkewa da kuka, hawayen da Mahmud yake riƙewa ne ya ɓalle haɗe da wanke fuskarsa lokaci ɗaya. Sun juya za su fita da sauri Mai daban-daban ya danƙo wuyan rigarsu yana faɗin.
"Billahillazi la'ilaha'illahuwa sai kun tsallaka mai gari, kai babu wanda fa zai bar wurin har sai mai gari ya dawo hayyacinsa." Su Mahmud suka yi tsilli-tsilli ƙirjinsu yana bugawa.
"Wallahi a ɗaure su har sai ranka shi daɗe ya dawo hayyacinsa, idan ba haka ba sai sun tsallaka shi, dubi idon munafuka sun yi kama da baƙaƙen mayu. Wai ma ku su waye a garin nan!" Daga ƙarshe Sallau ya wurga musu tambaya.
Daga Mahmud har Mudassir aka rasa mai magana, ba su yi aune ba Mai daban-daban ya fiszo wata ƙatuwar igiyar da yake ɗaure damin itace, shi da Haladu suka shiga ɗaure Mahmud da Mudassir.

"Wallahi mu baƙi

40 / 46