Dahuwar Kawo Book Compelet Ameera Adam

Author :  Ameera Adam Category :  Read Hausa Novels

Chapter   24 / 46

69K to 72K   out of 137.8K words

smau damar kiransa ba.

Yana nan zaune ya ji flashing ɗinta, a fili ya saki ajiyar zuciya. Hannunsa har rawa yake ya latsa layin nata, tana ɗaga wa ya ji ta fashe masa da wani irin kukan kissa. Wani abu ya ji yana zarga masa wanda ya kashe masa ilahirin jijiyoyin jikinsa. Sai da ya yi ƙarfim hali sannan ya iya fisgar maganar bakinsa.

"Wannan shagwaɓar taba gigita ni my Moon, idan ba kya son hana ni bacci a ɗan daga ta da kukan nan haka."

Daga can ɓangaren Maimuna ta sake yin wata shasshekw wace ta sake birkita shi, murya can ƙasa kamar wacce take waya da mijinta ta ce, "Ina kukan farinciki ne my J. Haƙiƙa ka faranta mini rai domɗn wannam wayar ba ƙaramin tsada gare ta ba."
Murmushi ya yi mata ya ce, "Ko nawa zan iya ɓatar mini Moon, fata da burina kawai ki mallaka mini kanki."

"Idan hat ni ce kamar ka samu J, kada ma ka sake wasu-wasi a kan soyayya ta."
Har Jafar zai yi magana Maimuna ta katae shi a shagwaɓe.
"Ɗazu matarka ta ci mutumcina bayan ta zo ɗiban gawayi, a gaskiya raina ya ɓaci domin an daɗe ba a ci zarafi kamar na yau ba. Duk da ba cikin faɗa ta yi mini magaanar ba, amma a wasan dare ta ƙare mini cin mutumci. Har takw yi mini ƙafafa a kan ita amfani take yi da gas."
Sai kuwa Maimuna ta rushe da kuka, kukanta yake ji har cikin ransa. Don ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, cikin rarrashi ya ce, "Ya isa haka baby Moon. Wallahi tun ranar da na fara ganinki ba ki kalar amfani da gawayi ba. In Shaa Allaha na san yadda za a yi na saya muki gas ki daina amfani da gawayi. Ita kuma ki bar ni da ita na rantse miki da Allah daga gobe ta daina amfani da gas gabaɗaya. A yanzu ma don dai dare ya yi, da a daren nan zan siyo masa kurfoti da buhun gawayi."


Ummou Aslam Bint Adam
+2347062062624
[13/02, 21:16] Ameera Adam: *NAUSHIN WUTA*

©®AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

GARGAƊI: Ban amince a sarrafa mini littafi da kowacce siga, ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.

SADAUKARWA
Tun daga farko har ƙarshe, na sadaukar da wannan littafin ga duk mahaifiyar da ta kasance uwa; ko mai burin zama uwa a nan gaba. Allah Ya saka wa iyayenmu maza da mata da gidan Aljanna Amin.

SHAFI NA BAKWAI

UWAR GIDA, AMARYA HAR MA DA MAI GIDA KU MATSO KUSA.🥳🥳🥳🥳🥳🥳🥳

Ina kuke matan habiby da Habibin kansa ku matso kusa ga kaya nagani na fada wanda habiby xai saka ki kasa gane shi 😍shin kina neman inda xakisai ma mijinki kyauta ta bazata ? Maza hanxarto musaka labule jallabiya ta gani ta fada da hula mai musulmin kyau wanda xai burge oga 😍 akan farashi daidai da aljihunki kundaisan kyauta tana kara soyayya

Kaima habiby ban barka abaya ba hanxarto gurinmu ka mallaki hula da jallabiya qualitatives via +234 816 916 8731

***

Wani irin farinciki ne ya lulluɓe zuciyar Maimuna, saboda dama ba a ranar Maman Nana ta saba zuwa tana yi mata fariya, tana baje mata jin daɗin da Jafar yake yi mata ba. Wani abin ma sai ta lura kamar da gayya Maman Nanan take yi, saboda mijinta duk ya fi ragowar mazajen layin rufin asiri. Wannan ne dalilin da ya sa Maimuna ta ci alwashin sai ta tarwatsa farincikinta, tun da ita ba ta samu kwatankwacin abin da Maman Nana take samu a wurin miji ba.

"Na ji kin yi shiru ko hukuncin da na ɗauka bai yi miki ba?"

Jafar ya furta jin Maimuna ta yi shiru, Maimuna ta sauke ajiyar zuciya ta ce. "Hakan ya yi Baby J, to amma ta ya ya zan mallaki gas ɗin? Ni dai ba sana'a nake yi ba ballantana na cewa mutumin nan saya na yi."

"Wannan mai sauƙi ne Moon, zan san yadda zan ɓullowa lamarin."
Hirar soyayya suka cigaba da yi tamkar ma'auratan da suke nesa da juna, kowanne yana cike da kewa da begen ɗan uwansa. Suna gab da yin sallama Jafar ya ce, "Wayar nan da na aiko ba ta buƙatar caji, na saka mata caji ɗazu. Abin da ya rage kawai don Allah ki ɗaukar mini hotunanki."

Maimuna ta ce, "Sai zuwa gobe idan Nazir ya fita, amma ka ɓoye su ta yadda matarka ko wani ba zai gani ba."
Murmushi Jafar ya yi ya ce, "Kada ki damu akwai folder da nake ɓoye hotuna, a nan zan ɓoye naki."
Yana faɗin haka daga gefensa ya ji Nazir ya yi masa sallama yana daga kan mashin, duk da ya san Nazir ba zai taɓa fahimtar da wacce yake magana ba. Amma sai da gabansa ya faɗi, ya cire wayar daga kunnensa ya ce.

"Ale Nazir barka da shigowa."

Nazir ya ɗan rage gudun mashin ɗinsa ya ce, "Barka dai Alhaji Jafar, ka na nan a bayan fage kana waya ko? Ai sai na aika na faɗa mata." Nazir ya yi furucin cikin barkwanci.

"Tuba nake kada ka sa a rufe mini ƙofa." Jafar ya furta yana kama kunnensa, dariya Nazir ya yi ya wuce gida. Ganin ya tafi ya sa Jafar ya ja dogon tsaki yana mayar da wayar kunne ya ce, "Ina tsaka da farinciki wannan mutumin zai datse mini, don Allah Moon ki rage ba shi kula a turaka. Wallahi haka kawai kishinsa yake nuƙurƙusata."
Maimuna da ita kanta haushin Nazir ya kama ta ce, "Ai yau duk bala'insa babu ma abin da zai haɗa mu, dama na kwana biyu ina juya masa baya."
Kamar ba za su rabu ba haka suka yi sallama.
Maimuna tana gama wayar ta yi saurin mayar da ita wurin da take, ta yi sauri ta haye gado ta kwanta ta rufe ido. A kan kunnenta Nazir ya shiga gidan, ya ɗan jima a falo sannan ya tashi ya shiga ɗakin.

"Maimuna! Maimuna!"

Ya furta yana bubbuga filonta, yamutsa fuska ta fara yi tana miƙa kamar wacce ta jima tana bacci.
"Sannu da zuwa."
Ta furta masa tana sakin hammar ƙarya.
"Yawwa sannu ya gida?".

A hankali ta zuro ƙafafuwan ƙasa, ta jinginta kanta da fuskar gadon ta ce. "Lafiya ƙalau."

Ya yi mamakin a 'yan kwanakin nan da Maimuna ba ta yi masa ƙorafi, domin kusan kullum idan ya dawo gida sai ta yi masa ƙorafi a kan kai wa daren da yake yi a waje. Miƙewa ta yi ta fito falo, Nazir ya rufa mata baya. Kayan abincinsa ta ɗebo ta ajiye masa har ta miƙe za ta koma ɗaki ya riƙo hannunta.

"Maimuna kwana biyu na ga duk kin sauya, me yake damunki ne?"

Fuska babu walwala ta ce, "Me ka gani?"

"Na ga kwana biyu kamar ba ki damu da ni ba, kuma ni dai na san ba wani abu na yi miki ba."
Nazir ya furta a sanyaye.
"A'a babu abin da yake damuna kawai dai baccin da na tashi ne!"

"Ba haka ba ne Maimuna, a 'yan kwanakin nan ko ƙarfe nawa na dare zan kai ba za ki kira ni ba, idan na dawo kuma ba za ki tambaye ni dalilin kai wa daren da na yi ba. A yanzu ko zan kwana ina chatting uffan ba za ki ce mini ba, ni sai na ga kamar haushina kike ji."

"A'a ni babu wani haushinka da nake ji, ai kowa rayuwar da ya ga dama ita yake yi. Tun da na lura kulawar da nake ba ka ce ta sa kake yi mini wasu abubuwan, don haka na bar wahalar da kaina."
Maimuna ta sake yin maganar tana shirin tafiya.

"Zauna mana, yau fa hira nake son mu yi. To yanzu dai ki yi haƙuri, ga biskit da chocolate nan na taho muku da shi ke da yara."

Ta fahimci sarai hirar da yake nufi, domin dama ba ta cika amfani a wurin Nazir ba sai yana buƙatarta. Sau tari idan hakan ta taso babu wata kulawa da nuna soyayya haka kawai zai afka mata, ta kawar da kai gefe ta ce.
"Ai kuwa sai dai ka yi haƙuri zuwa gobe kaina matsanancin ciwo yake, shi ya sa ma na sha magani na kwanta ɗazu." Tana gama maganar ta janye hannunta ta wuce ɗaki, kamar sakarai haka yake bin Maimuna da kallon mamaki. Ya san dai Maimuna ba shiga gidan kowa take ba, ballanta ya ce maƙota ne suke zuga ta. Kuma ya santa da ƙorafi matuƙar ya ɓata mata rai ko bai san laifin ba za ta fito ta sanar da shi. Da sauri ya tashi ya bi ta ɗakin a lokacin har ta ja bargo ta rufa, ransa ya sake ɓaci amma sai ya saita nutsuwarsa ya ce.
"Magana nake yi miki fa Maimuna kika shigo ɗaki."
Tana daga kwance ta ɗago ta ce, "Ni ma ai amsa na ba ka Abban Asiya."
Ƙwafa ya yi ya juya ya fita, ya zauna ya cigaba da cin abincinsa. Sai da ya gama uzurinsa sannan ya shiga ɗakin ya kwanta a gefenta, juyi yake shi kaɗai yana mamakin sauyin halinta. Don haka ya so danne buƙatarsa amma sai ya gagara, hannu ya kai ta janyo ta kamar tana jira ta ture shi tana faɗin.
"Haba Abban Asiya, wai me kake yi haka na ce maka ban da lafiya fa."

"Kin sauya Maimuna, Me ya sa kike son horar da ni ne? Yau rabona da ke kwana nawa, rannan kin ce mini zazzaɓi kike. Shekaran jiya kin ce ciwon baya, yanzu kuma kin ce mini kanki yana ciwo. Idan kina ganin ba za ki iya ba ni haƙƙina ba sai na ƙara aure." Nazir ya furta cike da barazana saboda ya san Maimuna tana da kishi, amma cikin halin ko in kula ya ji Maimuna ta ɗago ta ce.

"Sai me don ka yi aure Naziru? A kaina za ta zauna? Ko ni zan ciyar da ita, ruwanka ne ka ƙara aure kuma ruwnaka ne ka bari na samu lafiya. Idan kuma ƙarin auren ka ga shi ya fi maka mafita wallahi ni ko a gefen takalmina."

Tsoro ne ya kama shi saboda ya ji an ce idan mace ba ta ba ka kulawa, ba ta nuna kishi a kanka kawai zama take yi da kai ba don soyayya ba. Da a ce a shekarun ba ya ne ba zai yi mamakin jin haka daga gare ta ba, amma yanzu da shekarun aurensu suka tura ya lura duk ta zubar da makamanta.

"Au haka kika ce?"

Nazir ya faɗa a zafafe.
"Eh haka na faɗa, tun da kishiya ba a kaina aka fara ba." Tana gama faɗa ta sake gyara kwanciyarta.

Cike da kewar Maimuna Jafar ya nufi gida, a lokacin da ya shiga ƙarfe goma sha ɗaya da rabi. A zaune tunkur ya samu Maman Nana da alama jiransa take yi, ya shiga ɗakin kamar bai ganta ya fara rage kayan jikinsa.

"Abban Nana wato fitar da ka yi gidan su budurwarka ka tafi ko?"
Bai waiwayo wurinta ba ya ce, "In ji wa?"

"Sai an faɗa mini?"

"To tunaninki bai harsaso miki daidai ba." Shi ma ya faɗa fuska a haɗe. Hakan kuwa ya sake harzuƙa ta, rai a ɓace ta ce.
"Wai Abban Nana me kake nufi ne? Ka bi ka sauya mini lokaci ɗaya na rasa gane kanka, da idan ka shigo gidan bayan sallar Isha'i ba ka sake fita sai washegari. Amma yanzu kana gama cin abinci sai ka fice ba za ka dawo ba sai dare, na gaji fa wallahi na gaji da irin cin kashin da kake yi mini."

"To idan ba za ki iya ba sai ki nemawar kanki mafita."

Ta riski miyagun kalamansa a cikin kunnuwanta, ƙirjinta ya buga da ƙarfi. Cike da tsoro ta dube shi amma sai ta nuna masa ba ta fahimci abin da yake nufi ba ta ce.

"Me kake nufi?"

"Ina nufin idan ba za ki iya zama da ni da ki kama gabanki."

Wani irin dum! Ta ji kamar an kwaɗa mata guduma, da sauri ta runtse idonta ta buɗe su a kansa. Ta taka gabansa muryarta tana rawa ta ce, "Abin da za ka ce mini kenan Abban Nana? Dama ka gaji da ni ban sani ba?"

"Ko ban gaji da ke ba wulaƙancin da kika tarko ne ba zan ɗauka ba, na lura samu ma yana saka mace ta yi iskancin abin da take so. Amma babu damuwa tun da irin zaman da kike so mu yi shi kenan."

Shiru ta yi kamar ruwa ya cinye ta, ta shiga nazari daga safiyar ranar zuwa dawowarsa ko za ta iya tuna laifin da ta yi masa amma ba ta iya tunawa ba.

"Don Allah ka faɗa mini laifin da na yi maka Abban Nana?"

Bai tanka mata ba ya saki tsaki ya ɗauki fulo ya koma kan kujera ya kwanta. Abin duniya ne ya haɗe wa Maman Nana, sai ta ji ya fara ba ta tsoro domin lamarin nasa ƙara yin gaba yake yi. Don haka ta shiga alla-alla gari ya waye ta leƙa gidan Maimuna ko ta ba ta shawarwarin abin da za ta yi.

Washegari

Tun da Jafar ya yi sallar Asuba bai koma ba, gari yana yin haske ya shiga cikin kitchen ya ɗauke tukunyar cilinder gas ya fice da ita. Da yake Maman Nana ba ta tashi da wuri ba, saboda a daren bacci bai ɗauke ta da wuri ba ko kaɗan ba ta san wainar da ake toyawa ba. Sai da ta ji alamun buɗe gate ta tashi ta fito, a tsammaninta Jafar fita ya yi kasuwa.
Banɗaki ta shiga bayan ta fito ta shiga kitchen za ta shirya wa su Nana abin breakfast da na makatanta. Amma sai ta ga wayam babu clinder, ba ta kawo komai a kanta ba; sai ta yi tsammanin ko ƙaro musu gas zai yi saboda idan ya ga ya kusa ƙarewa yana ɗauka ya ƙaro mata.
Tana daga ƙofar kitchen ta hango shi yana kokawar shigowa da ƙaton buhun gawayi, sai da ya ƙarasa ya jingine shi sannan ya sake fita gate ya sauke mirgino buhu na biyu. Maman Nana tana tsaye ya gama dire buhunnan gawayin har guda biyar, sannan ya ɗauko kurfoti ya dire a gabanta. Fuska a haɗe ya ce, "Daga yau ga abin da za ki dinga girki da shi, gas ya sake tsada ba zan iya sayensa ba. Cilnder ma na sayar wa mai shagon da nake sako mana gas, sai a ci gaba da malejin rayuwa tun da komai tsada yake sake yi." Jafar yana gama faɗar haka ya shige ɗaki.

Kabir kwance ya yi a kan gado, yana jin haushin kansa a kan abin da ya aikata. Fushin Fauziya ya fi komai ɗaga masa hankali, don Fauziya mace ce mai haƙuri da sauƙin kai. Amma idan ta yi fushi ba ta iya zuciya ba, juye-juye ya fara yi yana hangen ta da take kwance idonta biyu tana hawaye. A hankali ya tashi zaune ya tsugunna a gefenta murya a sanyaye ya ce.

"Fauziya! Don Allah ki tashi mu yi magana, ba na son ki saka kanki a cikin wani hali saboda yanayin da kike ciki."

Ɗagowa ta yi ta dube shi, tana jin sautin muryar martanin batsar da yake mayarwa da Hafse a cikin kunnuwanta. Zuciyarta ta shiga zafi, wani abu ya tokare ƙirjinta. A hankali ta fara jin mararta tana tsira mata, ta cije bakinsa tana girgiza kai.

"Don Allah ki yafe mini..."

"Idan ka sake yi mini magana zan fice daga gidan nan na ba ka wuri."
Ta katse shi da wani irin sauti, kamar sabon munafiki haka Kabir ya ja jiki yana sunne kai ƙasa ya koma kan gadon ya zauna.
A cikin wannan daren daga shi har Fauziya bacci rabi da rabi suka yi, sai bayan Asuba ta samu bacci mai hauyi ya yi awon gaba da ita.
Tun da Kabir ya tashi bai koma ba, saboda ya san ya yi wa Fauziya laifi a hankali ya dinga aiki don kada ya tashe ta. Shi ya dafa wa yara abinci, ya shirya su suka tafi makaranta. Sannan ya shiga ɗakin ya share mata, kwanukan wanke-wanken kuma ya ajiye a bakin rariya zai wanke mata. Lawisa tana sanye da hijabi tana girki a bakin ƙofarta ta hango shi ya tsugunna zai yi wanke-wanke, miƙewa ta yi ta ƙarasa wurin ta ce, "Baban Na'ima ka bari zan wanke mata, ko jikin Maman Na'iman ne." Kabiru ya ɗan sosa kai ya ce, "Eh ta tashi ba ta jin daɗi ne, shi ne ta ɗan kwanta zan rage mata aikin."

"Subhanallah! Allah Ya raba lafiya, bari na ƙarasa girki sai na haɗa na wanke da nawa."
Godiya ya yi mata sannan ya koma ɗakin, tun da ya shiga yana son ya tambaye ta abin da za zai girka musu da rana yana shakkar tashinta da ɓacin ranta. Tukunyarta ya buɗe ya ga akwai sauran miya, sai kawai ya ɗora taliya ya dafa musu. Kafin Fauziya ta tashi tuni Kabir ya gama komai, hatta turaren wutar da take sakawa ya saka musu. Ya shiga ɗakin ya same ta a bakin gado a zaune ta tashi, fuskarta ta sauya sosai daga jiya zuwa yau duk ta rame.

"Ga ruwan wanka zan sirka miki sai ki yi wanka."

Kabir ya furta yana satar kallonta, ko kallonsa ba ta yi ba har ya sake maimaita mata.
"Don Allah ka matsa daga gabana Kabir." Da sauri ya fice daga ɗakin, ya

24 / 46