Dahuwar Kawo Book Compelet Ameera Adam

Author :  Ameera Adam Category :  Read Hausa Novels

Chapter   3 / 46

6K to 9K   out of 137.8K words

suke karkaɗe ƙafafuwansu su tafi. Gabaɗaya Bilkisu kallon munafukai take yi wa dangin Hafiz, don haka su ma suka janye jikinsu daga wurinta.
Duk wani shige da fice da Bilkisu za ta yi don ta san yarinyar da Hafiz ya aura ta yi, sai dai har lokacin ba ta samu ba. Watarana da daddare, kimanin biyun dare. Ta jango wayar Hafiz, ganin password a jiki ya sa jikinta ya yi sanyi, wani tunani ne ya faɗo mata. Da sauri ta shiga gwada sunayen yaranta bai yi ba, sai ta gwada sunansa ta samu wayar ya buɗe. Whatsapp ɗinsa ta shiga, a nan ta fara cin karo da lambar Amina da irin zafafan kalaman soyayyar da suke yi wa junansu.
Da farko ɗaukar lambar ta yi za ta kira ta zagi Amina, sai kuma wani tunani ya faɗo mata. Cikin sauri hannunta yana rawa ta rubuta.

_Ni Hafiz Adam, na saki Amina saki ɗaya, na sake ta saki biyu na sake ta har saki uku. Sakamakon saɓanin da nake samu da matata saboda na aure ki, domin ba zan iya ɓata wa matata rai ba._

Bayan saƙon ya tafi sai ta goge saƙon daga kan wayar, sannan ta ajiye masa wayar a gefensa ta koma ta kwanta tana jin zuciyarta fes.



Ummou Aslam Bint Adam🌚
07062062624
[17/06, 18:06] Ameera Adam: *DAHUWAR ƘAHO*

©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Gargaɗi: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ko a karanta shi a kafar sadarwa, ko ɗorawa a wata manhaja ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.

Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba, idan ya yi daidai da yanayin labarinki/ka arashi ne.

https://chat.whatsapp.com/IAZVt2Pz4LvIcklCxSTHwo

SHAFI NA UKU

Lokacin da Hafiz ya tashi zai yi sallar asuba misscall ɗin Amina ya gani rubutu, yake ya ji masallaci sun shiga da sauri ya zura wayar a aljihu ya nufi masallacin saboda tuni ya yi alwala. Ana idar da sallah ya fito daga masallacin, ya ciro wayar a nan ya sake cin karo da wani kiran nata. Ƙirjinsa ne ya buga da ƙarfi, hannu yana rawa ya ɗauki wayar yana faɗin.

"Salamu alaikum, Amina."

Kuka ya ji ta fashe da shi, hakan ya sake ɗaga hankalinsa. Jikinsa yana rawa ya sake cewa, "Amina me yake faruwa a gidan ne? Lafiya kike kuka?" Daga can ɓangaren Amina ta sauke ajiyar zuciya murya a dashe saboda kukan da ta sha ta ce.
"Tambayata ma kake yi Hafiz? Tambaya kake yi me ya faru? Dama ka so cin mutumcina ne shi ya sa ka zo gidanmu neman aurena?" Da mamaki ya ɗago wayar yana bin lambar da kallo don sake tabbatar da wacce take magana, cikin rashin fahimtar zancanta ya ce.

"Amina wai me kike faɗa ne? Kin san wa kika kira kuwa?"

"Kana nufin na fara hauka ne Hafiz? Ko ka ɗauka ina shaye-shaye ne?" Ita ma ta faɗa a ɗan fusace. Shiru ya yi yana nazari, don ya san Amina sarai mace ce mai haƙuri. Tun da suke tare ba ta taɓa faɗa masa makamantan irin maganganun nan ba. Gwaron numfashi ya sauke cikin tausasa murya ya ce, "Don Allah Amina ki yi mini bayani ban san me yake faruwa ba."
Wani takaicin ne ya sake rufe Amina, cikin gatse ta ce.
"Kana nufin har ka manta sakin wulaƙancin da ka yi mini, saboda matarka ta fi ni a wurinka don kuna samun saɓani shi ne za ka sake ni? AlhamduLillah tun da har na fahimci matarka ta fi ƙarfinka, na gode ka aiko gidanmu a karɓar maka sadakinka." Daga haka Amina ta katse wayar.

Wani irin gumi ne ya lulluɓe Hafiz, da sauri ya jingina da bango sakamakon jin da ya yi juwa tana yunƙurin taɗe ƙafafuwansa.
"Innalillahi wa inna'ilahir raji'un." Ya furta a fili, sannan ya zura wayarsa a aljihu. Da sauri ya nufi gida, ya shiga kiciniyar fito da mashin ɗinsa waje. Yana rufe gidan ya hau mashin ɗinsa, kai tsaye ya wuce unguwarsu Amina.

Yana zuwa ƙofar gidan ya ciro wayarsa ya yi mata kiran duniya ta ƙi ɗauka, ƙwanƙwasa ƙofar gidan ya fara yi a rikice. Don kallo ɗaya za ka yi masa ka fahimci yana cikin damuwa. Mahaifinta ne ya buɗe ƙofar ya fito, cikin girmamawa Hafiz ya tsugunna ya gaida shi sai kuma ya yi shiru ya ma rasa ta ina zai fara yin magana.

"Hafiz dama na so kiranka da kaina zuwa an jima. Amma na ji daɗi da Allah Ya kawo ka yanzu."

Da sauri Hafiz ya ɗago ya ce. "Baba lafiya kuwa? Dama... dama na ji Amina tana ta wasu maganganu." Mamaki ne ya kama Baba, sai ya ce.
"Shigo ɗakina, wannan ba maganar tsaiwa ba ce."

Baba ya furta yana shiga ciki, kamar zakaran da ya bi ta mahauta haka Hafiz ya bi bayan Baba jiki a sanyaye. Yana nan zaune a ɗaki Amina da Baba suka yi sallama suka shiga, wayar Amina ya karɓa ya nuna masa ya ce.
"Da asubar nan Amina ta nuna mini saƙon da ka turo mata cikin dare." Hafiz yana gama karanta saƙon ya ce.

"Wallahi Baba ban san yadda aka yi ba, wallahi ba ni na rubuto mata wannan saƙon ba. Tun da ko a daren jiya lafiya ƙalau muka gama waya da ita." Hafiz ya yi jim, ya ɗago da sauri ya ce.
"Sai dai idan matata ce, babu tantama wallahi sai dai idan ita ce Baba." Shiru Baba ya yi yana nazari, ya sauke ajiyar zuciya ya ce.

"To a gaskiya idan har haka ne sai ka tashi tsaye Hafiz, don ba na son duk wani abu da zai sa a dinga tashin hankali. Haka kuma wannan maganar ba za mu bar ta daga mu sai kai ba, dole ne ka kirawo manyanka a yi magana. Ita ma ya zama wajibi ka tsawatar mata, ka kuma kiyaye haƙoƙinta. Don za ka yi aure ba shi zai sa ka wulaƙanta matarka ba, ko ka dinga cin fuskarta kana cin zarafinta. Ka ji tsoron Allah Hafiz, wallahi idan ka cuci 'yar mutane Allah ba zai bar ka ba." Cikin girmamawa Hafiz ya russuna ya ce.

"In Shaa Allahu Baba."

Miƙewa Baba ya yi ya fita, har Amina za ta fita cikin sauri Hafiz ya ƙarasa ya riƙo ta. Rungumo ta ya yi jikinsa ya haɗa ta da bango ya ce.

"Kina tunanin akwai ranar da zan iya rabuwa da ke ne?"

A ɗan shagwaɓe Amina ta ce, "Na sani tun da tsoron matarka kake ji." Sunkuyawa ya yi ya sakarwa bakinta kiss ya ce, "Haka kike gani Meena, amma babu wani tsoro. Kin san duk macen da za a ƙara wa abokiyar zama dole a lallaɓa ta, musamman Bilkisu da take da kishi." Janye jikinta za ta yi ya sake matse ta ya ce.
"Me ya sa kike guduna ne?"

"To ni kada wani ya ganmu a haka." Ta ba shi amsa a sanyaye, zuba mata ido ya yi yana jin sonta na fisgarsa. Cikin wani irin yanayi ya ce, "Ai ba wamda zai shigo tun da kowa ya san ke matata ce, ba ki ga ma Baba ya ba mu wuri ba."
Zaro ido ta yi tana rufe baki ta ce, "To wallahi ni tafiya zan yi, wato duk kallon haka suke yi mini?"

Gyaɗa mata kai ya yi ya tallafo fuskarsa da hannu biyu ya ce, "Ina ƙaunarki Meena, na yi mamaki da har kika yarda zan iya rabuwa da ke." Tura baki gaba ya ta yi cikin jin nauyinsa, Hafiz lumshe ido ya ce.

"In Shaa Allah nan da sati biyu za a kawo kaya, sai a yi wunin biki a wuce wurin don haƙurina ya fara ƙarewa." Sunkuyar da kai ƙasa ta yi cikin jin kunya, ya sunkuya saitin kunnenta ya yi mata raɗa a kunne. Da sauri ta ɗago tana rufe ido cikin jin kunya ta ce.
"Allah Ya shirye ka, ni wallahi ba haka nake ba. Don Allah babu abin da ya dame ni."

"Ai shi ya sa na ga ba kya hana ni idan ina..."
Da sauri Amina ta saka hannu ta rufe masa baki, sai kuma ta ce.
"Ka zo ka tafi ka bar Madam tun da farar safiya." Cikin kwaikwayon muryarta ya ce.

"To duk ba ita ta ja komai ba."
Dariya Amina ta yi ta ce, "Allah Ya shirya ka Hubby."
Har ƙofar gida Amina ta raka shi tana jin soyayyar Hafiz a cikin ranta. Duk da ta ji zafin abin da Bilkisu ta yi, ta wani ɓangaren tana yi mata uzuri, saboda ba kowacce mace ce take danne zuciyarta ba idan za a yi mata kishiya.

Hafiz yana zuwa gida ya samu Bilkisu tana yi wa yara shirin makaranta, kallo ɗaya ta yi masa ta ɗauke kanta. Haka shi ma bai kula ta ba ya zauna har yara suka gama cin abinci, ya ɗauke su ya kai su makaranta. Lokacin da ya koma tana kwance a kan gado, a gefenta ya zauna ya ce.
"Bilkisu ki tashi za mu yi magana da ke."
Ɗagowa ta yi ta kalle shi a sheƙe ta ce.

"Faɗi maganarka ai kunne ne yake ji."

Ajiyar zuciya ya sauke ya ce, "Bilkisu kin san ina sonki ina ƙaunarki, kuma kin san babu macen da zan kawo na bari ta raina ki, ko ta ci mutumcinki. Kin san ba zan ɗauki haka ba, duk abin da kike wa 'yan uwana ina sane, amma duk da haka ban bari ɗaya daga cikin ƙannena sun raina ki..."

"Don Allah idan ba wata magana mai muhimmanci za ka faɗa mini ba ka ƙyale ni." Bilkisu ta faɗa rai a ɓace. Girgiza kai ya yi yana danne ɓacin ransa ya ce.

"Muhimmancinta ne ya sa na same ki da maganar. Bilkisu yanzu ba ki ji kunyar saƙon da kika turawa Amina a matsayin ni ba ne? Ko kin ɗauka aure wasan yara ne da za ki yi wannan shirmen? Don Allah ki kama girmanki Bilkisu, ina respecting ɗinki a wurin Amina. Don haka ita ma ko da wasa, ba ta taɓa kawo maganar wargi a kanki ba, ina girmamaki fiye da yadda kike tsammani. Ki girmama kanki ta yadda ba za ki bada ƙofar da yarinyar nan za ta raina ki ba, ni idan kin yi mini zan iya shanyewa. Amma kin san ba lalle ne ita idan kin yi mata wani abin ta ɗaga miki ƙafa ba..."

"To duk abin da za ka saka ta yi mana, wallahi duk shegiyar da ta kawo mini raini sai na yi mata dakan sakwara." Bilkisu ta faɗa tana tashi zaune. A ɗan zafafe Hafiz ya ce, "Kada ki sake zagar mini mata."
Bilkisu ji ta yi kamar ya watsa mata ruwan zafi, don haka a zafefe ta ce.

"Na zaga idan ka ga dama ka rama mata, 'yan iskan 'yan mata ba za su nemi mijinsu su aura ba sai mace ta raini mijinta su zo su aure suna tunƙahon mijinsu ne." Jin ba zai iya ɗaukar maganganun da Bilkisu take faɗa ba, ya sa shi ficewa daga ɗakin ya nufi ɗakin yaran ya kwanta a can.

Kamar yadda Hafiz ya faɗa cikin ƙasa da sati biyu ya ƙarasa haɗa duk wani abu da ake buƙata na lefe, juma'a tana zuwa aka kai kaya gidansu Amina. A nan su kuma iyayenta suka tsayar da ranar juma'a mai zuwa, a matsayin ranar da za a yi wuni da kai amarya. Hafiz ya yi ƙoƙari sosai, akwati biyar ya yi mata daidai rufin asirinsa. Ya ba ta kuɗin kamu da gyaran jiki don shi ba shi da ra'ayin zuwa wurin kamu. Haka ita ma Bilkisu akwati guda ya cika mata da kaya, dangin atamfofi da lesuna da kayan shafe-shafe har da kayan bacci. Yaran kuma ya saya musu sababbin ƙananan kaya kala ɗaiɗai da shadda kala bibbiyu.
A cikin satin Hafiz ya sa aka fitar da kujerun Bilkisu aka kai wurin kafinta ya gyara mata su, aka saka sababbin sosuna da sababbin yadi suka dawo kamar sababbi. Sai labulaye da ya saya mata masu yanayi da kujerunta duk don ya faranta mata. Sannan ya ba ta dubu hamsim ya ce ta yi duk wani gyara da za ta yi dangin kitso da ƙunshi. Ana saura kwana biyu Amina za ta tare ya kira masu fenti suka yi wa gidan fenti, sai dai jere ne ya hana 'yan uwan Amina su yi a ranar saboda yana tsoron kada Bilkisu ta aikata abin da za ta kunya shi a wurinsu.

Ranar juma'a tun da sassafe 'yan uwan Amina suka je gidan Hafiz yin jere, kallo ɗaya suka yi wa Bilkisu suka fahimci zai yi wuya a yi zaman lafiya da ita a cikin gida. Don haka suka dinga kaffa-kaffa, gudun kada ta ce sun yi mata wani abin. Saboda sun ji sai faɗa take yi wa yara da habaici, kuma abu kaɗan yaro zai yi mata sai su ji ta rufe shi da duka. Kusan azahar suna ta aiki sai ga Fadila ƙanwar Hafiz, ta yi sallama cikin gidan hannunta ɗauke da ƙatuwar cooler. A ƙofar ɗakin Amina ta tsaya suka gaisa da masu jere, ta miƙa musu abincin ta yi musu bayanin kanta. Ta sake fita ta shigo da ruwa da manyan lemuka ta ajiye musu, sannan ta nufi ɗakin Bilkisu.

Tun da Fadila ta shigo Bilkisu ta hango ta, ta cikin labule. Ta dubi ƙanwarta Hafsa ta ce.

"Hmmm dangin miji ko baƙaƙen munafukai, dubi Fadila can ki ga. Wai ita aka aiko ta kawo musu abinci, saboda neman wurin zama. Wai yanzu duk yadda nake da su Fadila, haka za su yi mini su koma ɓangaren amarya." Bilkisu ta ƙarasa maganar cikin ƙwafa.
Ajiyar zuciya Hafsa ta sauke ta ce, "To ya za ki yi ai sai haƙuri, kin san mijinki ne fa ɗan'uwansu. Kuma duk abin da yake so shi za su so, tun da ke dai bare ce a cikinsu." Shiru Bilkisu ta yi ta cigaba da girgiza ƙafa, suna nan zaune Fadila ta shiga ɗakin da murmushi bakinta ɗauke ta sallama.

"Ina wuni Aunty Bilkisu." Fadila ta faɗa cikin girmamawa, tun daga ƙasa Bilkisu ta ɗebo Fadila da harara ta watsar a gwasale ta ce.
"Lafiya."

Shiru Fadila ta yi tana tsaye, don ba ta ga fuskar da za ta zauna ba. Bilkisu ta ce, "To ai sai ki koma can tun da wurinsu kika zo."

"A'a abinci ne kawai na kawo musu." Fadila ta faɗa a sanyaye. Kamar Bilkisu tana jira ta ce.
"Ai shi ne na ce ki koma can, tun da ni matar yayanki ce waccan ɗinma da za ki wurin matarsa ce." Fadila ba ta tanka wa Bilkisu ba ta fice daga ɗaki ta yi wa 'yan'uwan Amina sallama ta tafi.

"Haba Aunty Bilkisu, ki dinga rage wani abin mana. Wai ba ki ga yadda Aunty Murja ta yi ba ne, kowacce mace fa tana jin kishi kawai iya taku ne." Hafsa ta furta, don ta lura idon yayarta ba ƙaramin rufewa ya yi ba. Cikin masifa ta ce .
"Ita daban ni daban, malama kema idan ɓata mini rai za ki yi ki fice ki ba ni wuri." Hafsa ta yi shiru tana mamakin zafin ran 'yar uwarta.

Koda 'yan uwan Amina suka gama jere ba duka suka tafi ba, sai aka bar mutum biyu a ɗakin da yayarta da kuma ƙanwar babanta. Suna gani Bilkisu shiga ɗaya-biyu idan ta yi sai ta yi musu habaici, ko ta saki tsaki tana harararsu. Sai da aka idar da sallar Magriba, sannan Hafiz ya aika aka ɗauko Amina zuwa gidansa.

GIDAN ALHAJI UMAR

Tun ranar da Shukura ta cika kwana shida a gidan Hajiya Karima ta yi ɗan jiƙe-jiƙenta, dangin abin da ya shafi tsimi da sauransu. Dama tun asali Hajiya Karima mace ce mai gyara sosai, tana da tsafta uwa-uba ba ta wasa wurin gyaran jikinta. Ta yi wannan haɗe-haɗen na musamman ne, saboda yadda ta lura da rawar jikin da Daddy yake yi a kan Shukura. Ba ta son ko kaɗan ya ga gazawarta, ko ta fuskaci wulaƙanci a wannan ɓangaren daga wurinsa. Saboda ta san duk son da namiji yake wa mace dole tana buƙatar gyara, kuma ko namiji bai fito ya bayyana ba idan bai samu yadda yake so ba za ta ga alama.
Ko lokacin da Alhaji ya shiga ɗakinta, ta gama shan tsumin gumbar nonon raƙumi da ta sassaƙen ɓaure. Yana shiga ɗakin ta ƙare masa kallo duk sai ta gan shi a firgice, ƙarasawa ya yi gefen kujerar da take zaune ya sakar mata murmushi. Martanin murmushin ta mayar masa, ya riƙo hannunta ya ce.
"Mommyn Mami kin ga yadda kika yi kyau kuwa?"
Murmushi ta yi ta ce , "Wanne irin kyau kuma, kai da kake da amarya." Ta faɗi haka don ta ji me zai ce.

"Kowa ai da irin nata kyawun."Ya furta mata yana murmushi. Shiru ta yi tana jin daɗi har a ranta, saboda ta ji an ce maza idan suka yi aure haushin iyayen gidansu suke ji. Amma ita sai ta ji yana yabonta, tana cikin tunani ta ji ya ce.

"Dama zuwa na yi na nemi alfarma a wurinki." Ba ta kawo komai a kanta ba ce.
"Alfarma kuma Daddyn Mami? Wacce iri kenan?"

Gabansa yana faɗuwa, ya zaro kuɗi daga aljihunsa ya dire a gabanta. Muryarsa tana rawa ya ce.
"Amm... dama... so nake ki sayar mini da kwanaki bakwai."

Dum! Ta ji kanta a saman kanta kamar an buga mata guduma, wani abu ne ya turniƙe mata ƙirji. Murya a ɗan sarƙe ta ce.
"Ban... ban gane ba." Kunya ce ta kama shi, amma har cikin zuciyarsa yake jin ba zai

3 / 46