Author : Ameera Adam Category : Read Hausa Novels
iya ɓata wa Shukura rai ba, uwa-uba ba ya son yin nesa da gangar jikinta. A tattaro mayafin jarumta ya yafa wa kansa sannan ya ce.
"Ina nufin ki sayar mini da kwana bakwai na ƙara a wurin Shukura." Ya ƙarasa maganar yana satar kallonta. Haɗe fuska ta yi tamau, rai a ɓace ta ce.
"Ban amince ba Alhaji."
Ransa ne ya fara ɓaci, don haka ya ɗauki kuɗin ya ɗora mata a cinya ya ce.
"Shi ya sa na kawo miki dubu hamsin ga shi nan, kwana bakwai fa kawai zan ƙara haba Hajiya." Ya ƙarasa maganar a ɗan tsawace. Da mamaki take kallonsa ita ma, don ta sake ɓata masa rai sai ta ce.
"Ka ɗauki kuɗinka ba na so, kuma kwana ban lamunce ba."
Da sauri Alhaji ya ce, "Au haka kika ce? Ke wacce irin mace ce ne wai? Shekara nawa muna tare da ke kawai don na ce ki ƙara mini kwanaki za ki ɗaga wa kanki hankali? Yarinyar nan fa 'yar cikinki ce, don Allah ban da abin mata kishin me za ki zauna kina yi da ita?"
Shiru Hajiya Karima ta yi har lokacin ba ta daina bin sa da kallo ba, zuciyarta ta fara wassafa mata abubuwa da dama.
'Kada ki yarda, idan kika amince masa wallahi daga ranar yarinyar nan za ta raina ki.'
'Ki yi haƙuri ki kyale shi ya yi kwanakin da yake so, 'ya'ya gare ki idan kika biye wa namiji ba kunya gare shi ba. Zai iya aikata abin da zai shafi tarbiyyar yaranki ko kuma ya sa su fahimci rashin jituwa a tsakaninku.'
Shawarar ƙarshe da zuciyarta ta ba ta, ta ɗauka don haka ta ce.
"Shi kenan babu damuwa, kwana bakwai ai kamar yau ne." Washe baki ta ga ya yi, ya matsa kusa da ita ya rungumo ta ya ce.
"Yawwa ko ke fa Hajiya, idan kika kwantar da hankalinki Shukura ba baƙuwar zafi ba ce. Yanzu akwai abin da kika buƙata ne?" Girgiza masa kai ta yi a sanyaye ta ce.
"Babu abin da muke buƙata."
Miƙewa ya yi ya fice daga ɗakin, ya nufi ɗakin Shukura. A kwance ya same ta, ya rungumo ta ya ce.
"Baby ta amince."
Da sauri Shukura ta riƙe shi ta ce.
"I love you Babyna." Fake ya sakar mata a goshi ya ce.
"I love you too my baby."
Ɗan lumshe ido ta yi ta ce, "To amma idan mun gama yau ina son shaƙatawa, almost six days kenan fa ina gida Baby." Shiru ya yi ya ce.
"Don't worry baby, idan wannan ne an gama."
Farr Shukura ta yi da ido sannn suka cigaba da hirar soyayya.
Ummou Aslam Bint Adam🌚
07062062624
[17/06, 18:06] Ameera Adam: *DAHUWAR ƘAHO*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
Gargaɗi: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ko a karanta shi a kafar sadarwa, ko ɗorawa a wata manhaja ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.
Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba, idan ya yi daidai da yanayin labarinki/ka arashi ne.
https://chat.whatsapp.com/IAZVt2Pz4LvIcklCxSTHwo
SHAFI NA HUƊU
A daren ranar sai da Alhaji ya fita da Shukura, ba su suka dawo ba sai da dare ya tsala. Don gabaɗaya yaran gidan sun yi bacci sai Hajiya Karima ce ta ji motsin shigowarsu, shiru ta yi tana mamakin wai ita ce yau Alhaji ya sayi kwana a wurinta. Murmushin takaici ta yi tana jin hawaye mai ciwo yana zubo mata, ganin tunani zai yi mata yawa ya sa ta ɗauki carbi ta kwanta da shi tana lazumi har bacci ya yi awon gaba da ita.
A washegarin ranar ma da yake Ruƙayya ba ta da lecture ta safe ita da Mommynta suka shiga kicin suka sarrafa abin karyawa. Kuma a ranar ne Hajiya ta ci alwashin yi wa Alhaji magana dangane da girki, tun da ta yi mata na kara wato girkin sati ɗaya. Tana son ta ji idan raba girki za su yi, ko kuma haɗewa za su yi. Su Shukura ba su fito ba sai kusan sha biyun rana, a lokacin yaran gidan duka sun tafi makaranta. Hajiya Karima tana zaune a falo tana kallo suka shiga, gaisawa suka yi da Alhaji sai washe baki yake yana haba-haba da ita. Shukura ba ta gaida ta ba, sai ita ce ta gaishe ta. A yatsine Shukura ta amsa mata, Hajiya ta yi kamar ba ta ga irin kallon rainin da take yi mata.
Kwanciya Shukura ta yi a jikin Alhaji ta ce, "Baby yunwa nake ji." Jin haka ya sa a birkice Alhaji Ya ce.
"Hajiya ina abincin ne?"
Sauke ajiyar zuciya ta yi ta ce, "Yana kicin." Miƙewa ya yi da kansa ya shiga kicin ya ɗauko musu ya ajiye, har zai zuba musu Shukura ta maƙale kafaɗa ta ce.
"Mu je can mana baby sai na fi sakewa."
Kamar wanda ake ba wa umarni haka ya yi zumbur ya miƙe zai fita, cikin sauri Hajiya Karima ta ce.
"Alhaji ina son magana da kai." Ɗan satar kallon Shukura ya yi sai ya koma ya zauna. Hajiya Karima ta ce.
"Dama game da girki ne, na ce za a haɗa girki ne ko kowa zai yi nasa? Saboda ina son sani ne don Shukura ta karɓi girkint." Shiru ya yi yana son jin abin da Shukura za ta faɗa, don yana gudin ya ɗauki wani zaɓin ta ce bai yi mata ba, Hajiya kuma ta ga kamar zaɓin Shukura yake bi.
"Tabɗi, gaskiya ba zan iya girkin haɗaka ba. Duka yaushe na zo da zan fara girka uwar tukunya, kowa dai ya yi nasa kawai shi ne magana." Shukura ta furta cike da tsiwa, jinjina kai Hajiya Karima ta yi tana jin zuciyarta na zafi. Kasa daurewa ta yi ta ce.
"To ai kin san yana da tawagar kika aure shi haka." Kamar Shukura tana jira ta ce.
"Eh saboda shi mijin mace huɗu ne, kuma don na aure shi ba shi zai sa na yi wa 'ya'ya bauta ba."
Hajiya Karima za ta yi magana Alhaji ya ce.
"Yanzu dai duk ba wannan ba, shi kenan kowacce ta yi girkinta ina ganin haka zai fi." Amsawa Hajiya Karima ta yi ta miƙe ta shiga ɗaki, taɓe baki Shukura ta yi ganin Alhaji zai bi Hajiya Karima ya sa ta riƙe hannunsa suka nufi ɗakinta.
Alhaji Umar mai leda shi ne cikakken sunan Daddy, asalinsa mutumin Jigawa ne. Neman kuɗi ne ya kawo shi Kano, shi da Hajiya Karima auren saurayi da budurwa aka yi musu, mahaifinta da mahafinsa duka abokai ne. Don haka aka haɗa su aure a wancan lokacin, lokacin da aka yi aurensu Alhaji dako yake yi a kasuwar singa da ke Kano. Rashin wadataccan ƙarfi ya sa bai kawo Mommy a lokacin ba, har sai da ya ta haifi Ruƙayya (Mami). Da yake a lokacin ya ƙara samun cigaba ya zama yaron shago. Daddy mutum ne mai zuciyar nema, kuma a tsaye yake a kan iyalinsa daidai gwargwado. Ba za ka saka shi a cikin sahun hamshaƙan masu kuɗi ba, kuma ba zai shiga sahun talakawa ba. Shi mutum ne mai rufin asiri daidai misali, yana da dukiya mai yawa da kadarori.
Hajiya Karima macece mai haƙuri da zurfin ciki, tun asali ba ta da hatsaniya. Zamanta da Alhaji ne ya sa a haka ake ganin ta yi baki, duk da wanda bai santa a baya ba zai dinga yi mata kallon marar son magana.
Haihuwarta takwas da Alhaji Umar biyu sun rasu, sai guda shida da suke raye. Ruƙayya ita ce babba tana shekara shirin da huɗu, sai Haidar yake bin ta. Shi kuma tsiran shekara ɗaya ne tsakaninsu da yake kwanikar haihuwarsu ta yi. Sai Nabil, Nazir, Sadik da kuma Sulaiman ɗan autanta mai shekara goma. Lokacin da Alhaji ya yi aure bikin Ruƙayya saura wata biyu, don haka take ta Allah-Allah ta bar gidan ko ta rage ganin kayan takaici. Ita da Haidar gabaɗaya suna level 400 a makarantar Maitama Sule University da ke Kano, Nabil da Nazir kuma sun yi candy neman Admission suke yi. Sai Sadik da yake ƙaramar sakandire, shi kuma Sulaiman yana ajin ƙarshe na firamare ba.
Tun da Alhaji ya raba girki kowa ya koma yin nasa, don haka wani lokacin sai a shafe wuni guda wani bai ga wani ba a cikinsu. A haka kwanaki suka dinga shuɗewa har Alhaji ya dawo ɗakin Mommy, yanayinsa babu yabo babu fallasa. Sai dai ta lura wuni Shukura ta yi tana shige da fice a gidan tana ɓace-ɓacen rai. Ita Hajiya abin har mamaki ya bata, saboda gani ta yi har idan kishi ne ai ita ya kamata ta nuna kishinta. Tun da ita ta shafe shekara da shekaru da shi suna tare. A daren ranar da Alhaji ya dawo ɗakin Mommy cikin dare suna kwance suka ji ihun Shukura, daga Daddy har Mommy rige-rigen fita suka yi don ganin abin da ya faru. A tsaye suka same ta daga ita sai wata yaloluwar rigar bacci, samarin gidan da su Ruƙayya ne su ma duk suka firfito. Ganin yanayin da take ciki ya sa su Haidar suka koma ɗaki, kallo ɗaya Ruƙayya ta yi mata ta saki tsaki har sai da Shukuran ta waigo suka haɗa ido, sannan Ruƙayya ta yi tafiyarya ɗaki.
"Me ya faru kike ihu Shukura?" Daddy ya furta cikin kulawa. Kuka ta rushe da shi ta ce.
"Ina kwance kawai na ji an shigo mini ɗaki, ban yi aune ba na ji an fara jan zanin jikina ƙasa." Cikin sauri Daddy ya ce.
"Shigowa? Ɗakin naki aka shigo?" Gyaɗa kai ta yi tana cigaba da kuka, haskawa ya fara yi ya ga ko ina a rufe kamar yadda yake. Ya haske saman doguwar katangarsu bai ga alamar za a iya hawa ba, haka daga ƙofar da za ta sada ka da babban gate a datse take. Cikin mamaki Dadday ya ce.
"Ko dai mafarki kika yi Shukura?"
"Ni babu wani mafarki, bayan ana ji na yi ihu na ji an fito da gudu kuma ba fita aka yi ba a cikin gidan nan ne."
Wani irin ɓacin rai ne ya dira a zuciyar Hajiya Karima, don ta fahimci sarai makirci ne da tuggu za ta yi wa yaranta. Rai a matuƙar ɓace ta ce, "Ke yarinya ki shiga hankalinki, wallahi kada ki kuskura ki saka yarana a cikin makircinki."
"To ni me nace? Na ce 'ya'yanki ne suka shigo? To ko dama can haka yaran na ki suke?"
Shukura ta yi maganar tana narkewa, a zafafe Hajiya Karima ɗago za ta yi magana Alhaji ya ce.
"A'a Hajiya ki dai bari a gama jin bayaninta, da kike musawa Shukura yarinya ce da za ta yi ƙarya ne?" Jikin Hajiya Karima wani irin sanyi ya yi, ta zuba wa Alhaji ido cike da mamaki.
GIDAN HAFIZ
Sai da 'yan kawo amarya suka watse sannan Hafiz ya shiga gidan cikin shigar angoncinsa ta babbar riga. Ɗakin Bilkisu ya fara shiga, ya same ta a kwance a kan gado idanunta duk sun kumbura alamun ta ci kuka ta more. Duk sai ya ji tausayinta ya kama shi, zama ya yi a bakin gadon ya ce.
"Ummu Sayyid." Ɗagowa ta yi ta dube shi, sai ta ga ya yi mata wani irin kyau. Nan take kishi ya mamaye ta, hawaye ya fara zuba daga idonta. Hannu ya saka ya goge mata, tana jin hannunsa ba ta hana shi ba. Cikin tausasawa ya ce, "Zo mu je falo." Girgiza masa kai ta yi ta ce.
"Ba zan iya ba Abban Sayyid."
"Don Allah ki daina kukan yana damuna." Ɗagowa ta yi ta zuba masa ido ta ce.
"Yanzu fa wurin wata za ka tafi ko? Dama Hafiz za ka iya mu'amala da wata macen bayan ni..."
"Don Allah ki daina wannan maganar Bilkisu, ki taso mu je please." A sanyaye ta zuro ƙafafuwanta ƙasa, ta ɗauki hijabi ta saka tana goge fuskarta. Ɗakin Amina ya shiga ita ma ta kira ta, Bilkisu tana ganinta gabanta ya shiga faɗuwa. Nasiha Hafz ya fara yi musu, jin ba za ta iya danne abin da yake cikin zuciyarta ba ya sa ta miƙe fuuuu ta shige ɗaki. Girgiza kai Hafiz ya yi, ya ce Amina ta koma ɗakinta, sannan ya shiga ɗaki wurin Bilkisu. Yana shiga ya hango ta ta cusa kanta cikin ƙafafuwanta, ƙarasawa ya yi gabanta sai kawai ta ɗago ta rumgume shi ta saki sabon kuka. Riƙe ta ya yi sosai, musamman yadda ya ji jikinta yana rawa. Murya a dashe ta ce.
"Mutuwa zan yi."
"Ki daina faɗin haka Bilkisu, ke fa musulma ce don Allah ki ɗauki wannan auren a matsayin ƙaddara."Hafiz ya furta cikin lallashi, sannan ya ajiye mata ledar kazarta da lemuka. Sallama ya yi mata har ya juya zai tafi ta ce.
"Au da gaske wurinta za ka je?"
Shi maganar ma dariya ta so ba shi, don ya lura wani abin da Bilkisu take yi kamar ba ta cikin hayyacinta. Ya waigo ya ce.
"Eh." Sai hawaye ya cigaba da zuba daga idonta cikin kuka ta ce.
"To ka je duk abin da ka yi mini, Allah ya yi maka Hafiz kuma ka zo ka ɗauki tsinanniyar kazarka ba na ci." Ta ƙarasa maganar tana yin jifa da ledar da ya ajiye. Hafiz bai kula ta ba ya wuce ɗakin Amina, sai da ya ba ta haƙurin jimawar da ya yi sannan suka shiga gabatar da abin da yake gabansu.
Kamar wata wacce aljanu suka kama haka Bilkisu ta dinga ɓurumtu tana shige da fice a tsakar gida, kusan yadda ta ga rana haka ta ƙarasa ganin darenta. Da asubar fari ta ji Hafiz ya haɗa musu ruwan wanka ya kai banɗaki, jin haka ya sake ɗaga hankalin Bikisu. Da ƙyar ta lallashi kanta, ta samu ta gabatar sallar asuba.
Tun asuba ta shiga ɗakin yaran ta dinga jibgarsu tana tashinsu sallah, abu kaɗan za su yi za ta fara zaginsu tana duka. Tsakar gida ta fita, ta cigaba da kwaramniya da kwanuka tana fafutukar ɗora abinci. Su dai yaran shiru suka yi, duk suka takure wuri ɗaya. Tsoron mahaifiyarsu duk ya kama su, sun san dai ranar asabar babu makaranta. Kuma sun ga sai shiri take yi tana musu masifar su yi su ci abinci kada su makara, tsoron kada ta dake su ya sa suka gagara faɗa mata. Don haka a ranar tun bakwai da rabi ta gama shirya su, ta ƙarasa ƙofar ɗakin Amina ta shiga bugawa da wani irin ƙarfi.
Tun da Hafiz ya yi sallar asuba bayan ya leƙa Bilkisu da yara, ya koma ɗakin Amina ya kwanta suka koma bacci. Suna tsaka da bacci suka ji bugun ƙofa a tsakar kansu, a hargitse ya fito daga shi sai gajeren wando yana faɗin.
"Lafiya Bilkisu me ya faru ne?" Kallon yanayin da yake ciki ya sake turnuƙe ta, a fusace ta ce.
"Ta ina za ka san abin da ya faru? Tun da ka saka mace a ɗaki kamar a kanta ka fara sanin mace." Ko kaɗan bai ji daɗin furucinta ba, saboda ko babu komai yaransa suna tsaye suna kallonsu.
Rai a ɓace ya ce, "Wai me yake damunki ne Bilkisu? Wacce irin maganar banza kike yi haka a gaban yara ne?"
"Ƙarya na yi? Ba macen ka saka a gaba ba? To duk jarabarka sai ka fito ka kai yara makaranta."
Bilkisu ta faɗa cike da kishi. Waigawa ya yi ya hangi yaran duk sun yi zuru-zuru, kallo ɗaya za ka yi musu ka fahimci a tsorace suke. Ga su sanye da uniform da kulolin abinci, girgiza kai ya yi a ransa ya ayyana tabbas Bilkisu ba ta cikin nutsuwarta.
"Dama suna zuwa makaranta ranar asabar ne? Ko kin manta yau asabar?" Shiru Bilkisu ta yi cike da kunya, jin hayaniya ta yi yawa ya sa Amina ta ɗan turo ƙofar ta leƙo. Kanta babu ɗan kwali ta sha ƙananan kitso mai kyau, ta yafa zanin rufa a jikinta.
"Ina kwana Aunty."
Ta furta a sanyaye, wani mugun kallo Bilkisu ta wurga mata kamar tana jira ta ce.
"Kada ki sake ce mini Aunty, ni ba yayarki ba ce. Me na haɗa da ke? Ai ƙanwata ba za ta taɓa auren mijina ba." Waigawa Hafiz ya yi ya ce.
"Koma ciki."
Babu musu Amina ta koma ciki, ya riƙe hannun Bilkisu ya kai ta ɗaki ya zaunar a kan kujera. Ƙasa ya yi da murya ya ce.
"Haba Bilkisu, me ya sa duk maganar da nake yi miki ba kya ji ne? Don Allah ki kama girmanki, ba na son ki dinga abin da yarinyar nan za ta zo ta raina ki. Yanzu don Allah me kika yi haka? Kin fa san yau weekend, yaran nan ba sa zuwa makaranta."
Idon Bilkisu ne ya ciko da ƙwalla ta ce, "To ai mantawa na yi." Hannu ya saka ya goge mata hawayen, zai miƙe ta sake cewa.
"Yanzu shi kenan kuma ka daina sona." Shiru ya yi cike da damuwa, ya girgiza mata kai ya ce.
"Idan ana mata ɗari ko fi, duk wacce zan auro ba zan daina sonki ba Bilkisu. Don Allah kada ki sa wannan a ranki, kin taɓa ganin namiji ya zauna da macen da ba ya sonta?" Girgiza masa kai ta yi ta ce.
"To amma ai ga shi nan ka je ka kwanta da wata, shi kenan ta gama gane mini sirrinka."
Murmushi ya yi don ya san kishi ne duk yake damunta, ya matsa kusa da ita ya ce.
"Ke ce