MAFARKI Love and Horror Story By Mrs Sadauki.txt

Author :  Mrs Sadauki Category :  Hausa Read

Chapter   18 / 18

51K to 53.5K   out of 53.5K words

ƙoƙorin ɗaukewa,don haka ba ƙaramin jin daɗi ta yi ba da Nelson ya shigo ya same su wanda hakan yasa ta samu damar silalewa.

Tana tafe tana gwada buɗe idon nata amma ta kasa,yau ɗin ma ji ta yi wani abu na yi mata motsi a tsakiyar goshi kafin kuma ta samu damar ganin duk abin da ke gabanta.Sam ba ta yi tunanin idonta ne na uku ya buɗe ba,a haka ta ƙarasa gida tana buɗe ƙofa Dadda ta saki ƴar tukunyar ƙasar da ke hannunta tana mai kallon idon da ke tsakiyar goshin IZZATU wanda kuma da idon ne take kallonta.


“Dadda lafiya kika saki tukunya haka kamar kin ga aljana?” IZZATU ta tambaya.

Dadda ta haɗiye wasu yawu kafin ta zo da sauri kamar za ta faɗi ta kamo hannun Izzatun .Jikinta na ɗan rawa ta fiddo wani tandun kwalli cikin aljihun rigarta,ta shafa wa kanta sannan ita ma Izzatun ta shafa mata.Kamar ƙuda haka suka dawo ƴan ƙananu da su,Dadda ce ta kama hannun Izzatun suka shiga wannan tandun kwalli wanda ya kasance wata duniya ce ta daban da wasu al'ummar ke rayuwa a cikinsa.



IZZATU wacce take ganin komai kamar a mafarki ta soma ƙoƙarin toshe hancinta da yake shaƙo mata wani irin wari kamar na ruɓaɓen kifi,ga wani irin duhu da ya mamaye ko ina.A cikinsa Dadda ke ci gaba da jan hannunta suna tako cikin caɓo har suka isa wani tabkeken Teku sai duk suka ja suka tsaya.A wannan lokacin duka idanun IZZATU uku a buɗe suke,murya na ɗan rawa ta ce “Dadda ina ne nan kuma kika kawo ni?”

Idon Dadda suna fitar da wasu ruwan hawaye ta ce “asalinki shalele zo mu je” sai ta ƙara janta suka fara ratsa ruwan har suka je tsakiya .Wasu mata ne suka fara yin da'ira suna fitowa daga ƙasan ruwan suna zagaye su.

A tsorace IZZATU ta riƙe Dadda gam,ɗaya daga cikin matan ce ta matso tana cewa “kar ki ji tsoro ƴata,ba ki zo nan don a cutar da ke ba sai don nuna miki hanyar da ya kamata ki ɗauka sannan kuma mu buɗe miki taurarinki” sai ta kamo hannun Izzatun nan take ruwan suka yi wani irin juyawa kamar walƙiya suna fitar da wani irin sautin wuluuuk.Jiri ne ya soma ɗibar ta,ganinta ya dinga dissashewa , kunnuwanta suka fara jiyo mata waƙe-waƙen kwaɗo,wani ɓangaren kuma dariyar mutane ce ke fitowa daga can nesa da su garwaye da maganganun wasu mutanen daban suna magana kamar a lokaci guda.Can kuma komai ya tsaya cak,tunaninta ya yi duhu,igiyar da ke saita numfashinta ta katse.Ba ta ƙara sanin abin da ya faru ba sai tashi ta yi ta ganta kwance a kan gadonta wanda aka yi masa ƙawa da manyan kyandir sun zagaye shi suna ci da wuta.Izzatu ta yunƙura za ta miƙe ta ji wani abu mai taushi da santsi a cikin tafin hannunta,tana buɗewa ta ga wani jibgegen Kwaɗo ne kore sharrr da shi ya zubo mata manyan idonsa....



*Da zarar na saki last free page shikenan book ya dawo 500 ,don haka wanda ke buƙatar discount ya yi niyya ya yi payment 300 Via* 2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank DM +27795045822

🚫Ga détail nan na bada Please ki tura kawai kai tsaye ki bani shaidar biya ta WhatsApp, yan Nijar carte Moov ko airtel ta 300f
[18/12 13:06] MRS SADAUKI: *INUWAR ALJAN*👻



```LoVe aNd HoRrOr story```👽


By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}



*SADAUKARWA:* Ga Rachida Mamar ƴan biyu, alherin Allah ya luluɓe ki . Ubangijin rahama ya kula da lamurranki👏🏻

*FCWA*☀️

________________________


10


Wani irin matsanancin dokawa ƙirjinta ya yi,kamar kuma wacce aka yi wa dole ta ƙi jefar da Kwaɗon sai ma kallonsa da take yi ita ma kamar yadda ya zuba mata manyan idonsa.

“Barka da safiya Queen!” ta ji wata siririyar murya irin ta maza,bakinsa ta ƙure da duba sai ta fahimci yana motsi kuma daga nan ne maganar ta fito.

“Kar ki ji tsoro ni ne abokin ɗebe miki kewa ” ya sake faɗa .

Ba tare da ta buɗe baki ba ta jefo masa tambaya ta idonta na tsakiyar goshi “wane ne kai? Mene ne haɗina da kai? Mafarki nake yi ko gaske?”

Tana gama jero tambayoyin ya yi tsul ya sauka daga cikin tafin hannunta ya sauka kan ƙirjinta,kamar wani mutum haka ya ɗora tannuwansa kan haɓarta kafin ya ce “na kasance tsawon ƙarni biyu da wasu ƴan shekaru ina wanzuwa a wannan doron duniyar ta bil'adama,ba don komai ba sai don yi wa masu jinin prophecy jagora zuwa tsoffin asirai da wasu ɗaiɗaikun musulmi suka yi amfani da su waɗanda suka sha banban da sauran waɗanda ki ka sani.Ba mafarki ki ke yi ba,a zahiri ne ki ke tare da protector ɗinki,babbar alaƙata da ke ita ce jagora” yana gama faɗar haka ya wani turo bakinsa gaba sannan ya tsirta mata yawunsa masu yauƙi,da wani mugun sauri ta rufe ido tana mai yin wata irin ƙara saboda zafi da raɗaɗin abin da ta ji ya game mata fuskar kamar wuta. A hankali fuskarta ta soma canza launi tana rikiɗa zuwa kore kamar dai jikin kwaɗo,tsawon lokaci kafin ta dawo normal .

Ta buɗe idonta tana mai jan numfashin wahala kafin ta tashi zaune, wannan karon kuma cike da murna ta ɗauko Kwaɗon ta ɗora a tafin hannunta kiss ta yi masa a goshi kafin ta sauka ta ɗauko ƴar ƙaramar jakarta wacce a duk inda za ta je tana maƙale da abarta a ciki ta jefa shi kafin ta shiga wanka.Sai bayan ta fito ta yi sallah tana tsaka da shirya wa Dadda ta shigo hannunta riƙe da ganyen bishiyar floris.

“Daga ina haka tun da safe?” Izzatu ta tambaya tana mai saka doguwar riga.
Dadda ta ce “ke ya kamata na tambaya ina zuwa da farar safiya?”

“Na warware zan koma bakin aikina,saura ke ki faɗa mini ina ki ka je?”

Dadda ta ɗan ja baki kafin ta ce “dajin tsira na je,ungo wannan itaciyar sirri ce ki dinga tafasa ta kina zuba ruwan a cikin shayin Yarima ”

Wani kallo Izzatu ta soma yi mata,Dadda ta dungure mata kai ta ce “yana da muhimmancin ne a rayuwarsa kin ga ke ma in kina so za ki iya sha”


Izzatu ta turo baki kafin a shagwaɓe ta ce “shi ne tun can ba ki taɓa bani ba sai yanzu da Yarima ya zo? To na ƙi na sha ɗin shi kaɗai zan saka ma tun da kin fi sonsa fiye da ni ”

Dadda ta yi ɗan murmushi kafin ta ce “haba shalelena!” Izzatu ta mayar mata da martani kafin ta fice,tana tafe tana rangaji har ta isa sashen Yarima.


Falonsa ta soma sharewa ta goge ta saka turare sannan ta shiga kitchen ta soma haɗa masa breakfast kamar yadda aka ɗora mata nauyin dukkan abin da ya shafe shi.Tana aiki tana karatun Alkur'ani cikin taushin murya da daɗin amo.


★YARIMA


Bayan na gama bincike akan babyn littafin sirri ban samu komai ba haka na kwanta lamo ina tunanin abubuwan da suka ƙunshi rayuwata a haka bacci mai ya ɗauke ni ban shirya ba sai kuma na tsinci kaina a wata duniyar wacce ba ta bil'adama ba.

A gaban idona babyn littafin sirri ta fito ta daga cikin page ɗin ta zo ta yi tsaye a gabana,a hankali take daɗa girma har ta zama matashiyar budurwa sai dai baƙin dogon gashin kanta ya rufe mata fuska hakan ya hana ni ganin ainahin face ɗin nata .Wasu fitinanun kayan bacci ne a jikinta waɗanda suka fallasa ni'imar da baiwar da Allah ya zuba mata.Cikin abin da bai fi minti biyu ba casbin hankalina ya katse ,nutsuwata ta gushe jikina na ɗan rawa na jawo ta gare ni ta faɗo kan ƙirjina ina shirin yaye gashin gaban goshinta ɗakin ya ɗauki duhu sai hannuwanta da na ji suna yawo a duk illahirin jikina.Cike da tsimin abin da ban taɓa jinsa ba a siffar normal ni ma na dinga mayar mata da martani har ta kai na kusance ta.Ba wai iya cikin baccin ba ne na samu gamsuwa a'a har a zahiri ina jin daɗin mu'amulantar juna da muka yi.


Ina gama samun kaina na farka daga baccin,da baiwa Izzatu na ci karo ta juya kenan za ta fita da sauri duk illahirin jikinta kuma rawa yake.Da na dubi jikina sai na ga ko albarkar blanket ɗin rufa babu,ƙila kuma ta ga yanayina ya canza ne a yayin da nake bacci.Ko kaɗan ban yi ƙoƙarin tsayar da ita ba,tana fita na miƙe cike da ƙyanƙyami ina jan tsuki na shiga toilet na cire kayan jikina na yi wanka na ɗauro towel na fito.


Gaban makeken madubina na yi tsaye wanda aka cika da mayukan gyaran fata da Kuma turaruruka.Ina tsane jikina ina kuma kallon siffata ta madubin,duk da ina baƙi amma ina da kyau da kuma nagartar da duk wata ƴa mace za ta so mijinta ya kasance da ita.Amma duk da haka wani irin tsoro ne nake ji kar na je wa da EZRA da buƙatata amma ta watsa mini ƙasa a ido duba da yadda na hango zallar ƙiyayyata a ƙwayar idonta.Na ja dogon numfashi kafin na soma shafa mai da turare,bayan na gama na je gaban drower na zaɓi kayan da zan saka da kaina saɓanin kullum baiwa Izzatu ce ke fitar mini da su.Ina gama kimtsawa na fita falo,can rakuɓe jikin kitchen na hange ta tana magana ita ɗaya don babu kowa kusa da ita.Ba tare da na ɗauke idona a kanta ba na je na yi zaune,sai kuma a lokacin ta farga da wanzuwata.Ta sunne kai ƙasa kafin ta fara takowa inda nake,ta ɗan tsaya nesa da ni kaɗan kafin ta ce “barka da fitowa ranka shi daɗe ”

“Sunana David in kuma ba za ki iya faɗa ba kawai ki ce Yarima ” na faɗa ina mai kallon yatsun ƙafafuwanta,wani irin yarrr na ji sakamakon ganin wani sirri a tattare da baiwa wanda ba kowacce mace ke da shi ba.

“To yallaɓai!” ta furta tare da juyawa ta shiga kitchen na bi bayanta da kallo a zuci ina cewa ‘bawan da zai samu wannan baiwar ya ji daɗinsa ya samu macen zinare ’


Ba ta wani jima ba ta fito hannunta riƙe da babban faranti,akan table ɗin gabana ta dire shi kafin ta soma haɗa mini shayi mai kyau sai dai aka samu akasi wajen rawar jikinta shayin ya zube mini a ƙirji.Ido kawai na rumtse yayin da kuma nake jin shashekar kukanta haɗi da hannunta yana goge mini rigar.


Cikin kiɗima da tsantsar tashin hankali take cewa “yi haƙuri don Allah, wallahi ba da niyya na yi ba.Hankalina ne ba ya jikina amma na yi maka alƙawarin ba zan sake aikata wannan kuskuren ba,don Allah kar ka hukunta ni ”


Ba tare da na buɗe idona ba na ji wani sashe na zuciyata na bani wata shawara da ta dace da halin da nake ciki ,ba tare da wani dogon tunani ba na buɗe ido ina mai haɗe rai na yi mata wata uwar tsawa wacce ta saka ta yin baya ta faɗi ƙasa kanta ya bugu a jikin table nan take kuma jini ya soma yi mata zuba.


Ba tare da ɓata lokaci ba ta ɓare baki ta shiga yin kuka,wanda zan ce shi ne raunina a game da ita don duk lokacin da na ganta cikin yanayin nan tana tuna mini ne da Joyel.

A hankali na sauko na soma ƙoƙarin tsaya da jinin ,sai dai ɗan kusanci da na samu da ita yasa na soma jin wata irin kasala na rufe ni.Na ɗan ja baya kaɗan na ce “je ki toilet ki wanke kayanki duk sun ɓace da jini,ki kuma wanke jikinki ”

Ba tare da ta ce komai ba ta miƙe za ta nufar waje,na dakatar da ita na ce “ki je can ɗakina” ta yo baya tare da nufar bedroom.Ta kai kamar minti biyar da tafiya kafin na take mata sawu,tsaye na yi ina jin motsin ruwa kafin na ƙarasa a bakin ƙofar zuciyata na ɗan dokawa.


A hankali na duƙa na soma leƙa ƴar hudar jikin handle,kusan suman tsaye na yi ganin baiwa Izzatu a tsaye gaban madubi daga ita sai pant ko bra babu amma ta juya wa ƙofa baya.


Das ! Das! Das! Haka bugun zuciyata ke tafiya ina Allah-Allah ta juyo don in ga abin da nake kwaɗayin ganin.Sai dai da dukkan alamu ciwon goshinta take ƙoƙarin rufewa,ƙugunta na duba wanda ya sha duwatsu ƙananu masu masifar kyau sai wani walwali suke yi.


Kamar wacce ke yi da gayya haka take ɗan motsawa sai ta yi kamar za ta juyo sai kuma ta koma daidai,a haka na shiririce ina kallonta ina haɗiyar yawu ina jin kamar na shiga ciki na same ta.

Yadda ƙafafuwana suka yi mini mugun sanyi yasa na lalaɓa na jawo blanket tare da kwanciya kan doguwar kujera na yi wa ƙofar toilet ƙuri da ido.Har sai da na fidda tsammani sannan ta fito da jiƙaƙun kaya,amma da dukkan alamu ma ba ta ankare da ni ba.
Fanka ta kunna ta yi tsaye daidai saitinta,ɗan juyawa ta soma yi tana yarfa ɗan maidaicin hijabinta ruwan ne suka soma feso mini a fuska,na lumshe ido ina jin ƙamshin turarenta na ƙara saukar mini da kasala.Ina cikin wannan hali sai ji na yi an faɗo mini ana kiran sunan.

“Wai Allah jiri nake gani!” ta furta tare da ƙanƙame ni,yadda ni da ita ɗin duk jikinmu bai da ƙwari yasa muka mirgino muka faɗo ita ke ƙasa ni kuma a kanta.Kusan a tare muka buɗe ido da ita sai dai ta yi saurin mayar da nata ta rufe ƙila ko jirin take ji,yayin da ni kuma muradina ya fi ƙarfin nagartata kawai na sauke bakina kan nata.

Yau ne karon farko da na taɓa jin son sumbatar mace,kuma yau ne farko da na fara.Babu wani tunani a cikin kwanyata banda na gusar da ƙishin da nake ji, wannan yasa kamar mayunwacin zaki haka nake kissing nata.Sam banda wata saurar nutsuwar da za ta sa na farga halin da take ciki, burina kawai na sani.Ina dab da cire mata sutura na ji wani masifaffen zafi ya ratsa gefen wuyana,babu shiri na mirgina gefe na dafe wurin da ke yi mini zugi.

Sinadarin ganina yana daf da rufewa na ga baiwa Izzatu ta kwasa a guje ta fita.Cikin dauriya da kuma jarumta na soma motsa bakina ina karanto ɗalasiman tsafi nan take na yi balaguron ruhi,na fitar da ruhina na bar gangar jikin nan kwance yayin da kuma na yi azamar tare baiwa Izzatu da ke dab da ta fita da katafaren sashena.Daidai nan free page ta ida duk mai son ci gaba zai biya 500 via 2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank DM +22795045822 ko kuma a turo katin mtn na 500.Don Allah duk wacce ke buƙata ga detail nan kawai ta tura sai ta bani shaidar biya.


*NB:* yanzu nake rubuta shi ,da zarar kuma ya zama complete 1k ne farashinsa.

18 / 18