ABBAN SOJOJI TAKUN TSAKIYA 2 BY BOSS BATURE.txt

Author :  Boss Bature Category :  Arewa Pen

Chapter   74 / 80

219K to 222K   out of 238K words

mata jiki sukayi ba,nan take taji soyayyarshi na ƙara ninkuwa acikin zuciyarta,
Cikin sanyin murya tace"bazan rabu dakai ba Abusufyan ɗina,i luv u so much,more than my life,bazan ta6a bijire maka ba,yanzu na gane cewa bani da masoyin da ya wuce kai aduniyar nan abusufyan,ina fatan Allah yabarmun kai,'ta ƙarasa maganar tare da hugging ɗinshi sosai ta kwantar da kanta asaman wide chest dinshi,dama tubarkallah duk da kananun shekarunsa yana da cikar kira ga hutu daya ratsa shi,hannunshi ya zura acikin hijabin jikinta yana shafa sumar kanta,sun jima a wannan yanayin kusan 30mins,kafin ya tashi motar ya miƙi hanyar komawa dasu gida,a kasalance yake yin driving ɗin,saboda sakonnin da abu ke aika mashi ajikinshi,duk ta jefa shi cikin wani irin yanayi,
  koda suka koma gida atare Suka ci abincin da Hajiya Ameenatu ta girka masu abun gwanin burgewa,bayin Allah ashe duk na bankwana ne,sukeyi ma juna basu sani ba,

lokacin kiran sallar magrib,abusufyan ya fito daga cikin toilet,jikinshi da danshin ruwa alamar alwala yayi,a lokacin abu na zaune gefen gadonsu tana jiran fitowarshi,jin alamar buɗe ƙopar shi yasa ta ɗan dago ta kalleshi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Sannu da fitowa hayatyna,"
Ƙarasawa yayi wurinta tare da zama daga gefenta yace"me kika tanadar mun yau idan nadawo gida da daddare?
Abu tace"komai kakeso,"
"To ki tanadar mun kan ki,yau zan baki mamaki,awashe gari zaki haifa mun babies bama ɗaya ba....'
  Dariya tayi sosai jin abunda yace kafin ya tashi yayi mata sallama tare da fucewa,'
Lokacin da aka kira sallar isha'e bayan tayi wanka ta ɗauro da alwala,sai da ta kammala sallar sannan ta shiga shirya kanta,tun tana shafa mai ajikinta take tunano kalamam abusufyan nacewa zata haifa mashi babies awashe garin ranar,ta lura ba ƙaramin son ƴa'ƴa gare shi ba,kusan kullum ne sai yayi mata maganar yaushe zasu haihu,wani lokacin har cewa yakeyi wai ko dae basu isa haihuwa bane shiyasa bata samu ciki ba,duk irin ƙoƙarin da yakeyi, don ba ƙaramin jarababbe bane,
Murmushi tayi tare da cewa"Nikaina aƙagare nake dana ga ƴa'ƴan da zamu haifa ni da abusufyan ɗina,nasan yaran zasu zama kyawawan gaske in dai suka ɗauko kyawun fuskar kowannanmu,amma ni dae nafi son su ɗauko fuskar shi,saboda koda wata rana in yayi tafiya mai nisa,zan dinga kallon fuskarsu a matsayin tashi,hakan zai ɗebe mun kewa,

Gaba ɗaya ɗakin ya gauraye da ƙamshin turaren da abu ta feshe jikinta dashi,bayan ta gama shafe shi da haɗaɗdun mayukan jikinta,komawa tayi gaban wardrobe ɗin kayansu ta buɗe tana tunanin wasu kaya zata sanya waɗanda zasu zautar da abusufyan,ta jima atsaye tana ruwan ido kafin ta hango wata rigar bacci Babby doll black color,net ne ajikin rigar shara shara ana kallon komai na jikin mutun,tamkar ma mutun bai sanya kaya bane saboda yadda take fitar da tsiraici,ba ƙaramin kyau rigar tayi mata ba,zubo da gashin kanta tayi ya sauko har wurin waist ɗinta,komawa tayi gaban mirror ta shafa jan baki red abakinta,

Bayan ta kammala shirin nata,ta shiga zagayen ɗakin tana jiran dawowar abusufyan,tana yi tana kallon wall clock dake manne a bango tana duba time,abu kamar wasa har ƙarfe 10 na dare babu abusufyan,shi da ya saba dawowa da zarar an kammala isha'e,baiwar Allah har ta fara gajiya da yawon,komawa tayi ta zauna gefen gadon tana sa ran dawowarshi,da zarar taji motsin mutun ya shigo cikin gidan sai ta miƙe jiki na rawa ta leƙa taga wanene  ashe Haris ne ya dawo,na biyu kuma data leƙa Abbansu ne ya dawo,ƙarshe dae bacci ya kwashe ta,wuraren goma sha biyu ta farka,ganin har lokacin bai dawo ba,yasa hankalinta yayi mugun tashi,saukowa tayi daga saman gadon ta ɗauko hijabi ta zura ajikinta,sannan ta fito daga ɗakin ta wuce bedroom ɗin haris,
  A ƙofar ɗakin ta tsaya tana kwankwasawa,
  Cikin bacci haris ya jiyo bugun ƙopar ɗakin nashi,muryarshi akasalance yace"Wanene,"
  Abu tace"ni ce Zainab,'
Saukowa yayi daga saman gadonshi yazo bakin ƙopar ya buɗe mata tare da cewa"lfy,meya faru ne abu?
  Abu tace"ɗan uwanka abusufyan har yanzu fa bai dawo cikin gidan nan ba,hankalina ya tashi sosai,bansan ko kana da masaniya akan inda yaje ba,"
  Cike da mamaki Haris yace"wai kina nufin bro ɗina bai dawo gida ba?tare dashi fa muka je masallaci,amma ba tare muka dawo ba,saboda yace mun yana sauri yazo wurinki ne,ni kuma na biya gidansu abokinmu ne,"
  Jin wannan maganar yasa hankalin abu ya ƙara tashi haikam,tuni idanunta sun cicciko da kwalla,dama bata da wuyar yin kuka,fargabarta kar ace wani abu ne ya faru da mijinta,
  Lallashinta haris yayi tare da cewa"just calm down ur mind,duk inda abusufyan yake yana atare damu,bana so ki tashi su mommy daga bacci game da maganar nan,hankalinsu zai tashi ne,bari na jaraba kiran numbar shi muga in zata shiga,"ya ƙarasa maganar tare da juyawa ya shiga cikin ɗakin nashi,
  Sai gashi ya dawo hannun shi ruƙe da wayarshi yana dannata,numbar shi ya kira,tana fara ringing abun mamaki akayi picking kiran,
  Da sauri haris ya kara wayar a kunnan shi yace"bros kana ina ne wai?har 12 baka dawo gida ba?duk ka tayar mana da hankali,"
  Gaban haris ne ya faɗi rass jin muryar mace tana cewa"mai wayar ya shiga wanka ne,'
  rejecting kiran yayi cikin sauri gudun kar abu tajiyo muryar macen da yaji,don ya santa da kishi,
  "Me ya ce maka"! Ta tambaya tana kallonshi,
  Daƙyar ya iya cewa"Am..um...kin gane wani aiki ne ya tsayar dasu a company,sai zuwa gobe ko da asuba zai dawo,dan Allah ki ƙara hakuri....'
  Tunkan yakai ƙarshen maganar tashi abu ta watsa da gudu ixuwa ɗakinsu ta faɗa saman gado tana kuka,tasha kuka sosai a ƙarshe bacci ya ɗauke ta,

Koda ta farka sallar asuba,abusufyan bai dawo ba,bayan tayi salla ta zauna tana karatun al'qur'ani don kar bacci ya kuma ɗaukarta,wuraren ƙarfe 7:30 tayi shirin zuwa islamiyya,duk da halin da take ciki na damuwar rashinshi,
   batare da sanin kowa ba ta fice ko breakfast ba tayi ba,a bakin gate suka haɗe da baba buzu,
   Zuƙunnawa tayi tare da gaishe shi"ina kwana baba,kun tashi lafiya,"
  Baba buzu yace"me ya faru abuna?naga fuskarki tayi jawur ta kumbura kamar kinsha kuka"?
  cikin sauri tace"a'a babu komai baba,lafiya ta lou,'ta bashi amsa tare da miƙewa tsaye,
  "Ina abusfyan ɗin yake ne yau bazai kai ki makarantar bane"?
  Shiru tayi tana tunanin amsar da zata bashi,
   Bai kawo komai aranshi ba,yace"kada ki makara ki wuce ki tafi,"
Amsa mashi tayi da toh sannan ta fito waje ta kama hanya tana tafiya ita kaɗae cike da damuwa,
  Kwatsam!kamar ance ta waiga ta hango Motar abusufyan yayi parking ɗinta a gefen hanya,mamaki ne ya kamata,
Jiki na rawa ta nufi wurin motar tare da sanya hannunta ta kwankwasa glass ɗin shi,
  Zuge glass ɗin akayi a slow,a gigice Abu ta zaro ido waje tana kallonsu,abun tamkar a mafarki, sun manne da juna abusufyan ɗin da take ta haukan nema tare da wata matashiyar budurwa cikin motar,budurwar ko kayan kirki babu ajikinta,inners ne kawai ta bari,da alama ma basu acikin hayyacinsu sunyi nisa cikin harkar tasu,
  Hankali amatuƙar tashe abu ta aza hannunta akai tana fadin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'una....!'
Tana ƙarasa faɗar hakan ta yanke jiki ta faɗi a sume ƙasa,zubewarta ƙasa ke da wuya,Motar nan tabar wurin tamkar bata ta6a bayyana ba,
  Adai dai lokacin kuma Motar Abusufyan ta shigo layin da gudun gaske,tunkan ya ƙaraso ya hangi abu sume a ƙasa cikin uniform dinta,gabansa ne ya faɗi rass,da sauri ya tsayar da motar tare da buɗe ta ya fito yana faɗin"kai!me nake gani haka?kodai idanuna ne suke nuna mun ba dai dai ba!abuna ce kwance a ƙasa!taya akai hakan ya faru!"
  ƙarasawa yayi tare da zuƙunnawa agabanta yana shafa fuskarta,ya jima yana mamakin yadda akai abu ta sume ƙasa,kuma tabbas itace,
  Hannu yasa ya ɗaukota ya nufi mota da ita bayan ya kwantar da ita abayan motar ya shiga gaban motar ya tashe ta suka nufi gida,

Lokacin da abusufyan ya shigo da abu a hannunshi,Hajiya Ameena suna xaune saman dining chairs ita da alhaji da kuma haris suna yin breakfast,
Hankali atashe suka nufo shi suna tambayarshi lafiya!meya faru da ita!
Hajiya tace"Yaushe kuka fita tare da ita batare da sanina ba!?
Abusufyan yace"mommy ba atare muka fita ba,ni jiya ban kwana agida ba,bacci ya ɗauke ni acikin mota ban ƙara sanin inda kai na yake ba sai da safen nan,kuma wayata ma an sace ta banganta ba,"
Mamaki ne ya kamasu su duka,musamman Haris kanshi ya ɗaure jin cewa an sace wayar abusufyan hakan na nufin cewa jiya wayar bata a hannunshi wasu ne suka ɗauke wayar,to garin yaya hakan ya faru,
  Hajiya tace"Haba abusufyan ɗina garin yaya har bacci ya ɗauke ka acikin mota,kuma aka sace maka waya,duk ta yaya hakan ya faru"?
  Muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"wlh mommy ni kaina bansani ba,wayata tun a masallaci aka sace ta,ban tashi ankara ba sai da na shiga cikin motata bayan mun rabu da haris,na kamo hanyar zuwa gida na dinga ganin biji biji acikin idanuna,dalilin dayasa na dakatar da driving ɗin nayi parking na motar,tun daga nan ban ƙara sanin inda kaina yake ba,sai yanzu dana farka,na biyo hanyar gida kenan naga abu a kwance ƙasa,ina tunanin wani abune ya tsoratar da ita shiyasa ta sume'
Alhaji yace"kaɗan daga cikin sakarcin kane sufyan!in ba shashasha ba taya zaka bar bacci ya ɗauke ka acikin mota har ka kwana awaje,ko tsoron wani abu ya faru dakai baka ji!salon kaja ma mutane bala'e ko!?
  Ganin ya rufe shi da fada yasa mommy ta 6ata fuska tare da kallon Abusufyan tace"Ka shiga da ita ciki"
  Amsa mata yayi kafin ya wuce da abu cikin ɗakinsu,
  "Dama ae kin saba goya mashi baya!yaron nan yayi laifi me yasa ba zaki bari ayi mashi faɗa ba!ke kina da tabbacin cewar baccin ne ya kwashe shi akan hanya har ya kwana waje?ni ban yarda da zancen nan nashi bama,akwai dae inda yaje,". 
  Rai a6ace Hajiya Ameena tace"ya isa haka Alhaji!kasan irin kalaman da zaka dinga faɗi akan abusufyan ɗina,in ba haka ba,ranmu xai 6aci ne gaba daya,
Tamkar zasuyi faɗa atsakaninsu,ganin haka yasa Haris cewa"pls mommy dan Allah kudaina mana,banaso inga kuna faɗa akan abusufyan,wai meyasa kuke haka ne?daddy kaima ka daina sanya baki akan lamarinshi mana tunda mommy bataso,ba shikenan ba,'.
  Jinjina kai kawai Alhaji yayi tare da kama hanya ya wuce upstairs,haris ya ruƙo hannun mommynshi suka koma don su ƙarasa yin breakfast ɗinsu,


121.
A6angarensu abu da abusufyan kuwa,bayan ya kwantar da ita saman gadonsu,ruwa ya dauko a roba ya ɗebo ya yayyafa mata a saman fuskarta,a hankali ta shiga mutsu mutsun buɗe idanunta,zuba mata ido yayi yana kallon fuskarta cike da tausayinta don yaga alamar jirwayen hawaye a fuskarta kuma ta ɗan kumbura,

Ware idanunta tayi akanshi koda taga shine a firgice ta miƙe zaune saman gadon tana ja da baya,ƙure ma head board ɗin gadon tayi tana faman zazzare mashi idanu,
  Cikin sanyin murya yace"Abuna,am really sorry jiya nasan kinyi kewata sosai,na kwana awaje ban dawo gida ba,nima ba da son raina hakan ya faru ba,"
  Yana kai ƙarshen maganar tashi abu ta fashe da matsanancin kuka tana cewa"ka cuce ni abusufyan,ka yaudare ni!kayi mun ƙaryar cewa zaka daina mu'amala da mata ashe ƙarya kakeyi,har yanzu kana tare dasu,da idona nagani kuma na shaida,hakan ya tabbatar mun da cewar a hotel ka kwana kai da karuwar daka ajiye tana biya maka buƙata,tunda ni ban isheka ba....'
  Hankalin abusufyan ba ƙaramin tashi yayi ba,a ruɗe yace"abu bangane akan me kike magana ba!dan Allah ki fahimtar dani!"
  Cikin shesshekar kuka ta sake maimaita mashi abunda tace
  Hannu ya aza akai yana fadin"innalillahi'wa inna ilaihirraji'un! Ya Allah kasa mafarki nake yi ba gaske ba,abu yau ke da kanki kike jifa na da waɗannan munanan kalaman!abu bani kika gani ba,wlh bani bane ni ban yi mu'amala da wata mace ba,ban haɗu da kowa ba,waɗanda kika gani acikin motar nan bani bane, wasu ne can daban,idanunki ne suka gwada maki ba dai dai ba....'
  A tsiwace tace"Abusufyan!nagama yarda dakai,saboda kai maƙaryaci ne kuma fasiƙi mazinaci.......'
  Bai bari taƙarasa maganarba afusace ya kwashe ta da mari,dafe kuncinta ta tayi ko gizau batayi ba taci gaba da cewa"Ni ka mara da hannunka saboda na faɗi gaskiya?koda yake yanzu har buguna ma zaka iyayi ai saboda ka samu wadda tafi ni,'
Kallonta yake yi yayin da idanunshi sukayi jawur jikinshi har rawa yakeyi saboda tsananin 6acin ran da ta sanya shi,
  Muryarshi akausashe yace"Abu kada ki sake kirana da mazina ci!ban ta6a aikata zina ba arayuwata,ko sunanta bana son inji an ambata balle har nayi yunƙurin aikatata,wlh kika ƙara kirana da sunanta saina sa6a maki......'
  duk wannan budurin da akeyi Hajiya da haris basu sani ba,saboda akwai tazara tsakanin bedroom ɗinsu abusufyan da kuma inda suke,

Harara ta wurga mashi har lokacin hawaye naci gaba da zuba a idanunta huci kawai takeyi saboda 6acin rai,
  daƙyar ta iya furta"Ka sake ni!saboda bazan iya cigaba da rayuwa dakai ba!kayi mun alƙawarin cewa zaka daina mu'amala da mata,kuma har rantsuwa kayi da al'qur'ani cewa in har ka sake kula mata,zaka sake ni saki uku!!!'
  Tsananin 6acin rai da takaici yasa abusufyan ya fashe da matsanancin kuka yana cewa"Zainab baki a cikin hayyacinki!wlh ba ke bace,nasan cewa ba yin kanki bane,aljanune suka shiga jikinki,"
  "Abusufyan ka sake ni!in ba haka ba zan illata kaina kowa ya rasa,"tayi maganar babu wasa a fuskarta,
  "Wlh bazan sake ki ba abu,bazan iya ba,saboda ni banyi maki laifin komai ba,zargina kawai kikeyi amma baki da shaida akaina,dan Allah abu kidaina wannan maganar zuciyata zata iya bugawa in mutu,kiyi haƙuri mu sasanta tsakaninmu nasan zaki fahimce ni,'
  Sam babu alamar sassauci a fuskarta,tamkar yana ƙara tunzurata haka taci gaba da faɗin ya sake ta,
  Ganin yaƙi sakinta yasa ta mika hannu tare da janyo drawer chest,sabuwar reza ta ciro daga cikin drawer ɗinta,
  Hankali tashe abusufyan yace"me zakiyi da ita abu?
    Fuskarta aɗaure tace"zaka sake ni ko bazaka sake ni ba!" shi kanshi sai da ya tsorata da yanayin yadda take magana,ganin yadda hijabin jikinta ya jiƙe sharkaf da zufa,kuma babu zafi aɗakin nasu,ga idanuwanta sunyi jawur dasu luhu luhu,jikinta kuma sai kerma yakeyi,
  Cikin sanyin murya yace"Abu pls ki saurare ni,zan fahimtar dake..kinsan ina sonki bazanso abunda zai cutar dake ba,bazan iya cin amanarki ba abu,
  damƙar hijabin jikinta tayi tare da cireta tayi wurgi da ita gefe guda,a fusace ta Sanya rezar nan abakin tafin hannunta na dama,ta tsarga wurin nan take jini ya soma tsastsafowa daga wurin
  Agigice abusufyan ya yunƙura zai kwace rezar hannunta,dakatar dashi tayi da cewa"Idan har ka kuskura ka matso zan kashe kaina ne!"
  Cikin shessheƙar kuka Abusufyan yashiga yi mata magiya yana roƙonta akan ta daina tsaga jikinta amma kamar yana tunzurata ne,
  Saboda taurin kai da kafiya irin nata ko zafin rezar bata ji ajikinta,kafin yayi wani yunƙurin abu ta sanya rezar asaman wuyanta ta shiga tsarga wurin jini ya shiga bulbulowa,
  A wannan lokacin ne abusufyan ya furta mata saki har ukku batare da saninshi ba,saboda tsoran karta kashe kanta,a gigice yace"ABU NA SAKE KI!NA SAKE KI!NA SAKE KI," 😭

Adai dai lokacin Hajiya da haris suka faɗo dakin kamar an jefo su,sakamakon Sautin ƙarar da abu ta saki da kuma kukan da abusufyan ya saki na fitar hayyaci,zubewa tayi saman gadon asume tana billayi saboda radaɗin rezar daya shigeta,

Gaba daya suka rufar mata suna ambaton Sunanta suna tambayar meya faru,a lokacin shima abusufyan ya yanke jiki asaman gadon ya sume,

Bayan wannan lokacin sai da abu tayi jinya agadon asibiti,inda Allah yaso rezar bata shiga cikin wuyan sosai ba amma ta tsaga fatar wurin sosai,

Bayan an sallameta sun dawo gida anan fa suka hadu su duka a falon gidan don jin abunda ya haddasa faɗan daya shiga tsakaninsu,Zainab bata 6oye komai ba ta basu labari hada sakin da abusufyan yayi mata,hankali atashe Abusufyan ya shiga rantsuwar cewar shi bai sake ta ba,saboda baya acikin hayyacinshi baisan ya furta mata ba,gaba dayansu babu wanda baiyi takaicin faruwan wannan al'amarin ba,musamman mahaifinta baba buzu,tun daga ranar da aka sallameta daga asibiti ko kallonta bai ƙara yi ba,in ma tagaishe dashi bai amsawa,ta 6ata mashi rai sosai,bai ta6a tunanin abu zata aikata abunda ta aikata ba saboda kishi daya rufe mata idanunta,

Abusufyan kuwa har ciwon zuciya sai da ya kusa kama shi a wannan lokacin,ba arziƙi hajiya Ameena tasa aka fitar dashi ƙasar turkey,wurin wata aminiyarta kuma abokiyar kasuwancinta,hajiya maimunatu dake zaune acan instanbul,a wurinta yaci gaba da zama,ta nisanta shi da nigeria ne saboda ta gusar da damuwar dake ƙoƙarin haddasa mashi Ciwon zuciya,

Bayan abusufyan ya koma ƙasar turkey da sati guda kacal,sai ga sayyadi yazo yi ma Abu jajen mutuwar aurenta,tun abakin gate ɗin gidan baba buzu yayi mashi korar kare,wannan abun ba ƙaramin ƙona mashi rai yayi ba,

Ana haka kuma abu ta koma yar gidan jiya,soyayyar sayyadi ta dawo sabuwa fal acikin ranta,ko bacci bata iyayi batare da tayi mafarkinshi ba,ko sallah takeyi sai ta dinga kawo zancenshi acikin zuciyarta, nan fa zuciyarta ta dinga azalzalarta akan son ta sanyashi acikin idanunta gashi an hanata fita ko nan da bakin gate bata iya zuwa saboda mahaifinta dake fushi da ita,da zarar ya ganta awaje zai nufeta afusace da nufin ya bugeta sai ta watsa da gudu ta koma ciki,hajiya da alhaji nuraddeen har haƙuri suka bashi akan komai ya wuce amma yaƙiyi,burinshi ya damƙeta a hannunshi yayi mata mugun bugu,don ya huce haushinta da yake ji,Abu ta ƙumsa mashi baƙin ciki sosai,

Ana haka,wata rana ƙawar abu ta islamiyyarsu wadda suke kira da Maryam ta kawo mata ziyara acikin gidansu,
A falo suka fara gaisawa dasu mommy kafin suka shiga cikin ɗakin abu,anan take sanar da ita cewa Sayyadine ya aiko ta a 6oye don ta kawo mata wayar da zasu dinga gaisawa dashi,'hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma abu ba,
Nokia ce ƙarama maryam ta ciro daga cikin handbag dinta ta miƙa ma Abu,cike da farin ciki ta kar6i wayar,
  Tafiyar maryam ke da wuya,sai ga kiran sayyadi ya shigo cikin wayar,jiki na rawa ta ɗaga kiran tare da yi mashi sallama,
  ko amsa sallamar baiyi ba yace"Hmmmm abu kenan!yanzu kin tabbatar da abunda nake faɗa maki akan Abusufyan ko?ae tun farko saida naja kunnanki akan ki rabu dashi ba mutumin kirki bane amma kika ƙi jin maganata,'
Abu tace"dan Allah mubar wannan maganar,ni ko sunanshi ma bana son ji,yanzu kaine araina,banda burin daya wuce

74 / 80