ABBAN SOJOJI TAKUN TSAKIYA 2 BY BOSS BATURE.txt

Author :  Boss Bature Category :  Arewa Pen

Chapter   48 / 80

141K to 144K   out of 238K words

da ɗaukar wayarta dake ajiye asaman laps dinta,missed calls ta gani na Abbas har kusan shida,duk bata ji ringing ɗin da wayar keyi ba,saboda bata cikin natsuwarta hankali atashe tace"nashiga uku!Ashe abbas ya kira ni bansani ba,yanzu mai zan faɗa mashi,gashi ban hadu da wadda akace Amal ce..."
   fuskarta a yamutse tayi maganar,yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin dialing ɗin numbarshi tabi kiran da yayi mata,tana fara ringing ya ɗaga kiran,cikin sauri takara wayar a kunnanta,saurarawa tayi tana jiran jin me zaice,
   "Ki dawo gida inason ganinki,"
Yana faɗin hakan yayi rejecting ɗin kiran nata,
  Nan fa ido ya raina fata,a kasalance ta tashi motar tare da karya kwana ta miƙi hanyar komawa gida,

*************************
Sosai Amal ke kuka tana ambaton sunan Allah abakinta duk tabi ta zauce,
  Rai a6ace JAHAN yace"yarinyar nan tayi mun shiru!nagaji da jin tsiwarta,duk tabi tayi confusing ɗina,Ayaan kodai ka toshe mata baki ko kuma in dakatar da driving ɗin nan don ni bazan juri tsiwarta ba,"
   cikin sanyin murya Ayaan yace"pls take it easy Jahan,yarinyar nan fa ba ƙaramin jiki take ji ba,ita kanta bazata iya control ɗin kanta ba saboda raɗaɗin ciwon da take ji,"
  Uban tsoki jahan yaja yana faman hura hanci,adai dai lokacin suka ƙaraso da Amal katafaren asibitin sgr,shiga da motar ciki yayi tare da samun wuri yayi parking ɗinta,fitowa Ayaan yayi kafaɗar shi ɗauke da Amal kai tsaye ya wuce da ita cikin asibitin,
  Jahan kuwa zaman shi yayi acikin motar yana jiran ƙarasowar ayaan ɗin,don yace bazai shiga cikin asibitin ba,ya miƙata kawai ya fito su juya,
   Ayaan na shiga ciki da sauri reception nurses suka kar6e ta,tare da wuce wa da ita medical room don a kwantar da ita,
   tsayawa yayi yana faman zarya a wurin,kiran jahan ne ya shigo wayarshi cikin sauri ya ɗaga kiran tare da karata a kunnan shi,
   tunkafin yayi magana jahan yace "what are u waiting for Ayaan!tun da ka miƙa ta awurinsu ka fito kawai mu juya gida,"
   amsa mashi yayi da okey,sannan ya kashe kiran,
  harya juya zai fita daga corridor ɗin,yajiyo muryar wata nurse tana dakatar dashi,tsayawa yayi tare da juyawa yana kallonta,ƙarasowa tayi da sauri cikin harshen turanci ta soma yi mashi magana"sir yarinyar taƙi bari mu dubata,da alama tana da damuwa sosai,akwai wani suna da take ta ambato abakinta,in badamuwa muna so ka shigo daga ciki kayi mata magana,may be ta samu natsuwa,"
   batare da musu ba,Ayaan yabi bayanta har cikin ɗakin da suka kwantar da Amal,sai faman kuka takeyi tana kiran Sunan Aunty amani,tana cewa dan Allah su kira mata ƴar uwarta karta mutu bata sata a idonta ba,
   ganin shi yasa sauran nurses ɗin dake aciki suka ja da baya tare da bashi wuri don ya wuce,
  Ƙarasawa ayaan yayi tare da samun wuri daga gefen gadon da take kwance,yama rasa ta yarda zai shawo kan yarinyar don tayi nisa bata jin kira sai faman sharara kuka takeyi ta cika ko'ina da kukan nata,
   tsawa ya daka mata,aikuwa a firgice ta mayar da idanunta akanshi yayin da jikinta yashiga yin kerma saboda tsoran da taji,
  Yarda ya zare mata idanunshi ba ƙaramin tsoro taji ba musamman launin kwayar idonshi da takasance ash colour,
  Lokaci guda tayi tsit tana faman zazzare idanu,
  dama yayi mata hakan ne don tayi shiru,sassauto da murya yayi tare da cewa"faɗamun menene damuwar?bakyaso ne ayi treating wounds ɗin dake ajikin ki?ko so kike ki mutu ne?
  Cikin shesshekar kuka tace"banso na mutu,inason ganin Auntyna ne,dan Allah ku kira mun ita tazo naganta kafin na mutu,inason ganinta,"
   tsananin tausayinta ne ya kama shi,bin idanunta yayi da kallo ganin yarda hawaye ke kwaranyo daga cikinsu,yarinyar dae ba ƙaramin jiki taji ba da alama,
   ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa"yanzu baki da lafiya,ki bari su duba jikinki,in yaso zuwa gobe ni dakaina zan kira maki auntynki a waya,kin amince da hakan"?
   amsa mashi tayi da eh,sannan ya miƙe tare da yi masu sallama,ya fuce daga asibitin,
   shaf shaf suka bar Asibitin da motarsu,

Koda Amani ta koma gida,abbas baiyi mata faɗan komai ba,ko tambayarta inda taje baiyi ba,hakan ba ƙaramin daɗin yayi mata ba,dama fargabarta kenan karya tuhumeta akan ina taje acikin daren nan,


Tun bayan da sehrish ta koma bedroom ɗinta a wani irin yanayi na kasala ta faɗa saman gadonta tare da kai hannu ta janyo pillow a ƙirjinta tayi hugging ɗinshi sosai,ta jima tana tariyo abunda ya faru tsakaninta da Sgr har lokacin jikinta bai bar kerma ba,duk wani juyi da zatayi sai ta dinga jin tamkar yana a jikinta ne,musamman data rungume filon nan sai taji tamkar shine ta rungumo ajikinta kamar yarda ya faru a bedroom ɗin shi,wani irin tsananin son shi ne da ƙaunarshi da kuma sha'awarshi duka suka mamaye ko'ina na sassan jikinta wannan yanayin ne ya haifar mata da jin matsanancin Sanyi,cikin sauri takai hannu tare da jan bargonta ta lullu6e jikinta duka dashi,daƙyar ta samu tayi addu'ar bacci kuma cikin sa'a baccin ya ɗauketa❤

A 6angaren su Hosana da jahad kuwa ƙin bacci su kayi saboda jiran zuwan Ya Omar ɗinsu sun sa ran zaizo,amma har dare ya ritsa baizo ba,hakan yasa suka fidda rai da zuwan nashi,tuni bacci yayi awon gaba dasu asaman gadon nasu,kowannansu na sanye da sleeping dress,hossana na rungume da pillow yayin da jahad ke manne da drawing book ɗinta asaman chest ɗinta,sai faman sharar bacci suke yi hankalinsu kwance,Rainon Omar,
  Wuraren ƙarfe ɗaya da rabi,jahad ta farka daga baccin da take yi,a hankali ta buɗe kyawawan idanunta tana kallon ceiling,bakomai ne ya faɗo mata aranta ba fa ce,addu'ar da tayi promising ɗin cewa zata dinga tashi tsakar dare tana taya ya omar ɗinsu da kuma ahalinshi, saboda kyautatawar da yake yi masu,hakan yasa take so ta saka mashi ta wannan 6angaren,
Tuna wannan yasa jahad miƙewa zaune daga kwancen da take, hannunta na dafe da zanen fuskar junaid,ɗago da littafin tayi tare da aza idonta akan fuskar tashi, murmushi ta ɗanyi tare da cewa"bansan kowanene kai ba,amma ka kwantamin araina,idan na kalli wannan murmushin kashe zuciyar naka sai inji wani irin sanyi ya ratsa zuciyata,insha Allah kaima zan sanyaka acikin addu'ata,da kowa ma,"
   ta ƙarasa maganar tare da ajiye drawing book ɗin asaman bedmattress ɗin,sannan ta zuro da ƙafafunta ƙasa tare da miƙewa ta sauko daga saman gadon,
    Riga da wando ne ash colour,sai hula data rufe kanta da ita,takawa tayi izuwa cikin toilet,after some minutes sai gata tafito tana yarfe ruwan dake a fuskarta da hannunta,
Wuce wa tayi wurin closet ɗinsu,Hijab ta ɗauko aciki tare da darduma,bayan ta shimfiɗe darduma,ta zura hijabin ajikinta sannan ta kabbara sallah da wannan kyakkyawar niyyar tata,cikin natsuwa ta shiga yin sallar,ba ƙaramin ƙoƙari jahad tayi ba,don sai da ta raba dare tana yin nafilfilin nan,har sai da ƙafafunta suka soma yi mata zogi sannan ta tsagaita tare da sallame sallar,hannayenta ta ɗaga sama ta shiga jera addu'o'i cikin harshen larabci tashiga karantosu ba adadi,
daga cikin waɗanda ta sadaukarwa wannan addu'oin nata harda Sehrish da kuma ya omar ɗinsu tare da ahalinsa da kuma sauran al'ummar musulmai baki ɗaya,ta jima tanayi ƙarshe ma asaman dardumar ta kwanta,kuma ahaka bacci ya ɗauketa,

Wuraren sallar Asubahi,Abbansu ya fito daga cikin toilet jikinshi sanye da jallabiya da alama alwala yayi,wucewa yayi wurin gadonshi domin ya tashi junaid su wuce masallaci,
  Zama yayi daga gefen gadon yana kallonshi sai faman sharar bacci yake yi,hannu yasa tare da ɗan bugun bayanshi tare da cewa"babyn abbansa baccin ya isa haka,ka tashi muje muyi sallah kada time ya ƙure mana,"ko motsi junaid baiyi ba,hannu abban nasu ya kuma kaiwa ya ƙara ɗan bugun bayanshi Yace"junaid ka tashi mana,"
   tun abbansu nayin maganar hankalin shi kwance harya fara shan jinin jikinshi,sosai ya shiga bugun bayan junaid don ya farka amma ko motsi wannan baiyi ba,cikin tashin hankali abban yakai kunnan shi a saitin hancin junaid don yaji ko yana numfashi amma sam babu wata iska dake fita a wurin,da hanzarin gaske ya juyar dashi yana fuskantar ceilling,sannan ya kuma kai kunnan shi saman ƙirjinshi saitin zuciyarshi, gaba daya Abba yaji zuciyar junaid ta tsaya da bugu,
   Cikin ruɗu Abbansu ya shiga furta"innallahi wa'inna ilaihirraji'un!junaid pls ka tashi!in ma wasa kake mun kadaina,bana son irin wannan wasan junaid,
    gaba daya duk yabi ya rikice,hannu ya miƙa tare da ruko bottle watern dake ajiye a bedside drawer wanda suke ajiyewa in case ko wani zai buƙata yasha acikinsu,
   Yatsun hannunshi har kerma suke yi wurin buɗe murfin robar,ɗebo ruwan yayi a hannunshi sannan ya shiga yayyafa ma junaid a fuskarshi,ko gizau junaid baiyi ba tamkar ba ruwa ake yayyafa mashi ba,hankali tashe Abban nasu ya ajiye robar ruwan asaman drawer dinsa,jiki na rawa ya tashi daga saman gadon,ya fito daga ɗakin,sai faman sauri yake yi duk yabi ya rikice,kai tsaye upstairs ya wuce,yama rasa wurinwa zai fara zuwa ya sanarma halin da ake ciki,
  da hanzari ya tunkari corridor din sashen Omar da Sgr kamar zaiyi tuntube haka yake ta faman sauri,
"Abba"! Muryar Marshal Omar ce ta katse mashi hanzarin shi,saboda tsabar ruɗu har abbansu ya wuce shi bai sani ba,
  Yana juyowa yaga Omar nan fa ya tunkare shi hankali atashe yace"Omar dan Allah kaje bedroom ɗina,junaid baya numfashi zuciyarshi bata bugawa bansan meke faruwa dashi ba...."
Hankalin Omar ba ƙaramin tashi yayi ba,ko ƙarasa sauraron Abban nasu baiyi ba ya wuce da saurin gaske ya sauka downstairs direct ya nufi ɗakin abban nasu,
  Akan hanyar zuwan shi bedroom ɗin na Abban nasu ya haɗu dasu Twins tare da fawan da kuma kanal yousouf da sauransu,tunda ya sanar dasu abunda abbansu ya faɗa mashi game da halin da junaid ke ciki,nan fa suka ɗunguma gaba ɗayansu izuwa ɗakin nashi atare,
       Shi kuwa Abban nasu part ɗin babban yayansu ya nufa don ya sanar mashi halin da ake ciki,adaidai lokacin daya shiga bedroom ɗin nashi,a lokacin shi kuma ya fito daga cikin toilet jikinshi sanye da jallabiya,bai jima da tashi daga bacci ba yashiga toilet don tsarkake jikinshi tare da ɗauro alwala,ganin yarda abban nasu ya faɗo cikin ɗakin nashi batare da sallama ba yasa shi cewa"Abba lafiya"?
    Fuskarshi cike da damuwa yace"ina fa lafiya?junaid na can araye ko amace na rasa ganewa,dan Allah kaje ka duba shi bansan meke shirin faruwa dani ne...........'
  
   A ruɗe Sgr yace"bana fahimtarka abba!me ya faru da junaid ne"?
    A ƙagare abban yace"kaje ka ganshi kawai!sam baya motsi kamar matacce..  "
   tunkan yakai ƙarshen tashi maganar tashi,sgr yayi hanzarin kama hanya ya fuce daga ɗakin,shima Abban nasu yabi bayanshi cikin sauri,

Marshal Omar ne zaune agefen gadon su kuma su fawan suna daga tsaye cikin yanayi na damuwa,sun tashe shi yafi a ƙirga har ruwa suka ƙara yayyafa mashi amma ko motsi babu,hakan yasa duk suka sha jinin jikinsu,
  Shigowar babban yayan nasu ne tare da Abbansu yasa suka juya atare suna kallonsu,ganin sgr yasa suka matsa tare da bashi wuri ya wuce,kai tsaye ya hau saman gadon ya ƙarasa har inda junaid yake kwance fuskarshi na fuskantar ceilling,
   Hannu yasa tare da shafa gefen fuskarshi da kuma wuyanshi kafin daga bisani ya janye hannun nashi izuwa saitin zuciyar shi,yana aza hannunshi asaman wurin nan take zuciyar junaid tashiga harbawa da sauri da sauri,
      gaba ɗaya duk sunyi zuru suna jiran jin me zaice tsoransu kar ace junaid ya mutu sai faman addu'o'i suke yi acikin zuciyoyinsu akan Allah karya tabbatar da hakan don bazasu juri rashin shi ba,
    ɗan ƙayataccen murmushi sgr yayi shi kanshi ba ƙaramin kwanciyar hankali yasamu jin zuciyar junaid na bugawa duk da yayi mamakin abunda Abban nasu ya sanar dashi nacewa zuciyar ta tsaya da harbawa,bayan shi kuma da yazo yasanya hannunshi a wurin zuciyar tashi tana harbawa,
  Jin yayi shiru baice komai ba yasa Abban nasu cewa"Son meya faru?junaid yana raye kuwa"?  A ɗan tsorace yayi maganar saboda tsoran Amsar da zata biyo baya,
   Cike da tabbaci sgr yace"junaid fa ba mutuwa yayi ba,he's still breathing,yanzu haka ma bacci yake yi"
   wata irin ajiyar zuciya Abban nasu ya sauke tare da fadin "Alhamdulillah" bashi kaɗai ba hatta sauran ma,
   A hankali sgr ya sanya tafin hannun shi tare da ɗan bubbuga bayan junaid ya ambaci sunan shi"junaid!junaid,"
  Kai tsaye kiran yashiga cikin kunnan shi,aikuwa ashagwa6e yace"pls Abba leave me alone,ni baccin bai isheni ba,tun ɗazu ka takuramin natashi nayi sal.......'bai ƙarasa maganar ba saboda buge mashi baki da Sgr yayi,hakan yasa ya ware idanunshi dake ɗauke da bacci yana kallonsu biji biji,ganin yarda sukayi mashi ƙawanya sun zuzzuba mashi ido,yasa ya miƙe zaune yana faman murza idanunshi don ya shaida su wanene haka,
  Sam bakin abban nasu yaƙi rufuwa saboda tsabar farin ciki,gaza jurewa yayi don haka cikin sauri ya ƙarasa daga gefen gadon ya ɗan russina tare da rungumo shi ajikinshi yana cewa"junaid nashiga tashin hankali sosai saboda halin da ka shiga,ba ƙaramin daɗi naji ba daka farka, da bansan wani hali zan tsinci kaina ba,"ya ƙarasa maganar tare da ɗan janye jikinshi daga na junaid ɗin yace"faɗamun menene ke damunka shalelena,"?
   turo baki junaid yayi tare da cewa"Abba su wanene waɗannan nifa bangane su ba,kuma kana gani wani ya bugar mun baki bakace komai ba,"
   hannu Sgr yasa tare da ƙara make bakinsa,aikuwa rai a6ace junaid yasa musu kukan shagwa6a yana bubbuga ƙafafun shi,hakan ba ƙaramin nishaɗi yasa su ba,
  Cikin shessheƙar kuka yace"wlh bazan yarda ba,duk wanda ya ƙara bugarmin bakina saina rama,"
  Hannu Sgr ya ƙara sawa tare da ɗan bugun bakinshi,a fusace junaid ya ɗaga hannu zai rama,tsayawa sgr yayi yana kallon ikon Allah,
   Junaid kuwa tuni idanunshi sun washe ganin babban yayansu yasa yayi saurin janye hannunshi,sai lokacin ya gane cewa ashe duk sune,
  Cikin sanyin murya ya ambaci sunan shi"babban yaya,"sannan ya juya tare da kallom Omar dake daga zaune agafen gadon yace"ya Omar," binsu yayi ɗaya bayan ɗaya yana kiran sunayensu a ƙarshe yace"meya faru ne nagan ku anan?Abba kodai idona ne ke nuna min badai dai ba,"
  Omar ne yace"junaid mun sameka awani yanayi ne shiyasa ka ganmu anan dukan mu,amma Yanzu Alhamdllh tunda ka farfaɗo,ka hanzarta tashi mu tafi masallaci muyi sallah duk da time ya wuce,"
   kallonsu fawan Omar yayi tare da cewa"kuyi gaba,zamu zo tare da shi,"
   amsa mashi su kayi da toh sannan suka fuce daga ɗakin,
  Su kuma sai da suka jira junaid yashiga toilet ya ɗaura alwala sannan suka fito tare dashi,
  Don tsabar gatanci ma Omar ya goya shi abayan shi kamar wani ƙaramin yaro ahaka suka tafi dashi,duk wannan budurin da akasha Haroon na la6e yana sauraronsu, sam babu wanda yasan dashi daga shi sai short ajikinshi,murmushin takaici yayi tare da cewa"kun makaro,aikin gama ya gama,dole ku rasa junaid,"

***************washe gari**********
Sehrish
A washe gari da wannan yanayin data kwanta dashi ta farka,daƙyar ta iya nufar toilet tayi wanka tare da fitowa ɗaure da towel,shaf shaf batare da 6ata lokaci ba ta kammala shirya kanta cikin school uniform ɗinta riga da wando bayan ta kammala shafe jikinta da body oil ɗinta,bin ko'ina tayi na jikinta tana feshe shi da turare gaba ɗaya hankalinta na akan Sgr,abunda ya faru jiya tsakaninsu,har yanzu ji take kamar mafarkine abun nan daya faru,yarda 6awon ayaba ya ja shi ya sul6e zai faɗi ta taro shi suka faɗa saman gadon,murmushi ta ɗanyi tare da cewa"wani ikon Allah,tunda nake kai mashi fruits ban ta6a kai mashi ayaba ba batare da na 6areta ba na yanka mashi ita ba,kamar yarda nake yanka sauran kayan marmarin amma jiya rabon ayi saina manta na kai mashi ita a haka,lallai 6awon ayaban nan ba ƙaramin aiki yaso yayi ba,da ace ya faɗi bansan wani irin buguwa zaiyi ba,"
   tsayawa tayi da tunanin nata na wani lokaci,ɗago da idanunta tayi acikin mirror ɗin tare da sakin wani irin ƙayataccen murmushi tace"ɗaya daga cikin amfanin 6awon ayaba kenan wanda mutane basu son dashi ba,wato ƙulla allaƙar soyayya,"
  Ƙarasa maganar tayi tare da fashewa da dariya,mayar da flower bomb ɗin tayi ta ajiye shi asaman mirror ɗin,sannan ta ƙarasa saman gadonta inda ta ajiye short hijab ɗinta tare da ɗaukar shi ta zura ajikinta,bata dauki school bag ɗinta ba saboda tana son zuwa kai mashi breakfast ɗinshi before ta wuce school,
Slippers ta zura a ƙafarta sannan ta buɗe ƙopar tare da ficewa izuwa cikin kitchen ɗin,tunkan ta ƙarasa ta hangi Hayaam acikin kitchen ɗin tana taya Azmee girki,nan take taji gabanta ya faɗi,ɗaurewa kawai tayi tare da sa kai cikin kitchen ɗin bakinta ɗauke da sallama,
   Juyawa Azmee tayi daga tsayen da take agaban gass tana kallonta fuskarta ɗauke da murmushi,cikin sauri sehrish ta gaishe ta"ina kwana aunty azmee fatan an tashi lafiya,"
  "Lafiya lou,Alhmdllh yau kinsha bacci ko leƙowa kitchen bakiyi ba,har nayi tunanin cewa ko baki jin daɗine,shiyasa ban tashe ki ba,"


97.
  Sunnar da kai sehrish tayi tare da cewa"Aunty azmee nikaina bansan ya akai nayi bacci dayawa har haka ba,naso ace nashigo kitchen ɗin da wuri don na tayaki aiki,"daƙyar sehrish ta kai ƙarshen maganar tata,ganin yarda hayaam ta zuba mata ido kamar zata haɗiyeta,tana a tsaye gaban choppping board tana yanka vegetables din da zasu yi amfani dashi,
   "Yanzu junaid kike jira ya kai ki school ɗin kenan?naga har yanzu ma bai fito daga bedroom ɗin nashi ba,'
  Kafin sehrish tace wani abu,Hayaam tayi karaf ta amshe da cewa"Junaid kuma?shine drivernta kenan?school ɗinsu babu bus ne"?ta jefa ma azmee tambaya,
  Shiru sehrish tayi batace komai ba don batasan amsar da zata bata ba,
Azmee ce tace"ae da yake bata jima da fara zuwa school ɗinba,har yanzu bata saba da wasu abubuwan ba,amma nan bada jimawa ba,zata fara hawa bus ɗinne,"
  Yatsina fuska hayaam tayi tare da mayar da idonta akan kayan lambun da take yankawa,
  ganin yarda Sehrish tasha jinin jikinta yasa Azmee cewa"ba zakiyi breakfast bane?
  cikin sanyin murya tace"A'a Aunty azmee bana jin yunwa,in naje school zanci acan,amma inaso kafin na tafi in kaima Babban yaya nashi breakfast ɗin in akwai abunda kuka kammala.....'
   Wani irin kallo hayaam ta watsa mata wanda hakan yasa ta ƙarasa maganar adabarbarce,
   "Babu buƙatar ki kaimashi breakfast ɗinshi,ke da zaki school salon kawai shiririta don kiyi late ko?to ki tafi kawai ni zan kai mashi breakfast ɗin nashi," cike da isa hayaam ke magana batare da jin wani ɗar azuciyarta ba,
  Ba sehrish ba hatta azmee

48 / 80