Gishirin Zaman Duniya Book 1 Mrs Bukhari

Author :  Badiat Ibrahim Mrs Bukhari Category :  Read Hausa Novels

Chapter   6 / 33

15K to 18K   out of 98.4K words

sha Allah za ku same ni mai biyayya a gareku. kuma zan hau kan tsanin da
kika d'aura ni akai har zuwa Aljanna. zanje in.Gaishe da su Goggo ne. sai in shiga wajan Bilkisu
za ta sanar da ni dokokin da aka gindayawa surukan gidannan, kamar yanda kawu ya
umarceni. " Toh Sadiya. sai kin dawo.
fita na yi. tare da bin Goggonnina d'aya bayan d'aya ina gaidasu. gabaki d'aya a tsarge na ke.
dan surukan gidan sai wani tab'e baki su ke yi da ganina. wasu ma har barin abinda su ke
gudanarwa su ke yi, su shige d'aki. dan karma mu gaisa. ga habaici da Hasiya matar Dauda
take yi mun a duk sanda zamu had'u kan cewar na gama tsofewa a birni ba miji, daga k'arshe
an kawo ni k'auye. na Auri k'anin bayana, abun kunya. data gama sai ta sa dariya. yauma
hakanne ya faru. dana wuce ta, sai na yi murmushi a raina na ce.
jahilci ciwo wanda ya fi hauka. da sallama na shiga d'akin Bilkisu, bayan ta ba ni izini. zama na
yi a saman kujerarta muka gaisa.
d'akinta ba k'azanta sam a gyare yake tsab ta kunna turare d'an tsinke ya na ta 'kamshi. d'iyarta
tana zaune a kan po ta na bayan gida. ga kuma wainar gero a hannunta ta na ci abunta kuma
da hanun hagu.
Bilkisu ki hanata cin abinci da hannun hagu. sannan bai dace mutum na kan bayan gida kuma
ya na cin abinci ba. d'an murmushi Bilkisu tayi tace.
"lahh ai ni bansan hagu da damar yara ba."
da mamaki na bita da kallo. tana k'ok'arin k'arb'e wainar hannun d'iyar tata. murmushi kawai na
yi na ce.
Dama kawu ne ya turo ni wajanki, ki sanar dani dokokin da ke kan surukan gidannan. dan in
san su.
tace
"Toh doka dai ta farko shine. Kawu matan shi basa d'aura sanwa. duk wata suruka a gidannan
za ta zuba mishi abinci a kai mishi amma sau d'aya a rana. toh sai mu ka yi tsarin da mu ka
kasafta kan mu gida uku. wasu da safe, wasu da rana, wasu da daddare, mu ke kaiwa. kuma
babu fashi. komai ciwo. na biyu kuma shine za ki dinga yin girki da surukarki wato uwar mijinki.

safe. rana,dare. shima ba fashi.
da abincin gandu ake yi. bayan wani rikici daya afku a tsakaninmu. shine kawu ya saka wannan
dokar, cewar kowa ta yi girkinta, shine ko wacce mace ta samu sauk'in rayuwa. Abu na gaba
shine.
wajibine ki bi matan yayun mijinki, duk safiya ku gaisa. akwai fitowa hira tsakar gida, wanda ya
ke wajibi ne. dan sada zumunci. dole yaranmu su kasance a tare. domun akwai d'akin yara
mata. da d'akin yara maza da aka ware suna kwana, dan shak'uwa. kuma baki da wani iko a
matsayinki na matar k'ane sai abinda matan yayu suka zartar akan kowa ma. wannan su ne dokokin wannan gida.
murmushi na yi mai k'unshe da ma'anoni da dama wanda na barsu a raina. godiya na yi mata ta
fito, zuwa d'akina.
Goggo Asabe ce a gaban mai gari su na k'arashe zancan su.
"ni hak'urin da na ke ta nema ka yi mun shine. Abar yaronnan ya Auri Khadija. kar a tauye musu
hakkinsu. Aure kuma, ai ba Aliyu bane ya ga mace ya ce ya na so ba. ni ma kaina fa na fi son
Khadija." mai gari ya ce.
"maganar gaskiya Asabe. ba na jin zan iya sauka akan wagga baka. Aure ko? na amince ya
Aure ta. amma in ya Saki waccan 'yar barikin daya Auro. in kuwa ba haka ba. wallahi sai dai a
hak'ura da Auran. dama yarinya ta na da manema. sabida al'kawarin da ke kanmu ne yasa ban
ba ma kowa dama ba" Goggo Asabe gabaki d'aya kanta ya chaza sosai. kuma ta san Aliyu zai shiga tashin hankali mai
yawa in aka ce yau ya wayi gari ya bar Khadija. cikin sauke murya tace.
"Toh ranka shi dad'e, ni zan koma. duk abunda mu ka yanke da 'yan uwa na, da shi kanshi
k'usar yak'in in ya dawo, za ka ji a bakin mai dambu. Maganar saki daya dawo, kafinma ya
shiga d'akinta ta juya mishi kai, zan sa ya sauwak'e mata. Ka sauraremu." ( hmm maman
Yaseer ke fa kinji) "Toh madallah ina saurarenki Asabe, yaro Allah ya dawo dashi lafiya."
sallama ta yi mishi ta fito.
ta na tafe ta na ta faman tunani akan wannan lamari da komai ya ke son lalace mata.
"duk Bala ne ya ja mun wannan tsiyar. ya k'ak'aba ma yaro Auran dole, yaro da wacce ya ke so
shi kuma. ni wannan kafiya ta me gari ta ishe ni wallahi"
duk maganganun nan ta na yin su ne, ita kad'ai a hanya. har ta iso gida. ( Oum Shuraim tace,
"kya ji da shi dai )

Sadiya
wunin wannan ranar cikin nasiha Goggo Hansatu ta k'arar mana da yinin.
washe gari ma ta d'aura daga inda ta tsaya. na saki jiki na sosai babu laifi.
kullum da safe ina zuwa gaishe da Goggonnina da kawu da matan shi. haka duk wacce na
had'u da ita a tsakar gida, ni dai zan gaishe su. wasu su amsa, wasu su yi kunnen uwar shegu
da ni. Ina jiyo su, suna hirar tsakar gida tare da shewa. Amma ban tab'a ko lek'awa ba.
Allah ya kawo mu ranar Dawowar Aliyu. Goggo Hansatu tun safe ta yi ma matan gida sallama
ta kama hanyarta. Ni kuwa a ranar na ci kuka har sai da idanuna su ka yi wani mummunan
kumburi. ji na ke yi tamkar in sa hannu na a ka, in rintima uban ihu, ko zan ji sanyi a raina. Wani
irin suya zuchiyata take yi mun.

bayan na share hawayena ne, sai na mik'e na duba agogo na 'karfe biyu da rabi na rana.
kitchen na shiga, na kunna ritso na d'aura ruwan tea. ina tsaye ya tafasa. a cup na zuba wanda
zan sha. sauran kuma na zuba a tea flase na barshi a kitchen d'in.
dai dai zan fito daga kitchen kenan. sai ga Fatima yayar.Aliyu ta shigo da sallamarta. cikin
fara'a na tarbeta. amma kuma sai na ga ta turb'une fuskarta. babu yabo babu fallasa ta amsa
gaisuwata. na ce da ita.
mu shiga daga ciki mana Fatima, naga kin tsaya daga nesa. Bud'ar bakinta tace.
"Fatima kuma, hala kin manta ni Yar Mijinki ce? Koda ma, mun yi tunanin ganin rashin d'a'a a
wajan 'yar boko. dama d'abi'arku ce rashin kunya da fitsara. Goggo na jiranki ki fito za mu je
d'auko K'anina mijinki kuma a filin jirgi. cijewa na yi. tare da bin bayan Fatima da kallo wacce ta
fice fuu. murmushin ba'kin ciki kawai na yi. kaya na sake daga atamfa zuwa material mai taushi. d'inkin riga da siket wanda ya kama ni ya
zauna.daram a jikina. kirjina ya d'an fito ta saman rigar har ana ganin tsagun daya raba
mamana biyu. gyalen kayan babba ne sosai kuma yana da kauri. yane shi na yi a kaina tare da
kama shi da pin. turare na fesa mai cool k'amshi. takalmi na mai tudu na d'auko na sa kalar
kaya na. ni kaina da na dubi madubi nasan na yi kyau sosai. amma gabana sai fad'uwa ya ke yi.
ga maganar da Fatima ta caka mun yana ta dukan zuchiyata, ga ganawa da Aliyu da zanyi.
Shima sai fad'ar mun da gaba ya ke yi. Da hanzari na fito tare da sa ma k'ofata kwad'o na rufe
ruf.
A babban tsakar gidan na samu su Goggo. ita da kawu, da Anas, da Fatima, Sai wata yarinya
fara da ban santaba. Amma kuma naga ta na watsomun wani mugun kallo.
"Ku yi hak'uri in na b'ata muku lokaci."
Kawune kawai ya ce.
"Babu komai Sadiya. Khadija ma yanzu ta zo."
kallon ta na yi muka had'a idanu. harara ta sakar mun. Sai yanxu na gane ta. Itace yarinyar da
Aliyu zai Aura.
ta b'angaren khadija kuma gabanta ne ya fad'i da ganin kyau da tsarin sura irinna Sadiya. ta ke
ta shiga kokawa da hawayen da ya ke shirin zubowa ya kunyatata. jikinta ne yayi sanyi, tare da
karayar zuchiya..Amma kuma data tuno Aliyu na dawowa zai sake ta. kafin ma ya shiga
d'akinta. sai ta yi dariyar mugunta kawai.
Sadiya

D'unguma mu ka yi baki d'ayan mu. mu ka hau Babur dan zuwa kan iyakar da za mu samu
motar zuwa sokoto.
na sha wuya a wannan hanya. mai tarin kwazazzabai. kafin mu sauka na yi wurjanjan dani.
kai tsaye mu ka shiga motar cikin garin Sokoton Shehu.
ina zaune a mota, gabana sai fad'uwa ya ke yi. kuma ni kaina ina jima kaina kunyar in kalli Aliyu
A matsayin mijina. Babba dani. Sannan ina fargabar irin amsar da zai yi mun. da ma irin
Rayuwar da za mu shinfid'a, mai dad'i ko akasinta.


mrs Bukhari ce

*GAWURTATTU BIYAR,5TAFIYAR TA MUSAMANCE*



1, *MU GANI A ƘASA..*
_Ummu Affan_

2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*
_Ummu Maher_

3, *GUNTUN GORO..*
_Mom Islam_

4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*
_Mrs Bukhari_

5_ *AUREN WATA TARA‍❤️‍*
_Miss Hajo_


Guda ɗaya N300
Guda biyu N500
Guda uku N600
Guda huɗu N700
Guda biyar 1k

*ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR*


Fatima Rabiu Sunusi
0037219728
StanbicIBTC Bank.


Shaidar biya tanan
0810 433 5144


Masu tura katin MTN
0814 179 9224

...........‍❤️‍....

*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU

Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number 08141799224



*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*

*INA MATAN MASU AMSA SUNANSU NA MA, INA UWAR GIDA, INA AMARYA, INA 'YAN
MATA 'YAN KWALISA?* *HAK'IKA DUK MACEN DATA ISA, SAI DA K'AMSHI DA GYARAN JIKI
BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI. 'YAR MUTAN KATSINAWA NAZO MIKI DA SIHIRTACCEN
K'AMSHIN DA ZAI JIJJIGA MIKI OGA, TA YANDA OGA ZAI LIK'E MIKI.* *SUNAN WANNAN
K'AMSHIN MANNE MATA, MAK'ALE MATA* * *WASU KUMA SUKAN KIRASHI DA D'AYE
MANNA* 'YAN MATA AKWAI NAKU HAD'IN NA DABAN.

*AKWAI KULACCA TA SUDAN*
MAI SIRRIN K'AMSHI DA GYARA FATA, GA UWA UBA SA LAUSHIN JIKI, DA KUMA
DAWWAMAR DA K'AMSHI A JIKIN FATA.

*AKWAI SIHIRTACCIYAR HUMRA, 'YAR SUDAN*
WACCE AKAI MA LAK'ABI DA 'YAR BAIWA MAI ABUN MAMAKI.
ITA KUMA TADA SHA'AWAR ME GIDA TAKE YI, TARE DA K'ARA DANK'ON SOYAYYA, DA
KUMA DAWO MA DA MATA MARTABARSU. UWA UBA AN HAD'ATA NE DA ITATUWAN
GYARAN JIKI, DA KUMA SIRRIN K'AMSHI MAI MOTSO SHA'AWAR DUK WANDA YA
SHAK'ETA.
BAN TSAYA IYA NAN BA.
AKWAI TURAREN KWANCIYA, WANDA AKE SHAFAWA A MATSE MATSI, DA SAMAN CIKI.

KE DAGA JI KINSAN AKWAI AIKI, DAN MAI GIDANKI SAI K'ARA SONKI DA KUMA MAK'ALE
MIKI.

INA DA TURARE D'AN GASKE NA TSUGUNNO, MAI FARFAD'O DA MARTABA DA KIMAR
GABAN MACE, K'AMSHI YA DAWWAMA A WAJAN, YANA SAUKAR DA NI'IMA, YANA KASHE
INFECTION, YANA MACE MACE TA HAD'E TSAM. YANA K'ARA D'AND'ANO.

INA HAD'A TURAREN FANT 'YAR UWA, WANNAN MA WANI SIRRINE NA MUSAMMAN


TA B'ANGAREN KAYAN MATA KAMA DAGA NA NI'IMA, NA INFECTION,DAMA NA MATSI IRI
IRI. DA DUK WANI MAGUNGUNAN MATA A KWAI SU, 'YAN GASKE, MRS BUKHARI 'YAR
MUTAN KATSINAWA TA ZO MUKU A SHIRYE TSAB.

AKWAI SETI NA MAI JEGO, WANDA YA K'UNSHI KOMAI DA KOMAI A CIKI.

KANA AKWAI SETI NA AMARYA, ITAMA NA MUSAMMAN NE, YANA D'AUKE DA
INGANTATTUN MAGUNGUNAN JIJITA ANKO.
'YAN MATA WANDA SUKE SHIRIN SHIGA DAGA CIKI KUMA AKWAI NAKU SETI NA
MUSAMMAN.

AKWAI MAN DILKAR GYARAN JIKI NA AMARYA, DA SABULUN AMARE NA MUSAMMAN
*BANGAREN TURARUKAN WUTA NA INA NAN*
*TURARUKAN D'AKI, DANA KAYA, DA TURAREN GASHI, DA TURAREN WANKA, TURAREN
MOPPING, TURAREN WADROPE, TURAREN BAYAN GIDA. KUJERAR TSUGUNNO,
KABBASA, DUK INA SIYARWA. DOMUN NEMAN K'ARIN BAYANI TU TUNTUB'I MRS
BUKHARI 'YAR MUTAN KATSINAWA. 08179523215
saina ji ku
*GISHIRIN*
*ZAMAN*
*DUNIYA*
_Daga Al'kalamin_
_Badi'at Ibrahim_
( Mrs Bukhari Ibrahim B4B)


Labari wanda yai duba kan gwagwarmayar mata a duniya. Da irin gudummawar da ilimin mace
ya ke bayarwa ga al'umma. Da kuma rawar da ilimin mata ke takawa a cikin gidajen Aure.

Kashi na 1
Babi na 13~14

Sultan Abbakar the 3rd international airport Sokoto State

A tsaye ya ke. ya na ciniki da masu taxi d'in da ke sana'a a bakin get d'in Airport d'in.
dogone sosai, ba irin tsayinnan mara tsari ba. domun faffad'an kakkauran k'irjinshi ya k'awata
tsayin na shi. Kasancewar su Goggo Asabe irin dogayen sakkwatawanne sosai. domun
mahaifin Sadiya har wani doron tsayi ya ajjiye. Haka mahaifinsu mai Hula ya ke. shi tsabar
tsayinshi ya wuce misali. Aliyu Fari ne sosai, irin fararen fatarmu na nan gida Najeria. shi ba siriri bane. kuma ba mai k'iba
bane. sai dai ya na da zubin gwarazan maza. kan shi babu tarin suma. saisayan aski ne a

kanshi. siririyar fuskarshi na d'auke da k'asumba da gemu me yawa, wanda kuma ya ke shan
gyara, da taza a kai a kai. yana da hanci daidai misali amma ba kamar biro ba. bakinshi kuma,
madaidaicine. idanunshi su na da tudu ta saman idanun na shi. sai dai a cikin asalin idanun. ba
su da girma sosai. gira da gashin idanunshi, irinna mazan mu na gida Najeria. wato dai dai da
misali.
Sanye ya ke cikin Farar jallabiyya mai kyau sosai. kanshi sanye da hular ustazan larabawa
wacce ake kifata a kai. a gida najeria ma ana samun irenta da mata ke yi mata sak'ar lilo.
sannan ana samun 'yan kantinsu a kasuwa.
k'afarshi na sanye da wasu slipas mai yatsa, bak'i. wanda ya fito da zara zaran siraran
yatsunshi masu kyau.
yana rataye da k'atuwar jakar baya. da akwatinshi trolla, sai kuma jakar tsaraba.
bayan sun gama daidaitawa da mai taxi zai shiga kenan, motar su su Goggo Asabe ta iso.

Sadiya

jiki a mace na sakko daga cikin motar nan. zuba ma wanda Goggo Asabe ta kira da K'usar yak'i,
idanu na yi. ina karantar shi da kyau. daga sama zuwa k'asa na kalleshi. gaskiya in na kushe
Aliyu ban kyauta ba. domun yanda na karanceshi, matashine mai hankali da nutsuwa. kuma
bashi da k'azanta a ido dana ganshi. murmushi ya yi yace.
"Ahhh Baba ashe kunsan zan dawo ne?
da sauri ya iso wajan Kawu ya rungumshi. suna murnar ganin junansu. Goggo Asabe tace.
"wato kawunka ya debe ma hankali, wajanshi ma ka soma zuwa ko?
murmushi mai burgewa Aliyu ya yi ma Goggo Asabe. bai ce komai ba ya rungumeta yana
lumshe idanunshi. Fatima da Khadija kuwa sai dariya su ke yi.
ni kuwa ina cikinsu tsamo tamkar wata bare. Gabana sai dokawa yake ta faman yi.
"Barka da zuwa Aliyu."
cewar khadija. harda wani sassauta murya dan ta yi taushi.
cikin dariya ya ce.
"Dijengala ke ce ki ka girma haka? Ai ko a hanya na ganki sai dai in wuce."
dariya su ka yi duka. Fatima tace.
"Ai kaine ka girma Aliyu. ji wata k'asumba daka tara. sai kace babban mutum. kuma ka sake yin
fari.
"Yaya Fatima kenan. ina yaran?"
"Suna gidan su Kawu na barosu acan.
Goggo Asabe ta ce.
"Ni kaina sai na ga ya mun wani bawai. ji uban gemu kamar soson waya k'usar yak'i. Ai wani sai
ya d'aura irin manyannan ne. Yaro da kai da d'anyan jininka ka zama wani babba."
kawu ya ce.
"Ai kuwa yayi kyau sosai. Sai dai dole zai canja mana. Shekaru hud'u fa. malam Iliya ne ya
sanar damu ranar da za ka dawo. ya ce kun had'u a Umara da ya je."
kai ya girgiza ya ce.
"Gaskiya ne. har gidan da muke ya je.

carab mu ka had'a idanu dashi. na ji matuk'ar kunya daya kamani dumu dumu ina kallonshi. Da
sauri na kawar da kaina.
yamutse fuska yayi, tare da d'aura d'an yatsanshi a gefen kanshi. Alamar tunani.
" Kawu wannan ba Anty Sadiya bace. Ta gidan Baffana?"
mai taxi ne yai musu magana da ya ga hirar tasu tak'i ci tak'i cinyewa.
"Malam ka fa barni a tsaye.
da sauri Aliyu ya juya, wajan mai taxi d'innan. yana mai bashi hak'uri. Sun tattauna ba mai
yawa ba. Sannan ya juyo ya ce.
" Kawu muje ko?"
Dawowa yayi zai 'dauki akwatin ya sa a bayan mota.
Goggo Asabe tayi tarab tace.
"Ke Sadiya. Aike ya dace ki d'aukar mishi. Ko a gabana ma zaki nuna mun ke 'yar duniya ce?"
wani abune ya tokare mun mak'oshina. Murya a sanyaye na ce.
"Kiyi Hak'uri Goggo.
take idanuwana su ka kawo ruwa. Ajjiyar zuchiya na ke ta saukewa a hankali. Aliyu da bai
fahimci Abinda Goggo Asabe ta ke nufi ba. Na hango rashin jin dad'i a fuskarshi.
Akwatin na d'auka. Har zuwa gaban motar. juyawa na yi, na d'auko jakar na ajjiye a kusa da
akwatin.
Mai taxi ya zuba komai a bayan mota.
Aliyu da kawu. suka zauna a gaban mota.
mu kuma mu na bayan mota dukkan mu.
Hira su ke ta yi, cikin raha da burgewa. Ni ko kaina a sauke ya ke, ina share hawayen da na
kasa dakatar da shi.
Ashe Aliyu ya na kallona ta glass d'in hannun da yake ta waje. Kasancewar ni ina zaune ne a
bak'in kofar shiga. Sabida sai da kowa ya shiga. Sannan na shiga gudun kar in yi wani laifin da
za'a sake tsinka ni.
kai ya girgiza tare da cije lebe.
Yace Baaba. Yaushe Anty Sadiya ta zo ne? ni fa ba dan jini ba.

6 / 33