Author : Badiat Ibrahim Mrs Bukhari Category : Read Hausa Novels
da kuzarin da zaka iya rik'e mace, dan haka ka sake ta, taje ta samu wani namijin can
ta aura." cikin jin tsananin zafi, jikinshi har rawa yake yi, wata jijiyace guda d'aya ta tsaya mai a tsakiyar
goshinshi.
"Tunda saki ku ke nema sai ku biyani duk abinda na kashe mata, ta kuma biya ni sadakina."
mik'ewa yayi ya fice a masallacin tsabar b'acin rai ko gani sosai ma ba yayi.
sai zuwa can kamilu ya fito, bayan ya gama tausar mai gari wanda ke cewa za su je kotun
musulunci a Zamfara.
Aliyu na tsaye a k'ofar gidansu kamilu, a wajan kamilu ya iske shi, idanunnan sun yi jawur sun
cika da ruwa, damma jarumine da sai yayi kuka, domun abunda ya ke ji a cikin zuchiyarshi
bazai kwatantuba, babban abunda yafi b'ata mai rai a cikin zancan Khadija shine kalmar rashin
kuzarin da mahaifinta ya jefeshi da shi.
mrs Bukhari
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. ♀️*
1, *MU GANI A ƘASA...*
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*
Badi'at Ibrahim
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*❤️
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300
*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya
0810 433 5144
Masu tura katin MTN
0814 179 9224
Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* ❤️
Instagram links
https://www.instagram.com/p/CgPTv1-oML6/?igshid=MDJmNzVkMjY=
Facbook group
https://facebook.com/groups/463653111781414/
Telegram links
https://t.me/+xYZCR9JY-aMzNDFk
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google
za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
G Z D
MRS BUKHARI
41~42
"Aliyu da baka biye mishi ba, kai kan ka kasan waye mai gari, kuma ko babu komai kana auran
d'iyarshi ne." Aliyu ya dubeshi da jajayen idanunshi yace.
"Ya riga dama ya gama tunzura ni a bisa maganar makaranta, ni inason kawo haske, shi yana
kare kujerar shi."
"Toh yanzu yace kotu zai maka k'ara saika sakar mai d'iya."
"Zan ga wanda ya isa ya sani dole, jahilci ne zai sa ya kaini kotu, acan al'kalin da yake
girmamawa ya ji komai daga gareshi." Kamilu yace.
"Mu bar wannan, tafiyar tawa na d'aga ta zuwa k'arshen shekarar nan da muke ciki. Ya kuka yi
da Baaba kuwa?" Ajjiyar zuchiya Aliyu ya sauke, labarta mai komai yayi."
"Ina jiran me zata ce yau ne, jiya ban ko iya runtsawa ba, tsabar damuwa Kamilu. Daga nan
wajan Baaba zanje dan jin me zata ce mun, ni fa ko bata bani umarnin zuwa dawo da Sadiya
ba, zanje kamilu, domun ya kamata abu sahunta" Kamilu ya dafa shi yace.
"Duk yanda kuka yi da Baaba zanji, inta kama ni inje in dawo ma da'ita sai in je. Maganar
makaranta ka ajjiye a gefe tukunna."
Sallama su kai da juna, kamilu ya shiga gida, Aliyu ma ya nufi hanyar gidan.
da Yaya Kabiru, da Yaya Sulaiman yaran Goggo mariya kuma manya a gidan ya ci karo, su na
tsaye suna jiran shigowar tashi.
Su Yaya Sajida, da Yaya Rukayya, da Yaya Safiya, yaran Kawu ne su ka shigo gidan da gayyar
yaransu. A wajan su Yaya Kabiru su ka tsaya.
"K'aramin taro mazan gidan su ke yi ne? Banga Dauda da Anas ba." Cewar Yaya Sajida data
kasance Babba a mata a gidan. Kabiru yace.
"Hmmm wannan shashashan yaron ne ya ajjiyemu a masallacin gidan mai Gari, sabida tsaurin
idanu wai mu zai dinga koyarwa a masallaci, sai kowa ya bar abunda ya ke yi ya zauna yana
sauraranshi, kuma wai har matan mu duk zai had'a ya koyar." Baki Ya Sajida ta tab'e tace.
"Ada mu Bamu san k'aninmu da rashin kunya ba, har saida ya auro 'yar boko, mai bud'ad'd'en
idanu, wacce bata ganin kowa da gashi, shine ya zama mara kunya. Amma za mui maganinta a
cikin gidannan damu take zancan." Yaya Ruk'ayya tace.
"Sadiya fa ance ba k'aramar 'yar duniya bace, ita da take aiki a cakud'e da maza, suna gugarta
tana gugarsu." Runtse idanu Aliyu yayi, domun gangar kishin matarshi ce ta kad'a a zuchiyarshi,
har sai da zuchiyar shi ta girgiza. 'Daurawa tayi da cewa.
"Ba dole Aliyu ya zama mara kunya ba, Hmmm nikam na shiga ciki." wucewa ta yi b'angaren
kawu mahaifinsu. Yaya Safiya tace.
"Amma ba daidai bane a sama Sadiya k'ahon zuk'a haka ba, Sadiya fa ba bare bace a
gidannan, itan jininmu ce, dan k'asa ta rufe ma mahaifinta idanu, sai kuma d'iyar da ya haifa ta
zama mujiya a cikinmu, dan kawai ta yi Ilimin zamani?" Ranta bai yi da'di ba da taji ana yab'ama
Sadiya irin wad'annan muggan alkaba'en. Aliyu dai yana jinsu bai ce musu komai ba, Su Yaya
Kabiru su ka mai tatass a tsaye a wajan. A wajan su ka wuce suka barshi, yana bin takunsu da
kallo, baki ya ciza kawai, shi yayi musu uziri dan yasa jahilci ke d'awainiya da su, amma ba
k'aramin tausar zuchiyarshi yayi ba shiyasa bai tanka musu ba, domun in cewa yayi zai tanka.
ba za'a kwace lafiya ba, abunda ke gabanshi shine zuwa dawo da Sadiya." Ahankali ya juya
zuwa d'akin su.
Goggo na zaune ita da Fatima, yai sallama ya shiga, waje ya samu ya zauna, Goggo ta bishi da
Harara.
"Baaba taron me za'ayi a gidannan da ni ban sani ba? Naga su Yaya Sajida har sun hallara.
ciki ciki tace.
"Sabida maganar Fatima da Ramatu ta wajan Iya, sai kuma taron cikin gida da aka jima ba'ayi
ba, Iya ma tana hanya, in ta zo kayi k'ok'arin had'amu fad'an da zata tsine mun, kai kuma sai
kasa ruwa a k'asa kasha. k'asa yayi da kanshi wanda ke yi mishi ciwo sosai.
"Baaba toh da inason tafiya Kano yau sabida dawo da Sadiya."
"Toh Sarki na Sadiya, babu inda zaka je baka da lafiya, tafiya ma da kyar kake yi, amma a haka
za ka yi zaman mota, ciwon da aka cema baya son zafi, da jijjiga." murya cikin sanyi, cikin
tsantsar biyayya yace.
"Baaba toh ko akwai wanda kika wakilta dan zuwa bikon nata? Juna biyu gareta na fi son tana
gabana ina kulawa da su, tunda hakkinane yin hakan." Goggo tace.
"Kai fita idanuna ka ji, Sadiya anan dai babu mai zuwa bikonta, domun babu mai k'aunarta balle
ya ji kewar rashinta. Af ni na manta, mai dambu da mai gari, harma da yardar khadijan dan a
gabanta akai komai. So suke ka saki khadija, tunda yanzu baka da lafiya cikakkiya." wani
b'oyayyan murmushi ya saki ta gefen bakin shi kawai. "Mai garin ya yi mun magana yau, mun gama magana, zaki ji komai k'ila a wajan mai dambu
ma."
Sallama su ka jiyo daga bakin k'ofar d'akin nasu. zainaba, da zuwaira yaran Fatima ne su ka
shigo a guje. Babansu yana tsaye a bak'in k'ofar d'akin, Aliyu yace.
"ka shigo Baban Ibrahim." shigowa yayi a mugun kunyace, kasa had'a idanu da kowa yayi,
Fatima ma sauke kanta k'asa ta yi, yaranta na jikinta suna wasanninsu, cikin girmamawa ya
gaishe da Goggo, a da'kile ta amsa mishi"
"Dama yaranne su ka ce in kawo su wajan umman su, jiya ko bacci ban samu yi ba, sai kuka
suke yi." Aliyu yace.
"Dama ina da shirin zuwa in sameka har gida domun naji, menene Yaya Fatima tayi ma har ka
yanke d'anyan hukuncinnan? Ga yaranku har biyar." Goggo ta mik'e ta ja Fatima tace.
"Mu je Fatima, yara kuma in zaka wuce ka wuce da su, ka kaima mahaifiyarka ta rik'esu." Fita
su ka yi, Aliyu kuwa dan kunya kamar zai nutse a wajan.
"Aliyu wallahi daidai da sau d'aya Fatima bata tab'a kwatanta yi mun biyayya ba a
zamantakewarmu, kwanciya da ita in zan yi, sai ta nemi shinfid'amun dokoki masu tsauri, har
mahaifiyata Fatima take yi ma rashin kunya, har kuka mahaifiyata take yi akan Fatima, hakan
ne ya sanya yayyu da k'annena basa mutumci da ita. Abunda ya faru har na sake ta shine,
tunzurani tayi, dan kawai nace aure nake so in sake, Aliyu a sanadiyyar Fatima har matan
banza nake bi dan in biya muk'atata, ni namiji ne wanda bazan ma iya kwana biyu ba tare da
d'umin matata a jikina ba. Daga cewa zan yi aure, sai Fatima ta d'auko ruwan zafi ta shek'amun
a jikina, cikina ma akwai inda ruwan ya k'onani, Allah yasa ruwan bai tafasa bane." Baban
Ibrahim ya d'aga rigarshi ya nuna ma Aliyu wajan k'unan k'aton k'una an barbad'eshi da
maganin galgajiya. Baban Ibrahim ya d'aura da cewa.
"kuma haka ta zage ni ta uwa ta uba, hakanne yasa na saketa saki biyu, ni na manta shaf
cewar akwai saki d'aya a baya" Shiru Aliyu yayi, domun ya girgiza da rashin kunyar Yayar tashi,
ya tsinke da lamarin, a hanakali Aliyu yace.
"Baban Ibrahim abunda ka aikata na zina laifine babba, ka yi kuskure da har ka bar xuchiyarka
ta rinjeyi gangar jikin ka wajan aikata zina, dan kawai mace. Mai yasa ba ka d'auki azumi ba, ko
kuma ka bari sha'awar ta kashe ka ka huta ma baki d'aya? ka yi gaggawar tuba kaita istingifari
Allah zai yafe ma kuskuren daka aikata, amma ka dage wajan adda'a kar dattin zina ya hau kan
yaranka da basu ji ba, ba su gani ba, ka koma da yaranka, kai musu tarbiya mai kyau, bayanin
da kai mun na ire iren rashin mutumci da Yaya Fatima tai ta tabkama, zan sanar da su in mun je
wajan zama, sirrinka kuma ka d'auka tamkar ka hak'a rami ne ka zuba shi." Godiya sosai yai ma
Aliyu, a tare su ka fito daga d'akin Goggo, Aliyu yai b'arayin Kawu, shi kuma ya na ri'ke da
hannun yaranshi ya fice a gida.
Da Sallama Aliyu ya shiga falon, kowa ya hallara Iya yanzu isowarta kenan, ganin Aliyu shi
kad'ai ne yasa tace.
"Sadiya ma ta zo ayi da ita, ai ita ba suruka bace." Yaya Sajida ta tab'e bakinta ta kau da kai
gefe. Aliyu kuma bai ce da Iya komai ba, dan baisan me zai ce ba. Kawu yayi k'arfin halin
mik'ewa ya soma jawabin abunda ya hassasa wannan taron na gaggawa, tare da ba Aliyu
umarnin bud'e taro da adda'a" cikin nutsuwa ya dinga ragargazo adda'a da harshen larabci,
bayan ya gama adda'ar ne Iya tace.
"Toh manya manyan abubbuwa sun faru, na farko shine batun b'atan mijin Rahama, da kuma
batun Sakin Fatima, wanda shi Sulaimanu yai k'ok'arin zuwa ya sanar da ni.
Ku mata matan bari in soma daku, Aure ba hauka bane, hakurine, ki sani ko kin kaso auranki
kin dawo gida, wani namijin zaki aura, dan ba uwarki zaki aura ba. Fatima za mu baki dama
muji me ya had'aki da mijin naki, ko kuma Asabe ta cika burinta na ganin kin dawo bazawara?"
Fatima ta shiga nuk'u nuk'u na rashin gaskiya aka yi a ka yi ta k'i ta yi magana. Aliyu ne ya
d'aga hannu ya ce.
"Ina da magana" Dama aka bashi, nan ya basu labarin rashin mutumcin Fatima tiryan tiryan, sai
sirrin mijinta ne kad'ai bai yi magana a kai ba.
Nan kowa ya shiga tafa hannu da karkata kai, ai kuwa nan Iya ta caccaketa iya son rai, Fatima
taci kuka ta k'oshi.
"Sai maganar Rahama, tsakani da Allah ni inaso Rahama ta bar gabana ita da yaranta, Safiya
babbar ce kad'ai za mu ci gaba da zama da'ita, Sauran yaran tara da ita cikon na goma za su
zauna anan, dana koma zan sako su a abun hawa su tawo, za so mata da kayanta. wallahi in
na ci gaba da zama da ita a gabana tausayinta ne zai ajalina, abun yayi mata yawa kai jama'a.
Kuka iya ta fashe musu da shi, harda sheshshek'a. Kowa a falon ya amince da dawowar
Rahama da yaranta gidan, Aliyu ne yace yana da magana.
"Iya ni a ganina Yaya Rahama ta ci gaba da zama dake zai fi, duk wani tallafi da za mu yi mata,
tana gaban naki za mu yi mata. Iya yaran nake dubawa, suna makarantar arabi da boko, kuma
ita ma tana d'an aikinta, Iya ki barsu a gabanki, hatsi dai zan taimaka muku dashi, na cefane
kuma su Yaya Kabiru sa dinga harhad'a muku. Ilimi na da amfani Iya musamman ilimin 'ya
mace" nan fa aka yi ca a kan Aliyu da maganganu, harara Goggo ta zuba mishi, tasan duk
wannan maganar ilimin da ya ke yi dan Sadiya ne. Iya ta ce.
"Ya isa hayaniyar haka, yaro ya fad'i gaskiya kuma sai na ji na gamsu, dan yaran ko basu tsira
da komai ba sa tsira da ilimi, kuma zai rik'esu a gaba. Dama rashin abincinne yake tayar mun
da hankali, kuma duk laifin Sulaimanu ne." Kawu ya sauke kai ya dinga ba iya baki.
a haka dai aka gama wannan taron kowa ya kama gabanshi."
Sadiya
Babur d'inmu ne ya sauka a k'ofar gida, da kyar na sakko, dan ciwo ya sake tsananta fiye da na
da ma, marata sai karta mun ciwo take yi, ga jiri, da bushewar baki duk ni kad'ai. Sallama mu ka
yi a cikin gidan. Ba kowa a tsakar gidan, ko wacce tana shashinta
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. ♀️*
1, *MU GANI A ƘASA...*
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*
Badi'at Ibrahim
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*❤️
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300
*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya
0810 433 5144
Masu tura katin MTN
0814 179 9224
Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* ❤️
Instagram links
https://www.instagram.com/p/CgPTv1-oML6/?igshid=MDJmNzVkMjY=
Facbook group
https://facebook.com/groups/463653111781414/
Telegram links
https://t.me/+xYZCR9JY-aMzNDFk
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google
za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
G Z D
MRS BUKHARI
43~44
Kai tsaye muka wuce shashen Goggo Asabe, Yayi daidai da b'ullowar Aliyu ta wata 'kofar, dan
'kofofine a gidan kashi kashi. Idanu ya zuba mini, cikin wani kallo me ma'anar me yasa zaki yi
mun haka?" jikinane ya sake mutuwa sabida marairaicemun da yayi, tare da cika ni da kallon
k'auna. Ni kaina naji sanyi sosai dana yi tozali da Aliyu. Da sauri ya iso wajansu Goggo
hansatu, ya amshi jakar kayana, da wata k'atuwar laida wacce ni kaina bansan meye a ciki ba."
"Goggo barkan ku da zuwa, inata shirin tahowa sai kuma ga ku. Sai sauke kai yake yi dan
kunya. Goggo Hansatu tace."
"Aliyu kenan babu komai ai duk d'aya muke, an riga an had'u ai, yanzu dai tare muke da bak'o
yana waje ka shigo dashi." Sai satar kallona Aliyu ya ke yi, ni kuma bance mishi komai ba. Da
sauri ya nufi b'arayinmu, na bi takunshi da kallo, har zuwa wannan lokacin Aliyu jinya yake yi,
domun baya tafiya daidai. A bakin d'akin Goggo mu ka yi Sallama, izinin shigowa ta bamu,
ganin mune yasa ta had'e rai, ko me kuma ta tuno sai ta d'an saki fuska har tana cewa.
" 'Yan balaguro an dawo?" k'asa nayi da kaina kawai, cikin ladabi na gaisheta, tare da tsantsar
kunya. Babu yabo babu fallasa ta amsa mun. Goggo Binta tace"
"Asabe bayan rabuwa, mun same ku lafiya ko?" Goggo tace.
"cikin k'oshin lafiya Binta, saukar yaushe?" Goggo Binta tace.
"Kusan sati biyu kenan."
"Ayya" shine abunda Goggo Asabe tace, gaisawa su ka yi da Goggo Hansatu, daga nan ta
tsuke bakinta tai shiru, Goggo Binta tace.
"Asabe ga Sadiya mun dawo muku da abunku, sai hak'uri, kuma bata kyauta ba data tsallake
gidan mijinta ta tawo gida, ga