Kaddarar Zuciya Book 2 Complete JIddah Barkum

Author :  Jiddah Barkum Category :  Read Hausa Novels

Chapter   14 / 40

39K to 42K   out of 117.5K words

Inteesar cikin tausayi, “daughter… tun yaushe kike wannan zazzabin?” Inteesar ta buɗe idanunta da ƙyar, muryarta na rawa saboda sanyi, “tun… karshen dare…” Mommy ta dafe ƙirjinta, “subhanallah. amma me ya sa baki kira ni ba?” Inteesar ta yi murmushi mai rauni, “ban so… in tashe ki…” Mommy ta girgiza kai, “kina magana kamar ba ’da mahaifiyarki ba. ki jira ni, zan dawo yanzu.” ta sake shafa goshinta cikin tausayi, sannan ta fita da sauri. Aamaan na hannunta.

Da suka isa falo… ta miƙa shi ga Shemau, “Shemau. karɓi Aamaan ki goya shi, kada ki bari ya sake komawa ɗakin yanzu.” “to Hajiya.” Shemau ta karɓi yaron, shi kuwa… har yanzu yana ta buɗe ido yana neman Inteesar.

Mommy ta juya kai tsaye zuwa kitchen, cikin gaggawa… ta haɗa mata tea mai ɗumi, ta ɗauko maganin zazzabi, ta zuba ruwa a bowl, ta kuma ɗauki towel domin a riƙa goge mata jikinta idan zafin ya ƙara tashi. Ba tare da ɓata lokaci ba… ta koma ɗakin Inteesar, zuciyarta cike da damuwa.



Bayan Mommy Haleema ta tabbatar Inteesar ta yi barci mai nauyi… ta janye bargon da ta gyara mata kaɗan, ta sake shafa goshinta. Zafin ya ɗan sauka kaɗan bayan maganin da ta sha, amma har yanzu jikinta ba ya da ƙarfi. Mommy ta sauke numfashi, “Allah ya ba ki lafiya.” ta kashe AC ɗin kaɗan saboda rawar sanyin da Inteesar take yi, sannan ta fita daga ɗakin a hankali, ta rufe ƙofar a hankali.



A wannan safiyar kuwa… gidan Alhaji Kabeeru ya sauya gaba ɗaya. Tun ƙarfe goma na safe… ’yan uwa da abokan arziki suka fara shigowa. Ba a yi hayaniya ba, ba a yi wata walima ba, komai ya kasance cikin sirri kamar yadda Daddy ya tsara. Kowa da ya zo… ya san dalilin da ya sa aka zaɓi hakan. Ba lokacin shagali ba ne, lokacin gyaran rayuwa ne, lokacin cika wata ƙaddara ce da Allah ya daɗe da rubutawa.



Bayan an idar da sallar Jumu’ah… mutane suka taru a babban masallachin unguwar.

Umar kuwa… zaune yake cikin farar shadda mai tsabta, fuskarsa cike take da natsuwa… amma zuciyarsa… Allah kaɗai ya san halin da take ciki. Bai yi magana ba, kansa a sunkuye, yana sauraron yadda aka fara gudanar da komai.

Alhaji Yusuf ya gyara zamansa, yau ya zo ne domin ya cika wata amanar da yake ganin ita ce mafi dacewa. Ya dubi Daddy, sai Daddy ya gyada masa kai cikin girmamawa. Nan aka fara gudanar da ɗaurin auren. Mai ɗaura aure ya fara da huduba, ya yi nasiha game da aure, game da amanar mata, game da tsoron Allah. Sannan ya juya ya kalli Alhaji Yusuf, “shin ka yarda ka aurar da Fateema Muhammad Kabeeru ga Umar Abdallah… ya ɗan dakata… …a kan sadaki naira dubu ɗari biyar?” Alhaji Yusuf ya amsa cikin nutsuwa, “na yarda.” sai ya juya wajen Daddy, “shin ka karɓa a madadin Umar Abdallah?” Daddy ya kalli Umar, Umar ya kasa ɗaga kansa, sai Daddy ya amsa da tabbaci, “na karɓa.” Mai ɗaura auren ya sake tabbatar da komai, daga nan… cikin murya mai ƙarfi ya ce, “na ɗaura auren Umar Abdallah da Fateema Muhammad Kabeeru a kan sadaki naira dubu ɗari biyar. in Allah ya yarda.” muryoyin amsa suka gauraya wajen, “Allah ya sanya alkhairi. Allah ya ba su zaman lafiya. Allah ya albarkaci wannan aure.”

A lokacin… Umar ya ji kamar lokaci ya tsaya, kalmar… “an ɗaura auren…” ta ci gaba da maimaituwa cikin kunnuwansa. Ya kasa gane… ko yana mafarki ne… ko yana farke. Shekarun da suka shuɗe… addu’o’in da ya yi cikin dare… hawayen da ya ɓoye… fatan da ya binne a cikin zuciyarsa… duk suka dawo lokaci guda. Yana jin kamar an ɗauke shi daga ƙasa… an kai shi wani wuri da bai taɓa tunanin zai isa ba. Da ƙyar ya ja numfashi, hannayensa suka ɗan yi rawa, wani siririn hawaye ya ziraro ta gefen idonsa. Shi kansa… bai san hawayen farin ciki ne ba… ko na tsoro… ko kuma na tuna Nana. Domin duk lokacin da ya yi ƙoƙarin yin farin ciki… sai fuskar Nana ta bayyana a gabansa, sai ya tuna murmushinta, sai ya tuna haƙurinta, sai ya tuna addu’arta. A hankali ya lumshe idanunsa, cikin zuciyarsa kawai ya furta, “ya Allah… idan wannan shi ne alkhairin da ka rubuta… ka sa in zama mijin da Inteesar za ta yi alfahari da shi, kuma ka sa Nana ta kasance cikin farin ciki a kabarinta.” ya buɗe idanunsa a hankali. Daddy ya kalle shi, idanunsu suka haɗu, Daddy ya yi masa wani ƙaramin murmushi, Umar ya mayar masa da murmushi, murmushi mai rauni… amma cike da fata.



Bayan an gama ɗaurin auren… ba a yi wata doguwar walima ba, kowa ya san dalilin hakan. Wannan aure ba aure ne na nuna farin ciki ga duniya ba… aure ne da aka gina bisa ƙaddara, addu’a da kuma fatan samun waraka. Mutanen da suka zo daga nesa suka yi sallama da Daddy, suka yi wa amarya da ango fatan alkhairi da zaman lafiya sannan suka kama hanyoyinsu. Cikin ɗan lokaci… gidan ya koma cikin shirunsa kamar ba wani babban al’amari da ya faru.



Bayan an idar da sallar magariba… Daddy ya zauna a falonsa, ya dubi Mommy Haleema, “Haleema…” “na’am Alhaji.” “ki kira min Fateema.” Mommy ta miƙe ba tare da ta tambayi komai ba.

A hankali… Inteesar ta turo ƙofar falon, sanye take da well ironed hijab dinta har ƙasa, ko kafarta ba a gani, “assalamu alaikum.” “wa alaikumus salam.” ta fara gaishe da Daddy, sannan ta juya ta gaishe da Yaya Adam, ta gaishe da Yaya Abubakar, ta gaishe da Khalil. A ƙarshe… ta ɗan juya inda Umar yake zaune, ya sunkuyar da kansa, ko kallonta bai yi ba, ta yi masa sallama cikin ladabi, ya amsa cikin ƙasa-ƙasa. Mommy Haleema ta shigo daga bayanta, ta zauna kusa da Daddy. Inteesar kuwa… ta zauna a ƙasa kusa da ƙafunsa kamar yadda ta saba tun tana yarinya. Sai falon ya yi tsit, shiru mai nauyi. Inteesar zuciyarta idan banda bugawa babu abinda take yi.

Sai Daddy ya kirata a nutse, “Fateema…” nan take… gabanta ya faɗi. Tun tana ƙarama… ta san abu ɗaya, idan Daddy ya kira ta da cikakken sunanta… to akwai magana mai muhimmanci. A hankali ta amsa, “na’am Daddy.” Daddy ya zuba mata ido, “waye ni a wajenki?” ta ɗan ɗago kai, sai ta sake sunkuyar da shi, “kai ne mahaifina.” Daddy ya gyada kai, “kuma kin san… cikin mutanen duniya… babu wanda yake miki fatan alkhairi fiye da ni?” ta kasa magana, sai ta gyada kai kawai, hawaye sun fara taruwa a idanunta ba tare da ta san dalili ba. Daddy ya ci gaba, “kin san… hakkina ne a matsayina na ubanki… in nemo miki mijin kirki. kin san hakan?” ta sake gyada kai, har yanzu… ba ta iya magana ba, bugun zuciyarta ya ƙara sauri. Daddy ya ja numfashi, sannan cikin nutsuwa ya ce, “saboda wannan hakkin… a yau… na ɗaura miki aure…” ya yi ɗan shiru, ya juya ya kalli Umar. Umar kuwa… tun shigowarta… bai ɗaga kansa ba. Daddy ya dawo da kallonsa kanta, “…da ɗan ɗan’uwana… …kuma… …yayanki… Umarul Faruq.”

Kalmar ta sauka. Inteesar ta ji kamar duniya ta tsaya, da sauri ta ɗago kanta, idanunta suka zazzaro, numfashinta ya tsaya, wani irin jiri ya ɗebe ta duk da a zaune take. Da sauri ta kai hannayenta biyu kan ƙirjinta, kamar zuciyarta za ta fito. Ta buɗe baki… amma babu kalmar da ta fito, sai hawaye, masu zafi, masu nauyi. Kowa yana kallonta, sai Umar kaɗai, har yanzu kansa yana ƙasa. Daddy ya sake magana, “na san… wannan labari ba ƙarami ba ne, na kuma san… ba ki yi tsammaninsa ba. amma… na yi wannan hukunci ne bayan istikhara, bayan shawara, bayan dogon tunani, bayan na nemi abin da na yi imani shi ne mafi alkhairi gare ku.” sai ya miƙa hannunsa ya nuna ƙirjinsa, “Fateema… idan kina son ki yi mini biyayya…” sai ya juya ya nuna Umar, “ki bi mijinki, kuma ki ba shi mutuncin da Allah ya ba shi.” ya sake kallonta, muryarsa ta yi laushi sosai, “ba na umartarki da soyayya, domin soyayya tana hannun Allah. amma ina umartarki da kyautatawa, ina umartarki da haƙuri, ina umartarki da mutunci. ina umartarki… duk ranar da rayuwa za ta yi muku tsanani, duk ranar da za ku saɓa, duk ranar da za ki ji ya ɓata miki rai… kada… kada ki taɓa ɗaga masa murya. kada na taɓa jin kin ɗaga masa murya.” ya sake maimaitawa, “kada na taɓa jin kin raina shi, kada na taɓa jin kin tauye masa hakkinsa. sannan… ka da ki manta… shi ma yana da hakki a kanki kamar yadda ke ma kike da hakki a kansa.”

Falon ya sake yin shiru, shiru mai nauyi. A wannan lokacin… ba Inteesar kaɗai ce take kuka ba, Umar ma… har yanzu kansa na sunkuye, wani siririn hawaye ya zubo daga idanunsa, ya faɗo a hankali… kan carpet ɗin falon, sai wani, sai wani. Bai yi yunƙurin goge su ba, domin bai san… hawayen farin ciki ne… ko na tsoron amanar da aka ɗora masa, ko kuwa… na tuna Nana Aseeyah. Falon ya yi tsit kamar ruwa ya cinye su.

Daddy ya sake zuba mata ido, ya lura hawaye kawai ne suke zuba daga idanunta, amma ko kalma ɗaya ba ta iya furtawa. Cikin sanyin murya ya tambaye ta, “Fateema…” ta ɗan ɗago kanta da ƙyar, “ko kina da wani abu da kike son faɗa?” shiru… Inteesar ta buɗe baki, sai dai babu kalmar da ta fito. Da ƙyar… ta girgiza kanta alamar a’a, ba don ba ta da abin faɗa ba… sai don ta rasa inda za ta fara, ta rasa abin da take ji, ta rasa abin da take tunani, ta rasa ko tana mafarki ne… ko kuwa a zahiri ne. Daddy ya daɗe yana kallonta, sai ya gyada kai a hankali, ya ɗaga hannayensa kaɗan, “Allah ya yi miki albarka. Allah ya sanya alkhairi a cikin wannan aure. Allah ya ba ku zaman lafiya. Allah ya ba ku zuri’a ta gari… …mai albarka.”

Amma… a lokacin… Inteesar ba ta ma san abin da Daddy yake faɗa ba, kalamansa suna shiga kunnuwanta… sai dai ba sa isa zuciyarta. Kamar komai ya fara dusashewa, kamar falon gaba ɗaya yana nisa da ita. Sai muryoyin sauran mutanen falon ne suka gauraya lokaci guda, “amin. amin ya rabb.” Daddy ya sake dubanta cikin tausayi, “za ki iya tafiya.”

A hankali… Inteesar ta ɗora hannunta kan carpet, ta yunƙura ta miƙe tsaye, da ƙyar ta tsaya, sai kanta ya yi wani irin mugun sarawa. Ta lumshe idanunta na ɗan lokaci, da ta sake buɗe su… sai ta fara ganin komai yana juyawa. Fuskar Daddy… ta zama biyu, Yaya Abubakar… ya koma uku, Khalil… kamar mutane uku ne zaune a inda yake, falon gaba ɗaya ya fara juyawa a idanunta. Numfashinta ya ɗauke, ta kai hannu za ta riƙe kujerar da ke kusa da ita… amma hannunta bai kai ba. “Inteesar!” Mommy Haleema ta kirata cikin firgici. Sai dai… ta riga ta makara. Jikin Inteesar ya yi laushi gaba ɗaya, idanunta suka lumshe, kafafunta suka kasa ɗaukar nauyinta. Cikin daƙiƙa guda… ta faɗi ƙasa.

“Fateema!” Daddy ya miƙe tsaye a firgice. “Intee!!” Mommy Haleema ta yi ƙoƙarin tare ta… amma ta riga ta zube a kan carpet. Sumammiya… ko motsi ba ta yi. Falon gaba ɗaya ya kaure da tashin hankali. Yaya Abubakar da Adam suka yi saurin ƙarasa gare ta, Khalil ya fito da gudu daga inda yake. Mommy Haleema ta ɗaga kanta tana kiran sunanta cikin kuka, “Inteesar! daughter! buɗe idanuwanki!” amma… shiru, sai numfashinta mai rauni kaɗai yake fita a hankali.

A gefe guda kuwa… Umar ya tsaya kamar an dasa shi a ƙasa, jikinsa ya mutu murus, idanunsa suna kanta… fuskarsa ta sauya launi. Da ƙyar ya iya motsa ƙafafunsa ya matso kusa, ya durƙusa a gabanta, ya kira cikin murya mai cike da tsoro da rawar jiki… “…Inteesar…” amma ba ta amsa ba, kamar wacce babu rai a jikinta.

Sorry for the typos not edited

*KADDAR ZUCIYA*

*CHAPTER EIGHTY: 80*

*A BRIDE IN THE MAKING*

*JIDDAH BARKUM*

———

“Khalil!”

Yaya Adam ya kira cikin tashin hankali, “kawo ruwa da sauri!”

Khalil bai jira a sake gaya masa ba, da gudu ya nufi fridge ɗin falon, ya buɗe shi da sauri, ya ɗauko bottle na ruwan sanyi, ya dawo da gudu. Ya durƙusa kusa da Inteesar, a hankali ya buɗe murfin ruwan, ya fara yayyafa mata a fuska, “Princess… Intee… buɗe idanuwanki…”

Mommy Haleema kuwa ta kama hannunta tana shafawa, Daddy kuma tsaye yake yana kallonta cikin damuwa. Umar… har yanzu durƙushe yake, idanunsa ba su bar fuskarta ba ko daƙiƙa guda.

Sai bayan wasu mintuna… Inteesar ta ja wani dogon numfashi, sannan wani, sai ta fara numfashi da sauri… da sauri… kamar wacce aka ciro daga cikin ruwa.

Mommy Haleema ta matso kusa da ita, ta ɗaga kanta a hankali, ta gyara mata hijab ɗinta da ya zame, ta shafa mata goshi, “alhamdulillah…”

Inteesar ta buɗe idanunta a hankali, ta fara kallon mutanen falon ɗaya bayan ɗaya, kamar ba ta san su ba, kamar ba ta san inda take ba. Idanunta suka sauka kan Daddy, suka wuce kan Yaya Abubakar, kan Khalil, kan Adam, sai… kan Umar. Da sauri ta kau da idanunta.

Mommy Haleema ta kama hannunta, “zo…” a hankali ta taimaka mata ta miƙe, jikinta ba shi da ƙarfi, da ƙyar take taka ƙafa. Mommy ta rungume ta fita da ita daga falon. Babu wanda ya ce komai, kowa ya tsaya yana binsu da kallo, har suka ɓace daga falon.



Da suka shiga ɗakin Inteesar… Mommy ta rufe ƙofar a hankali. Ba su yi taku biyu ba… sai Inteesar ta zame daga hannunta, ta durƙusa ƙasa, sannan ta zauna kan carpet.

Sai ta fashe da kuka, ba irin kukan da take yi a baya ba. Wannan kukan… ya fito ne daga can ƙasan zuciyarta, kuka mai ciwo, mai ɗaci, mai nauyi. Ta dafe ƙirjinta da hannu ɗaya, numfashinta yana rawa, da ƙyar ta iya magana, “Mommy…” ta kira cikin murya mai karyewa.

Mommy Haleema ta durƙusa gabanta, ta kama hannayenta, “ina jin ki, daughter…” Inteesar ta girgiza kai, hawayenta suna ta zuba, “…aure…” ta furta da ƙyar, ta haɗiye wani abu mai ɗaci, “…Yaya Umar…” abin da kawai ta iya faɗa kenan, sai kuka ya sake ƙwace mata.

Mommy Haleema ta janyo ta cikin jikinta, ta rungume ta sosai, ta shafa bayanta a hankali, “shhhhh… ki daina kuka, daughter, ki kwantar da hankalinki.” Inteesar ta ci gaba da girgiza kai, kukanta yana ƙaruwa. Mommy ta sake rungume ta, “kina so Daddy ya ji kamar bai isa da ke ba ne?” da sauri… Inteesar ta girgiza kanta, “a’a…” muryarta ta dusashe cikin kuka.

“to…” Mommy ta share mata hawaye, “ki daina kuka. ki mayar da komai ga Allah, ki yi addu’a, ki roƙi Allah ya sanya wannan shi ne mafi alkhairi gare ki. domin mu mutane… ba mu san abin da gobe ta ɓoye ba.”

Inteesar ta sake fashewa da kuka, ta dafe kanta, “Mommy… …aure… …Yaya Umar… …yayana ne…” ta kasa ƙarasa maganar, lebbanta suka fara rawa, ta dafe bakinta. Sai da ta yi ƙoƙarin haɗiye kukanta, amma ta kasa. Da ƙyar ta furta, “…mijin…” kalmar ta tsaya a maƙoshinta, ta girgiza kai da ƙarfi, kamar zuciyarta ta ƙi karɓar abun. Sai ta sake gwadawa, “…mijin…” hawaye suka rufe mata fuska, “…mijin…” ta kasa faɗin sauran, sai kuma cikin kuka mai tsananin ciwo ta furta, “…mijin Yaya Nana…”

Nan take… ta rushe gaba ɗaya, ta manne kanta a ƙirjin Mommy Haleema, ta fashe da wani irin kuka mai ƙarfi, kuka mai sauti, kuka wanda ya fito daga zuciyar da ta cika da ruɗani, “Mommy… ta ya ya zan iya… ta ya ya zan iya kallon Yaya Nana… …a ranar alƙiyama… …idan na zama matar mijinta?”

Mommy Haleema ta runtse idanunta, sai dai ta daure, ta ƙara rungume Inteesar, ta ce cikin murya mai cike da taushin uwa, “ki saurare ni, daughter… wasu ƙaddarori… ba mutum ne yake rubuta su ba, Allah ne. kuma abin da Allah ya rubuta… ko da zuciya ba ta fahimta yau ba… wata rana… …za ta fahimci hikimarsa.”

Inteesar ta ci gaba da kuka, kuka mai tsananin ɗaci. Yayin da Mommy Haleema ke shafa bayanta cikin lallashi.

Inteesar ta ɗago jajayen idanunta da suka kumbura saboda kuka, ta kalli Mommy Haleema cikin ciwo, “Mommy… meyasa ba ki faɗa min Daddy zai aurar da ni ba? meyasa kika yi min shiru?” ta ƙarasa maganar cikin wani sabon fashewar kuka.

Mommy Haleema ta ja ta sosai cikin jikinta, ta shafa kanta a hankali, “saboda… umarnin Daddy ne.” ta faɗa cikin sanyin murya, “kuma kin san… dukkanmu muna ƙarƙashin ikonsa.”

Inteesar ta lumshe idanunta, sabbin hawaye suka sake zubo mata. Mommy ta ɗago fuskarta da hannunta, ta share mata hawayen, sai ta ce cikin muryar uwa mai cike da taushi, “Princess… kin san ni, kin san Daddy, kin san yayyanki, dukkanmu muna sonki. wallahi… ba za mu taɓa haɗa kai mu jefa ki cikin abin da muka san zai zama halaka gare ki ba.”

Inteesar ta ci gaba da kallonta cikin hawaye. Mommy ta sake tausasa muryarta, “saurare ni. idan har…” ba ta ƙarasa ba, sai ta ɗan yi shiru, ta tabbatar Inteesar tana saurarenta, sannan ta ce, “idan har ba kya son Umar…” na ɗan lokaci… idanun Inteesar suka cika da wani ƙaramin haske. Mommy ta ci gaba, “na yi miki alƙawari… zan tsaya a gefenki, zan taimake ki. amma…” ta ɗaga yatsa ɗaya, “akwai sharadi.”

Da sauri Inteesar ta ɗago, “Mommy… mene ne sharadin?” Mommy ta yi murmushi mai laushi,

14 / 40