FARRAH HAUSA NOVELS COMPLETE BY M SHAKUR COMPLETE.doc

Author :  Maman Shakur Category :  Arewa Pen

Chapter   14 / 48

39K to 42K   out of 142.7K words

.ba jinjina kai Alhaji yayi yana murmushi yace  Masha Allah, ga muryanki nan Tubarkallah Allah kara sauki  Farrah yasake kiranta anatse hakan yasa ahankali tadago kanta ta kalleshi, ajiyan zuciya Alhaji yasaki, yace  kingan ni nine mahaifin Zayn, mijin Mamin ku, da Mariya da Fatima da Maryam, Zayn kadai Allah yabani, rana daya kuma Allah yakawoki cikin rayuwan mu, akwai abinda yasa nasaka aka kiraki, inaso na tambayeki ne naji amsanki kafin nai komi yasakeyin shiru sanan ahankali yace  Farrah kawunki ya sanar damu ke marainya ce, matata nan Maman Zayn likita ce, itace tamiki aiki a operation, taga tabo da dama ajikinki wanda yake nuna na alamun duka ne, yanzu inaso namiki wani tambaya banso kimin karya kinji gyadama Alhaji kai tayi ahankali, anatse Alhaji yace  wanene yasamiki garwashin wuta abaki? Shiru tayi gabanta nafaduwa dum dum, dafata Mami tayi ahankali tace  kada kiji tsoro ki yayi gaskiya kinji gyadama Mami kai tayi sanan takalli Dad, batasan ya akayiba kasa karya tayi ahankali tace  In& na  Matar kawunki ? Gyadama Alhaji kai tayi tace  eh  ita ke dukanki ma ? Gyadama Alhaji kai tayi takai bayan hannunta dasauri tashare hawayen daya zubomata, shiru dakin yayi Alhaji na kallonta, murya chan kasa yace  akwai abinda ake cema adoption aturence, yana nufin zaki dawo diyata ni da Mami da kotu tabamu mune custodian naki, kula dake yafita daga hannun su kawunki yadawo hannunmu dundundun ki dawo yarmu musaki amakaranta da sauran su, nakira lawyer na halama ya iso yanzu, yanzu hakama kawunki da matarshi na gidan nan chan bangaren baki, amman so naki nafara jin bakin ki kafin nasa akawo kowa nan, Farrah Alhaji yakirata ahankali murya chan kasa tace  Na am ahankali yace  kin yarda ni da Mami muzama iyayenki? Wasu kalan hawaye ne suka cika idanunta, tunda take baa taba bata daraja da mahimmaci dahar za a zaunar da ita atamabayi yardanta Awani abu ba sai yau, tunda tahadu da mutanen nan sunada kirki sosai, batada kowa aduniyan nan banda kawu shi kadai gareta amman shima baya sonta baya kaunarta agabanshi aka kashe mata yar uwa baice komiba, dafata Mami tayi dasauri ta kalli Mami, Gyadamata kai Mami tayi alamun tace  eh ahankali tace  eh Abba rungumeta Mami tayi tana share mata fuska tace  daina kuka to sai alokacin Zayn yadan saci kallonta, fuskanta na jikin Mami tana goge hawayen dasuka zubomata kaman ance ta kalleshi hada idanu sukayi da Zayn din hararanshi tayi tareda dauke kai.


Dauke kai shima Zayn yayi dasauri yana regretting kallonta ma dayayi waya Alhaji yayi sanan ya katse wayan yakalli Mami yace  tafi da ita sama .



Wani Babban lawyer Alhaji ne yashigo falon tareda Uncle, sai Malam da idanunshi sukai zuru zuru da Inna da itama idanunta sukai zuru zuru, Malam yay mamaki dahar gida aka shigo aka daukesu suka shiga jirgi, Inna ihu tadingayi a helicopter wai zata mutu hanjin cikinta zasu zube.


Malam na ganin Alhaji da gudu yataho gabanshi ya tsugunna yahade hannayenshi biyu yace  Alhaji dan girman Allah kayakuri kada ka karbe kudaden daka bani, wlh wlh shairin shaidan yasa na gudu nakoma kauyenmu, to inbama shairin shedan ba ai nasan Kunsan kauyen kuma nakama nagudu, Alhaji dan Allah kayakuri wlh bazaka gane bane, Alhaji nima diyata daya rak, ina fama dakai na, kanwata tazo ciwon datayi shine ya tsiyatar dani tatas banda ko kwandala matata ce keda awakai suma awakan ranan da Farrah ta ceto dan gidan ka duka ta batar dasu, wlh ashirmena naso nagudu ne kawai nahuta inje na karata da matata da diyata guda amman nai kuskure kuya kuri tunda yake maganan kowa ke kallonshi, cikin fushi Uncle yace  ina miliyan goman damuka baka bamu kayanmu ku dauki yarku amaidaku kauyenk& &  tsayar da maganan datakeyi yayi ganin Alhaji yadagamai hannu, nuna kanshi Alhaji yayi yace  kai tun kana dan kankanin ka kataba ganin nai kyauta sanan nadawo na amshe kyautan danayi sunnar da kanshi kasa Uncle yayi yace  a a Yaya maida hankalinshi kan Malam Alhaji yayi da Inna da itama ke zube gaban mijinta jikinta na rawa tunda take bata taba ganin aljannan duniya irin gidan nan ba, murmushi Alhaji yasakin musu yace  ku zauna da kyau dan Allah ni bakamin komi ba kuma bansa adaukoka sabida kudin danabaka ba nariga nabaka gonakin suma nariga nasa anma mai garin ku magana shi gwamnan Adamawa duk sanda ka koma zaka amsa koba komi yarinyar da bakaso yarinyar daka gudu a asibiti kabarta kaga kaci arzikinta Alhaji yakara murmushi jikin Malam yay sanyi yakoma ahankali ya zauna hakama Inna, gyaran murya Alhaji yayi yace  abinda yasa na nasa akawomin?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? kai nauyin dake kanka kake kokarin gudun mawa nakeso nacire maka shi daga kanka gabaki daya, diyarku Farrah nakeso nazama mahaifinta a shar ance, cinta shanta, suturanta karatunta duka yadawo kaina, zai zamto Farrah tadawo diyata shine kawai abinda yasa na nemoka zaka bani ? Alhaji ya tambayeshi dasauri Malam jikinshi har bari yake yace  eh eh wlh nabaka Alhaji Inna ma dan sosa keya tayi azuciyanta tanaji inama ace Rakiya ce ta taimaki yaron, kaman ta chakama kanta wukan bakin ciki takeji, kallon Lawyer Alhaji yayi yace  give him the papers tashi yayi zuwa wajen Malam dan yabashi papers din yakuma nunamai inda zaiyi signing, dan yatsine fuska Zayn yayi yamike tsaye hanyar stairs yayi yay sama abinshi, shi kanshi baisan mesa yazo saman ba kujeran dakenan falon sama ya zauna yana kallon kofan dakin da yake tunani nan ne dakin Farrah dan shine dakin dake kusada na Mami, yadade yana kallon kofan, kaman akwai abinda ke controlling nashi tashi yayi zuwa gaban dakin yay jimmm yana kallon kofan, ahankali yadaga hannunshi yakai zaiyi knocking kofan dan cizan lips dinshi yayi yasauke hannun kasa ahankali, sake daga hannun yayi zaiyi knocking daidai nan aka bude kofan Farrah ce tabude kofan da saurinta dan ana kiran IPad din Mami dake wajenta zata kaimata saura kadan tafada jikin Zayn ta tare kanta ta hanyar kai hannunta daya ta daura kan kirjinshi daidai saitin zZuciyanshi as kariya daidai loOkacin kirjinshi ya buga dumm!=??? FARRAH =???



' I AM SO SORRY VIPs, TIME TO SPOIL YOU ALL DA UPDATES>?s?>?s?

EPISODE 2?? 3??
Bala in faduwa gaban Layla yayi ganin yanda idanun Zayn sukayi ga hannunta dahar wani kalan zugi yafara sabida yanda Zayn ya damke hannun, fizge hannun nata tayi da karfi sanan tawuce inda ya jefar mata da riga ta dauka tasaka sanan tazo tafice saida kofan yarufe sanan Zayn ya kalli Farrah dake kuka sosai har lokacin kokarin kwace kanta daga jikinshi take, hannunshi yasa yacire hannunta daga kan fuskanta cikin dan kakkausan murya yace  ke open your eyes juyarda fuskanta gefe tayi dasauri tana kokarin fizge hannunwanta daga nashi amman takasa, dan gajeren tsaki yaja yanajin yanda take kuka aranshi cikin dan fushi ya jijjigata yace  why are you crying now meke saki kuka eh ? Yasake shiru yana kallon gefen fuskanta da shine saitin fuskanshi dan tsaki yaja ahankali yace  what s your business with my life? Damn it stop crying Farrah! Yadaka mata wani uban tsawa da har zuciyanta saida taji yakada tsayawa kukan datakeyi yayi chak, sakin hannayenta yayi cikin kakkausan murya yace  kalleni nan juyoda fuskanta tayi ahankali sanan gently tabude idanunta kaman mai tsoron bude su ta daurasu akan fuskanshi idanun har sundanyi ja gashin idanun sun tattare da hawaye, wani irin yirrrrr yaji data kalleshi da moist idanun, ajiyan zuciya tasauke ahankali dayaji saukanshi akan fuskanta, dan kauda fuskanshi yayi kadan sanan yadawo da fuskan yadaura idanunshi kan nata daure fuska yayi yace  goge fuskan ki hannunta takai ahankali ta goge fuskan tass kaman yanda yasata, yatsine fuska yayi yakalleta from head to toe yace  go juyawa tayi dasauri tafice daga gym din hartana neman tuntube, har lokacin jikinta yaki dawowa daidai, sai ganin abinda tagani just now take Ya Zayn yakama ma Layla dasuka gani jiya tareda kishiyan Mami nono zaisha, wani kalan abu taji acikinta yataso mata tareda tsigan jikinta kaman zatai amai yamata wani warrrrrer ajiki, dasauri tabude kofan dakin Mami tashiga, Mami dake cikin kitchen jin anbude kofa tace  Farrah kene ahankali tace  eh Mami daga kitchen din tace  yauwa imaza jeki shirya mutafi saloon nafito miki da kayan dazaki saka ahankali tace  to sanan tawuce sama.



Saida yaga fitanta sanan yawuce yakoma kan machine din dayake kai dazu ya zauna, dan gajeren tsaki yaja sai kawai yatashi safan hannun yacire ya Yar awajen ko kashe wakan gym din baiyiba yafito yawuce side nashi wanka yayi dagashi sai towel a waist kawai yazo yafada gado sai bacci yau tun asuba yatashi.

Yanda tafado falon da bala in fushi yasa Hajiya Mariya tace  ke lafiya ? Cikin tsananin fushi tace  Mommy wai waye wanan yarinyar tajiya ? Dasauri tace  Meya faru tell me everything ? Cikin fushi Layla tace  son ta yake Momny kwashewa da dariya Mommy tayi sosai tace  so anya kinsan abinda kike fadi kuwa Layla? Zayn ne zaiso mutum, please leave that just tell me what happen fadama Hajiya abinda yafaru daga farko zuwa karshe tayi Hajiya ta jinjina kai tace  Alhaji ne wai yay adopting yarinyar, kinsan tun farko farkon aurena dashi babu kalan rokon Alhaji da banyiba kan muyi adopting yara yaki Amma kinga ai yanzu yayi dayayi kuma sai yabawa favorite wife dinshi, komi yakusan zuwa karshe wannan alkawari, just duk yanda zakiyi kiyi kisami kan yaro ya yarda dake kinjini ko that s my only hope Gyadamata kai Layla tace  don t worry Mommy I can do anything for you murmushi tayi tace  jekiyi wanka kizo kiyi breakfast tashi tayi tawuce sama.



Wanka fara tayi tafito daure da towel kowani motsi tayi sai abinda yafaru dazu yafado mata, inda aka mata aiki Mami harta cire bandage din jikinta nada kyau sosai, shiryawa tayi cikin kayan da Mami ta ijiye mata Riga da skirt na atampa ja, sun bala in amsanta, gyale tadauka a hannu tafito afalo tasami Mami tana waya ganin Farrah saida tai murmushi tace  kinyi kyau sosai My baby Oya muje tashi tayi tacigaba da wayan datake suka fito mota suka shiga bodyguard din Mami yajasu wani babban saloon Mami takaita, wanke Mata gashinan dakeda uban dauda akayi, akai blowdrying sanan Mami tasa aka mata kitso shuku yan kanana ana mata pedicure itadai Farrah kallonsu kawai take, tsaf aka gama komi tsayin gashinta har waist, ciki suka wuse Mami tasa aka mata facials sanan tasayamata wani set na cream da sabulun wanka damai spa din tamata recommending, Mami tasa aka mata waxing nanne fa Mami na zaune a falo amman taji kukanta dan murmushi Mami tayi, saida aka gama sanan tafito idanunta sunyi zuru zuru, Mami tace  sannu akunyace ta gyadama Mami kai sanan suka fito ita kanta jin jikinta tayi daban, wani babban super market sukaje, shopping Mami tamata na mamaki Farrah sai kallonta take bata taba sanin akwai wayanda basune suka haifeka ba amman zasu soka da zuciya daya ba sai awajen Mami saida suka gama aka loda komi a mota sanan suka shiga Mami tace  kinaso kiga Mama na ? Dasauri ta gyadama Mami kai tace  eh Mami dan murmushi Mami tayi tace  itama ta kosa taganki yanzu zamu .



Tunda suka shigo layin su Grandma take kallon layin shi layin ba kaman na irinsu Mami bane, parking sukayi a kofar gidan aka bude musu kofa, kayan da Mami tasayama gidan Bodyguards suka shiga fitowa dashi itakuma Mami da Farrah sukai ciki, da sallama suka shiga gidan, Mama ce tafito daga dakinta tana rikeda charbi a hannu tace  oyoyo oyoyo oyoyo jikalle na wani kalan murmushi Farrah tayi ganin yanda tsohuwan dake kama da Mami sosai tamata oyoyo har gabanta Farrah taje ta tsugunna ahankali tace  ina kwana Mama dasauri Grandma tace  tashi tashi Allah kadai ake tsugunnamawa, Allah yamiki albarka taho muje daki taja hannun Farrah suka shiga daki Mami kuma tai murmushi tana biyosu abaya, zaunar da ita Mama tayi akan kujera sanan tace  yau kaf Mutan gidan nan sun fita sunje bikin saude ni kadai bari nakawo miki abinci dasauri Farrah tace  a a Mama bari na dauko miki  je uwar daka na zakiga kula ki dauko gyadamata kai Farrah tayi da sauri sanan ta ijiye gyalenta kusada Mama tawuce dakin data tabbata nanne uwardakan kulan datagani tadauko sanan tafito takawo takara komawa plates data gani takawo, Mama tace  ci abinci iya cinki kinga Maman nan taki bata son cin abinci ita Zayn yabiyo dan murmushi tayi tadan dagakai takalli Mami gani tayi Mami na kallonta, ahankali tace  Mami zakici abinci ? Gyadamata kai Mami tayi ahankali tanajin wani sanyi aranta Zayn baitaba tambayanta taci abinci ko zataci abinci ba yara mata daban ne kawai duk wanda Allah yabamawa yace Alhamdulillah.


Yanda Mami tace  eh yasa dasauri tabude kulan tuwone da miyan karkashi dayaji nama da man shanu, fara zubawa tayi ahankali Mami dake kallonta tace  ki zuba mana tare dagokai tayi takalli Mami saikuma tai murmushi sosai itama Mama dake kallonsu duka biyun murmushi tayi, zuba musu tayi sanan tadauka takai gaban Mami, saukowa Mami tayi kasa sanan suka faraci feeding Farrah tadingayi abaki har suka cinye, kwashe kwanukan Farrah tayi tafita dasu waje inda taga makwarara, kwanukan data gani na datti ta hada tass tashiga wankewa daga daki Mama tace  mekikeyi Farrah  wanke wanke Mama murmushi Mama tayi takalli Mami tace  Allah yabaku ladan abinda kukayi, sanan Allah yatayaku riko murmushi tayi tace  Ameen Mama tace  yanda kika taimaketa ubangiji Allah Ya taimakawa Zayn dinki haka Ya shirya dashi yakuma natsar dashi murmushi Mami tayi tace  Ameen Mama, kin shanye magungunan ki tabe baki tayi tace  nifa nagaji da shan magani fa Mami ki kyaleni tashi Mami tayi dasauri tashiga uwar dakinsu gaban drawer tana dudduba magungunan Mama tace  Mama wai mesa bakishan magani, sune fa zasu dinga controlling da regulating BP dinki eh Mama dan Allah kidinga sha naji.
Sai gab da magrib sukabar gidan Mama, har atampa Mama tama Farrah kyauta dan Farrah ta gyara gidan tsaf ta gyara dakin Mama ta share harda cire duka yanan gidan dana zaure sai dariya suke itada Mama suna tambayanta ya akayi tacire yanan Xauren nan abokanen Zayn ne wai tsoronsu yake da gizogizo, babu kalan labarin tsorace tsorace Zayn dabata jiba, suna kaiwa gida sukai Magrib anayin isha i Mama tasata tai bacci dan goGbe monday zaa kaita school.=??? FARRAH =???



'

EPISODE 2?? 4??
Da asuba Mami tashigo ta tada ita, salla tayi sanan tafito tasami Mami a falon sama suka fara karatun Alqur ani, saida suka gama Mami takara duba wajen dinkinta yay healing sosai, ganin 6:30 yasa Mami tace  jekiyi wanka zan fito miki da kayan da zaki saka Zayn zai kaiki school yau dan murmushi tayi sanan ahankali tace  Mami kallonta Mami tayi tace  naam murya chan kasa tace  Mami tsoro nakeji kada amin dariya a school kinga daga kauye nazo kuma ban iya turenci ba tunda take maganan Mami ke kallonta muryanta dadi tafara magana kaman kada ta daina, dan murmushi Mami tayi tace  Zayn zai kaiki Best school dayake nan Abuja, and one of the characteristics of schools haka shine basama mutum dariya, basa bullying and zasu dauki lokacin su su koyarda ke da kyau, ban sanki da tsoro ba, sanan b ajin kunya wajen neman ilimi kizama mai kwazo kibama wayanda zasu miki dariya kunya kinji, and I am here, ga Yayanki Zayn, ga Abban ki komenene baki iyaba duk zamuyi guiding naki, we are your parents, muje naciro miki kayan dazaki saka Mami tai maganan tana kama kafadabta sukai daki, wardrobe nata Mami tabude wani pink long sleeve t-shirt Mami taciro mata na mata mai botura na glass agaba, sai wani black long skirt, da black gyale karami, ta ijiye mata akan gado, tace  jekiyi wanka kifito bari naje naduba breakfast nakuma tada Zayn, koda yake nasan Abban ku yatadashi yanda yasan zai kaiki school haka ficewa tayi itakuma Farrah tashiga wanka, wanka tayi sanan tadaura towel tafito, manta tashafa sanan ta shirya tsaf tasaka kayan da Mami tafito mata dasu taje gaban madubi wani kalan kyau tayi bana wasaba, bude kofa da akayi yasa tajuyo Mami ne, murmushi tayi ganinta hakan yasa Mami taja kujeran gaban madubi ta zaunar da ita tace  yau zaki fara school ki kula da kanki, makarantan ku akwai both maza and mata ki zama yarinya mai natsuwa baruwanki da maza malamai ko dalibai bude idonka kiga kwalli Mami tasaka mata, sanan tadau man baki na Vaseline tashafa mata a lips, lips nata kaman tasa mata pink jan baki, drawer ta taja, Mami tadauki wani gold ear ring na dan makale tasaka mata a kunne sanan tadauki wani simple chain na gold shima da babu pendant ajiki tasa mata awuya dan wuyanta yadinga walkiya, bracelet na LV Mami tasaka mata a hannu sanan tai murmushi tabata wani flat black slippers na saint Laurent size dinta 37 tasaka sanan Mami tace  muje babban jakan makarantan da Mami tasaya mata jiya tadauka daga kan gado da bakin gyalen Mami tai gaba ita kuma biyeda Mami tana kallon kanta dan kayan sun mata kyau, tunda suka fara sauka daga stairs ta hango Zayn zaune afalon shima ya shirya yana sanye da riga da wando na jean da

14 / 48