Author : Zahra Royal Star Category : Read Hausa Novels
/>
Tana kallon Hali dake bacci har lokacin hankalinta kwance, ji take inama ita ce Halin a yanzu, saboda Halimar ita bata tab'a soyayya ba, sai dai azo ace ana sonta, kuma ba'a tab'a gudunta ba, sai ma ita ce ke gudun masu son nata, domin wata irin murd'ad'd'ar mutum ce mai wuyar sha'ani kwata-kwata bata san yama soyayyar take ba, har aka zo ta sami wani hamshak'in mai kud'in daya fito yana son auranta, shima da kyar ta basa had'in kai har ya shigo gida. Duk da ita kanta ansan Tasiu a gidan, duk inda ta zauna sai tayi maganarsa, sau d'aya ya tab'a zuwa Katsina shima sunje gidan Y'an uwan Umma ne dake cikin garin Katsina a can suka had'u dashi, da duk a waya ta sanshi ko a fili basu tab'a had'uwa ba, soyayya ce take irinta social media. Bata san illar da take ma rayuwarta ba, da bazata sake fad'awa soyayyar wadda bata tab'a sani ba, amma ina a haka kaddarar tazo. Hatta school Hali ita ta wuce ta gaba da secondry har kawo yanzu da ake shirin aurar da ita ga wani mai kud'i....
*RAUNIN ZUCIYA*
*©Zahra Royal Star*
*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*
EPISODE 2
*K'auyen Tudun Wulli, Kankia Local government Katsina State Nigeria*
K'ank'ance ido take tana duban matashiyar yarinyar tada shigo cikin gidan tana sauke abunda ke kanta.
Mik'ewar da zatai ta hangi Inna Laure dake tsaye tana mata wani mugun kallo.
Wani irin miyau ta had'e tana sake kallon Inna Lauren tsoro na sake rufeta sosai.
Sakin tsintsiyar dake hannunta Inna Laure tayi tana matsawa sosai kusa da yarinyar.
Hannunta ta mik'a ta kamo k'unanta tana murd'eshi da k'arfi. Wata y'ar k'arar azaba yarinyar ta saki. Inna Laure cike da tsananin tsanar yarinyar ta ce.
"Wato ke muguwa algunguma, yanzu Bilki ta zo take gaya min, an ganki da wani mai mota ya ce kizo cikin Motar zai saye awarar nan duka, tsabar ke y'ar bak'in ciki ce, irin tsiya shine kika ce masa ke ba y'ar iska bace ko?, to kuwa tunda kika yarda baki saida awarar nan ba na rantse da girman Allah yau Habiba sai jikinki ya gaya miki"
Kuka Habibar ta saki mai sauti tana kallon Bilki dake hararta dake gefenta bayan fitowarta daga d'aki jin fad'an da Innar ke mata.
Cikin muryar kuka da tsananin tsoron Innar ta bud'e baki ta ce.
"Wallahi Inna d'an iska ne fa, ni kuma tsoronsa nake ji shi yasa banje ba, latse y'an mata fa yake, shine fa aka tab'a cewa yayi ma wata ciki a K'auyen nan f......
Kwaffffff Inna ta bige bakin Habiba dake magana, dafe bakin tayi tana runtse idonta da k'arfi, wani rankwashi taji Innar ta sake sakar mata a tsakiyar kanta.
Wani ihu ta saki tana jin wata irin azaba da tayima kanta dirar mikiya.
Kuka take yanzu sosai jin yadda Innar ke sake murd'e mata k'unne.
"Ai wallahi yau ba abunda zaisa banci kutumar ub*nki ba Habiba, ke har kin san wani abu wai shi iskanci d'an uwarki?, ko an tab'a latse ki ne ban sani ba?".
Wani kukan Habiba ta saki tana kallon yadda Inna ke zare mata ido. Girgiza kai Habiba ta kamayi tana fad'in.
"Ni Inna ban san komai ba wallahi dan Allah ni dai kiyi hakuri".
"Zaki ce uwarki ne yau wallahi, zanga ubanda zai baki abinci yau, ke ko Mlm ne ya dawo da uwar data yafeki basu isa susa na baki abinci ba yau wallahi"
Zaro ido waje Habiba tayi ganin Inna ta jawo ta kiiiiiiiiiiiiiiiiiii ta matso da ita bakin murhu, wata wuk'ar nanin takalmi dake cikin garwashin wuta ta d'akko.
Wani uba-uban ihu Habiba ta saki ganin ta cirota daga murhun tana kamo tafukan Hanyanta biyu, cike da tsananin rashin imanin gaske Inna Laure ta nana mata wuk'ar nan dake d'auke da wani irin zafin wuta.
Wani irin ihu had'e da kururuwa Habiba ta saki tana jin wata irin tsananin rad'ad'i had'e da wata irin azaba da ta rufe mata jiki, wani irin azababben zafi ne yayi ma Kwakwalwar kanta kawanya, wani irin azababben jiri-jiri ta fara gani had'e da wani irin juyawar kai, lumfashinta take jin kamar zai bar gangar jikinta tsabar azabar data yima ilahirin jikinta kawanya.
Kyarma jikinta yake yadda Inna Laure ta rik'e ta sai nana mata wuk'ar nan take wacce tayi jawur cikin wuta.
Cike da rashin imani tsantsarshi Inna ta wancakar da Habiba gafe ta fad'i k'asa, kuka Habiba ta saki da k'arfi, da wani irin mahaukacin sauri ta fara hurama hannun nata iskar bakinta, tana hawaye sai yarfa hannun take, tafin hannun nata yayi jawur duk ya tashi ya k'une sosai.
Inna ba tausayi ko imani ko dana sanin abunda tayi mata ta nunata da yatsa ta ce.
"Daga yau idan wani ya kira ki domin saye awarar dana ke d'ora miki nan take baki kud'i masu yawa wadda ma yafi na awarar dana d'ora mikin, domin Allah Habiba kar kije kamar yadda kike yau, ni kuma tsaf bazan gaji da azabtar dake ba. Ke baccin ma ina da k'arfin hali ubanwa zai iya abunda nayi miki a rayuwa, Mlm yaje ya auri uwarki ba san asalinta ba, daga gudun hijira daga Niger ta fad'o garin nan, shi yaga kyakykyawa buzuwa shine ya mak'ale mata, ya aureta har aka haifeki, har kawo yau da muke babu ubanda ya tab'a zuwa a matsayin dangin uwarki, aka haife ki ta mutu, aka barmu da alak'ak'ai, shima Mlm d'in yazo ya mutu ya barni da bak'in iri da tsintacciyar mage, marar asali kawai. Da wata ce bani ba da tuni kin kama gabanki, ta barki kin shiga duniya, sai ni dan na rik'e ki na rufa miki asiri shine zaki watsa min k'asa a ido makira algunguma?, ko wuta na ce ki fad'a ba fad'awa zakiyi ba?, dan kinje kin keb'e da wani namiji uban miye a ciki?".
Kuka sosai har yanzu Habiba keyi ido rufe take kuka ta tunanin, inama Innar zata kyaleta ta shiga duniyar, daya fiye mata zama tare da Innar, domin babu abunda take k'unsa zai azaba da kyara.
Bilki dake gefe tana ma Habibar kallon uku saura, ta matsu a kusa da ita tasa hannunta ta kaima Habibar rankwashi a kai tana cewa.
"Shegiya da kyau kamar dangin Aljanu. Wallahi na tsani wannan Habibar Kinga fa koda yaushe ita ce ake cewa ana so ba ni ba, na rantse da Allah indai ban auru ba, kema baki ba yin aure wallahi".
Wani kalar abu Habiba ta had'e na tsananin bak'in ciki da tausayin kanta, tabbas ba tun yau ba Bilki ke k'orar mata samari had'i da ita kanta Innar, duk da shekarunta bai gaza sha takwas ba, ta girma Bilki amma yadda ta rainta kai kace ita ce babbar ba Habibar ba.
"Ai ba saima kin fad'a ba Bilki, ai ita da aure sai dai taga anayi muguwa mai bak'in hali irin na uwarta, wannan kyan naki da ina da dama sai na lalata shi wallahi".
Rasssss gaban Habiba ya buga da k'arfi jin furicin Inna. Ashe k'iyayyar da suke mata harta kai haka.
Wasu hawaye suka sake zubo mata sosai idonta sun kad'a sunyi jawur sun kunbura sosai.
Wani tsaki Bilki ta saki tana sa k'afa ta hauri Habibar ta wuce d'aki tana mata wani irin kallon banza......
*Unguwar Yammawa Rimaye, Kankia Local government Katsina State Nigeria*
Farkawa Hali tayi tana mik'a, shashshekar kuka data ji ne yasa tayi saurin wartsakewa tana duban inda take jiyo kukan na fitowa.
Hango Ummi d'uke a k'asa kamar sallah ta gama tana kuka tana kallon cikin wayarta.
Wani d'an tab'e baki tayi ta sakko daga gadon harta sakko Ummi bata sani ba.
Cikin wayar Hali ta kalla ganin hoton da take kallo yasa Hali sake tab'e baki tana mamakin yadda Ummi d'in ta d'au soyayyar wani banza can ta saka ma kanta tana wahalar da kanta akan D'a namiji.
Ita fa ko yanzu wadda aka sa masu rana dashi, idan ba shi ya nemeta ba, sai su shekara a haka, ko chatting basu cika yi ba, ita hidimar gabanta ma ya isheta.
Hoton data gani yayi bala'in bata haushi, video call ne Tasi'un keyi da wata budurwarshi yayi Screenshot ya d'ora a status, sai wani daya d'ora sunje wajan shak'atawa da budurwar suna shan iska, sunyi hotona masu kyau irin na y'an gayu, shine ya d'ora.
Kai wani kalar bala'in haushi ne ya sake rufe Hali, da haushin Ummi d'in, d'an gwal ne shi?, da bazata rabu da shege ba?.
Tsakin data kuma d'ankarawa ne ya dawo da Ummi cikin yaccinta, domin tayi nisa cikin k'unci zuciya da kukan zuci dana fili, k'irjinta na mata wani irin azababben zafi, wani irin bala'in kishi ne take ji yana taso mata, ashe haka ake ji?, ashe haka mata ke jin kishin nan?, ashe abun ba sauk'i ne dashi ba?, ita saurayi ne ma ba wai miji ba, inaga mijinta ne?, bata tab'a tunanin haka take da tsananin kishi ba sai yanzu. Domin tsabar b'acin rai da kukan da take ledar k'asan d'akin da take zaune akanta bata san lokacin data rink'a kamota tana yagata ba, sai da ta dawo yaccinta ta lura da yadda taci uwar ledar K'asar dama ba wata mai kyau bace, duk ci ubanta ta tsufa da yawa, sai gashi ta idasa cin ubanta.
Ganin kallon da Hali ke mata, kamar zatayi magana sai kuma tayi shuru tana sakkowa daga kan gadon.
A hankali Hali ta ce
"Ina buk'atar shayi ki had'u min, had'e da ruwan wanka ki saka min, zan fita da wuri ne yau".
Wata nannauyar ajiyar zuciya Ummi ta saki tana amsawa muryarta a shek'e, tana sake jin jikinta na d'aukar wani irin sanyi had'e da sarewa lokaci d'aya. Ta fahimci dai damuwarta damuwarta ce, a cikin gidan.
Da wani irin bala'in raunin zuciya ta mik'e ta nufi kitchen d'in tsakiyar gidan nasu.
Aikin gidan baya bata wahala, dan haka dandanan ta gama, ta share gidan ta d'ora mata ruwan zafin da take buk'ata, da shayin da Hali d'in ke so.
Hatta Umma dake da hawan jini tasan irin abincin da take ci, har kawo yanzu bata jin Ummar na amsa mata gaisuwa, d'aga kai kawai take mata a haka ne alamar ta amsa gaisuwar tata, lokacin da kuma take jin miskilancin ta ko duban inda take bata yi bare ta samu Umman ta d'aga mata kai.
Gaba d'aya gidan irin rayuwar da suke sai ya kasance kowa miskilin kanshi ne, saboda tsabar babu wata fira dake shiga a tsakaninsu, idan kaga ana magana a gidan ana fira to tsakanin Halimar ne da kuma Umma, hatta Baba Mlm ba wani sake masa suke ba, har yanzu Umman ta kasa manta irin abunda ya mata shekarun baya da suka wuce.
Yanzu Baba Mlm ya koma koyama almajirai dama Mutane da dama karatun addini, dama kuma can da baya yana d'aukar mutane da dama karatun addinin, shi yasa yanzu bai wani cika zama gidan ba, yana waje tare da D'alibansa da sauran jama'ar da yake d'auka karatu, ita kanta Ummi d'in wani lokacin shine yake k'ara koyar da ita karatun al'qur'ani da sauran littatafan Addini.
Zaune suke su duka a parlon gidan, sai Ummi dake waje tana sauran aikace-aikace daya rage bata idasa ba, dare ya fara har takwas da rabi, Mlm bai shigo ba.
Su Umma dake parlo tana iya jiyo yadda suka fira cike da raha, da ace zata je parlon kota matsa inda suke, yanzu zasu mik'e subar wajan, ko kuma suyi shuru subar maganar da rahar da suke, abun nan naci mata tuwo a kwarya, abun na damunta, sosai, ji take inama itace zaune da Mahaifiyarta kamar yadda Hali ke zaune da Umma suna fira da raha da annashuwa.
Darammmm dararammm k'arar harbe-harben Bindiga ya k'arad'e gaba d'aya wajan garin da cikin garin.
Ummi dake tsaye bata san lokacin data zubar da kayan wankin data yi su tun rana ba, sai yanzu data tsaya take idasa kwashe sauran.
Jikinta ne ya kama rawa, y'an Bindiga a yanzu tunkan dare ya tsala? mik'e faruwa ne?, mi suka zo yi a garin nasu Innallihi wa'inna alaihir raju'on, kawai Ummi ke fad'a a zuciyarta.
Ganin Hali ta fito daga d'aki ta rugu a guje ta nufi k'ofar gida, had'e da bankota ta rufe da sakata jikinta na rawa.
Ummi bata san lokacin data ce "Hali Baba bai shigo bafa".
Bata kalleta ba ta ce "shine ya kira waya ya ce ko mi muke mu tabbatar mun rufe gida, y'an Bindiga ne suka shigo garin nan, suna can tsakiyar titi sun kashe titin suna fashi, suna tare ko wacce mota dake tahowa".
"Shi Baba Mlm d'in fa yana ina?".
Wani duba tayi mata ta saki tsaki mai sauti ta ce.
"Wai da kike ta wannan abun wani kike fi sonshi ne?, baki ji miye na ce miki bane?, ce miki nayi ba cikin garin suke fashin ba, titi ne kawai suka kashe suna fashi. Shi kuma Baba Mlm suna waje a shigon dake waje shida D'alibansa sun rufo shagon suna ciki".
Wata irin ajiyar zuciya ta sauke tana sake furzar da Iska, tana ganin Hali ta shige d'akin Umma ta rufe k'ofar d'akin.
Kayan ta kwashe tana jin yadda suke sake sakin Bindiga k'arar Bindigar kanta wani tashin hankali ne.
Garin yayi shuru sab'anin harbin da sukai a farko yadda taji garin ya d'auki hayaniya had'e sautin guje-gujen mutane.
Da sauri jikinta na kyarma ta d'ibe kayan wankin ta shige d'akinsu dashi ta rufo k'ofar itama.
Zubewa tayi akan katifarta tana kallon gadon Hali da ita ce kad'ai ke kwanciya akansa, sai ita dake kwana akan katifarta k'asa.
Yadda take jin tashin k'arar Bindiga tasan ba k'aramin fashi suke ba, samun kanta tayi da addu'ar kariya ga bayin Allah, dama su kansu.
Sun kwana biyu basu ji d'uriyarsu ba, ashe suna nan basu daina addabar yanki su ba. Sufa Allah ma na sansu da basa tab'a shiga gidajan dake cikin garin Rimaye sai dai suzo suyi ta'asa iya bakin hanyar garin.
Wayarta ta jawo ta shiga wajan numbers, number Tasi'u take kallo ji take kamar ta goge komai nashi dake cikin wayarta, hannunta na rawa ta goge numbers, wajan hotona taje shima d'aya bayan d'aya hannunta na rawa tana jin wani abu na taso mata a can k'asan zuciyarta, bata san lokacin data ji hawaye na zubo mata ba, sai da ta gama gogesu tass kawai ta samu kanta da fashewa da kuka marar sauti.......
*RAUNIN ZUCIYA*
*©Zahra Royal Star*
*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*
EPISODE 3
*Ummi POV*
A hankali ta shiga bud'e idanuwanta da sukai mata nauyi saboda irin kukun data shi jiya, da kuma fargabar y'an Bindiga da suka shigo garin jiya, da rashin bacci da bata samu ba sosai a daren jiyan, domin sai wajan uku ta samu bacci ya kwasheta sai yanzu data farka jin kiran sallar asubahi.
Wata irin ajiyar zuciya ta sauke, a hankali ta mik'a hannunta na dama ta aje wayar dake hannunta har lokacin bata ajeta ba, da ita tayi bacci a hannunta.
Ajeta tayi tana mik'ewa jin jikinta a sanyaye ga kanta da yayi mata wani dummmmm. Da sauri ta tsaya tana dafe kanta da hannunta, domin tana mik'ewa tsaye taji wani irin azababben sarawar Kai.
Runtse idonta tayi da k'arfi tana d'an girgiza kan nata, idonta kansu sunyi jawur tsabar rashin bacci.
A hankali ta rik'e bango d'akin tana takawa a hankali zuwa tsakar gida domin shiga toilet.
Sai da ta d'auro alwalla tana jin sai lokacin taji motsin Mlm daya riga da ya fita sallar asubahin Masallaci.
Ta tabbata jiyan cikin dare ya shigo gidan.
A hankali take tafiya ta koma cikin d'akin nasu. Ita kad'ai ta kwana yau Hali na d'akin Umma, kuma har lokacin ba wadda ya bud'e k'ofar d'akin Umman.
Ta d'an juya tana kallon k'ofar d'akin Umman, kamin ta idasa shigewa d'akin nasu.
Bayan ta sallame sallar ta d'aga hannunta sama tana rok'on Allah tana kuka marar sauti hawaye na rige-rigen zubo mata akan kyakykyawar fuskarta.
Ta dad'e tana addu'a tana jin zuciyarta na rik'e nauyin data mata a k'irji.
A hankali ta sauk'e ajiyar zuciya, tana sauke idonta akan wayarta data ga haske ya kawo, message ne ya shigo, hannunta na kyarma ta kai ta d'akko wayar, Allah ya sani duk zaton ta zata ga sak'on Tasi'u ne, saboda kamin bacci ya kwasheta sai ta aika masa da message mai tab'a zuciya.
Amma sai taga sab'anin hakan, domin MTN ne suka turo mata message d'in. Wasu guntun hawaye ne suka zubo mata a gefen idonta, a hankali cike da sanyin jiki ta aje wayar tana d'an kwantawa a gefen katifarta, tana jin yadda zuciyarta ke azalzalarta ta kira shi. Danne zuciyarta take amma ina sai da ta kai hannunta ta d'auki wayarta ta rik'e numbersa, duk da jiya ta goge ta a cikin wayar tata, to ta riga da ta rik'eta a cikin kanta, sake sakata tayi ta danna number ta fara kiran number, jikinta na d'aukar rawa haka kawai.
Ringing take ba alamar za'a d'auki kiran nata, ringing d'aya idan tayi sai zuciyarta ta buga da k'arfi, har ya tsinke ba'a d'auki kiran nata ba.
Tayi mai kira ya kai sau uku ba'a d'auka ba.
Aje wayar kawai tayi tana jin wani bala'in haushin kanta a lokacin.