Auren Wata Uku Book Complete By Sameena Aliyu.doc

Author :  SAMEENA ALIYU Category :  Arewa Pen

Chapter   39 / 52

114K to 117K   out of 153.1K words

dalilin haka. Asshe Aliyu na ya aure  yar wann mutumin..! Ta kuma rushewa da kuka.

Asshe ta dubeta cikeda tausayawa  Aunty Kwaise mijinki loves you. Wllhi koda ace yayi aure bazai daina sonki ba. Ni fah ban taba ganin wacce mijinta ke mata irin Son da Uncle Engr ke Miki ba. He loves you dearly. Zai komai dan farin cikin ki Aunty Kwaise. Keda kanki kin fada Aurensa da wann yarinyar Fannah k addara ce kawai batada kowa bayan mahaifinta da ya Mutu ta dalilin aiki k ark ashin ma aikatan mijinki da yake. Wllhi na tabbata dan ya taimaketa ya aureta. Ba wai dan yana So ba ko dan ya daina sonki. Idan ba so da mijinki ke Miki ba. Mutum kaman Engr Aliyu matashi mai tashen kud i ga k uruciya ga dama na rayuwa da ya samu ai da tuni ya cika gidan nan da mata sai yanzu da k addarar hakan tazo. Dan Allah kar ki saka wani Abu a ranki.

Mommy ta dago tana share hawaye  Asshe bazaki taba ganewa ba. Namiji Akan mace sunansa namiji bazakiyi shaidarsa ba. Nidai bazan iya sharing Mijina da wata ba balle wann bagidajiyar  yar lebura.

Asshe ta furzar da huci  Toh ya kike so ai yanzu.?

Mommy bata iya bata amsa ba sai mik ewa da tai ta shige k uryar daki wani sabon kuka na taso mata.
Haka ta yini a daki bata aikin komai sai kuka. Asshe ke Lek ata lokaci zuwa lokaci. Ko abinci Mommy ta kasa ci ranan.

Can dare taji shigowar motar mijinta. Nan ta Mike da sauri tana lek en window. Hangosa tai tareda Amaryar sa tana biye dashi kanta a k asa. A haka suka shigo har parlorn gidan.

Koda Daddy ya shigo ya tadda Mommy juya masa baya tai. Ya k araso jikinsa duk a mace  Kwaise. My love.. Sai ya kasa ci gaba da magana yayinda kukan Mommy ya karu.

A hankali ya isa ya rungumeta ta baya. Su duka biyun hawaye na gangaro masu. Cikin kwantar da hankali yake furta  Wann shine k addarar mu Kwaise. Allah ya k addari Fannah zata shigo cikin rayuwarmu. Yarinyar abun tausayi ce bata da kowa sai mahaifinta da ya rasu sakamakon aikin da yake k ark ashina.

Mommy na hawaye take girgiza Kai  Ba hurumi na bane na tuhumeka dan ka k ara aure Aliyu. Addini ya halatta maka auren mata d ai d ai har hudu idan kanada hali. Kawai alfarmar da zan rok a daga gareka shine Kai Adalci tsakaninmu.

Ya murmusa yana dubanta. Ya saka hannunsa ya share hawayen da suka gangaro mata  I love you Kwaise.. So much..! Ban tab a son wata mace sama dake a rayuwata ba. Ki tayani addu a Allah ya bani ikon yin Adalci tsakaninku because.. I m not sure idan son da nake Miki zai barni na kamanta adalci.. Kwaise ba kece cikin tashin hankali ba. Ni ne cikin tashin hankali.. Because son da nake miki baida match da ko wace mace. When it comes to you wayona baida yawa Kwaise.

Mommy ta tsaresa da ido kafin ta k ak aro murmushi ta riko hannayensa  You can do this in sha Allah mijina. I m here for you.. Tashi na shiryaka amarya tana jira.

Kaman rak umi da akala haka Daddy ya Mike Mommy ta shiryawa tsaf harda su fesa turare kaman ba ita ce ta yini kuka a daki ba.

Koda suka fito suka tadda amarya ma Mommy bata nuna komai ba. Asshe taita mamakin canzawan  Yaruwar tata. A haka rayuwa ke tafiya masu Mommy bata nuna komai ga Daddy ya saki jiki ganin hankalin Kwaise ya kwanta. Ya maida hankali kan bunk asa k aramin kampaninsa a nan birnin Maiduguri da Kewaye.

Watan Fannah biyu a gidan ta fara nuna alamun masu juna biyu. Kwaise da kanta ta dauketa ta kaita asibiti akai mata gwaji aka tabbata tana d aukeda karamin ciki na tsawon watanni biyu. Sosai Mommy ta nuna marnanta har kaman tafi Fannah murna. Lokacin Daddy na cuku cukun Kai Kasuwancinsa tsakanin Abuja da wasu jihohi Mommy da kanta tai masa Albishir na cikin da amaryarsa ke dashi sanda sukai waya tinda shi a wann lokacin ya rage zaman Maiduguri. Farin ciki wajen Aliyu Maitama baya misaltuwa. A wann lokacin yai ma matan nasa kyauta ta sabuwar mota dal  yar yayi a wancan lokacin. Ya kuma d ebesu gaba daya suka tafi Umra suka gode ma Allah da kyautar da yai masu dan a lokacin aurensa da Kwaise kusan shekaru biyar kenan babu rabo saida Fannah ta shigo sai gashi ta samu daga shigowarta.

Bayan dawowar su daga Umra Daddy ya tafiya ta kasuwanci da zai d aukesa kusan wata guda.

Asshe ta dubi Mommy wacce keta faman sakin murmushi tana gustiran Apple. Ta d an girgiza Kai tace  Kenan kin yarda ta rigaki Haifa masa Magaji Aunty Kwaise.? Ni fah kirkikin da kike ma matar nan tai yawa. Ke kaman bakijin kishi irin na mata da ake fad a.

Murmusawa Mommy tai  Asshe kenan. Sarai nasan abinda nake kuma lokaci yayi da zan executing plan dina. Trust me.

Asshe ta girgiza Kai  Toh amma Aunty Kwaise mai zakiyi yanzu.?

 Wann cikin da Aliyu Maitama ke rawar k afa akansa da Kansa zai sheganta sa tin a ciki kafin a haifosa. Zai ma Fannah korar wulak anci. Wann cikin kuma Engr Aliyu Maitama bazai taba accepting dinsa ba.

Asshe ta girgiza Kai  Amma ta ya zakiyi hakan.?


Mommy ta kuma gyara zama  Uban Fannah labourer ne a kampanin Maitama. Bincikena ya tabbatar min akwai wani lebura matashi kuma abokin aikin mahaifinta dake mutuwan sonta. Hasalima saurayinta ne kafin iftila ain da ya samu mahaifinta ya samesa. Zuwa Kai ma mahaifinta abinci da take site a can Saurayin nata ya ganta ya fara sonta. Da uban ya Mutu mijina bai san da labarin tanada wani saurayi da suke soyayya ba Wanda shima yake aiki k ark ashin sa. danginta sukai wuf suka nuna masa batada kowa saidai ya aureta sabida tinanin zasu sami kudi. Ance sadaki suka yanka masa kaman dai mai biyan diya. Saida masa ita sukai. Fannah batada say ga danginta Wanda bayan rasa mahaifinta da tai ba rike ta zasuyi ba dole suka tilasta mata auren mijina dukda tanada Wanda take so. Dashi zanyi amfani na fitar da Fannah daga gidana dan ance har gobe yana mutuwan sonta.

Asshe ta sauk e ajiyan zuciya  Toh ya abin zai kasance.?

Mommy ta kuma murmusawa  Abin shine kece zaki taimaka min har komai ya kankama K anwata.

Asshe ta girgiza Kai cikin rashin fahimta  Kaman ya kenan Anty Kwaise.? Ki sanar Dani wane irin taimako zanyi dan nafi kowa burin matar nan ta fice daga gidan nan.

Mommy ta jinjina Kai suka tsara yanda zasu aiwatar da komai cewa Asshe ta tafi ta samu wann Saurayin suyi ciniki dashi da Mommy yazo gidan a ranan da Engr Aliyu Maitama zai dawo gari ya kamasa a d akin matarsa zai hau kan dik abinda ya gani ya zauna tinda su biyun tsaffin masoya ne. Ta k arashe tana sakin murmushi.

Da taimakon Asshe Mommy ta tsara komai har shigowa gidan da Auwalu tsohon Saurayin Fannah yai ba tareda kowa ya gansa ba.

Fannah da fitowarta kenan daga band aki tayi wanka cikin murnan mijinta na hanya zai dawo ya dubasu itada abin cikinta mai watanni uku a lokacin. Nan ta tadda Auwalu tsohon saurayinta kwance saman gadon ta daga shi sai singlet da gajeren wando. Jikinta ya d auki kyarma ta soma salati tana karanto Innalillahi. Kafin tai wani aune Auwalu yai tsalle ya capkota had ida toshe bakinta da k arfin gaske. Fannah tana kuka tana k ok arin kururuwa amma inaa ya toshe bakinta.

Daddy ya dawo cikeda d oki da murnan ganin matarsa mai juna biyu. Ko sashensa bai nufa ba ya fara nufan b angaren ta d aukeda tarin tsaraba irin Wanda mata masu juna biyu ke so. Nan ya tadda Kayan tashin hankali maras misaltuwa k ato rungume da matarsa dake d aure da towel ya toshe mata baki da hannunsa guda. Ga wani mummunar murmushi saman fuskarsa.

Daddy na huci yake duban mutumin Wanda ya saki Fannah bayan shigowan Daddyn. Ya duka jiki na kyarma yanda yake fad in Engr ya masa sutura dole Yai ma Fannah bada amincewarta ba fyade yai mata.

Daddy ya shak osa tamkar zai aikasa lahira ya kasa furta komai sai huci da kyarma da jikinsa keyi sabida b acin rai. Da kyar Mommy ta janye Daddy. Ta isa ta yafa ma Fannah mayafi ta rufe mata jiki wacce towel ne kawai d aure jikinta. Ta dawo ga Daddy tana fad in  Engr kar ka biyesa kar Kai kisa. You are not like him. Ni dama tinda yake zuwa gidan nan ban yarda dashi ba.

Daddy ya dubeta da mamaki  Dama ya Saba zuwa.?!

Mommy ta jinjina Kai kaman gaske  Ai idan Baka nan yakan zo. Da abubuwa na kwadayi irin na masu ciki yakan ce Kai ka aiko shi zuwa wajen Fannah. Sabida abinda take so yake sayowa.

Asshe da fitowarta kenan sabida hayaniyar da taji ta dubi mutumin da Daddy dake duke yana kyarma tace  A ah.. Wann mutumin ai mak ocin su k awata Baana ce. Kuma ta&  Sai tai shiru ta kasa ci gaba da magana.

Mommy tace  Kuma me Asshe.. Meye Baana ta sanar dake..?

 Ta sanar dani shi d in Saurayin Fannah ne Wanda mutuwan mahaifinta ya hana aurensu& Hasalima mahaifin Fannah kafin ya rasu ya masa alkawarin bashi ita..!

Daddy ya dago jiki a sanyaye yana duban Fannah wacce kuka yaci k arfin ta  Haka ne.? Wann D an iskan saurayinki ne.?! Ya tambaya yana dubanta.

Jin bata amsa shi ba ya sa ya kuma daka mata tsawa  Ki amsa min..! Haka ne..!

Auwalu ne ya bama Daddy amsa da fad in  Duk Wanda zaka tambaya Rankayadade haka ne. Fannah toshuwar budurwata tace da nake matuk ar so. Kuma mahaifinta ya min alk awarin bani ita.. Amma  yanuwanta Sun karya wann alk awarin sabida kwadayin abin hannunka. Saidai ni da Fannah bamu rabu ba.. Washe garin ranar da ta tare gidanka ma ba aiki na tafi ba gidanka na taho.. Kuma duk randa nazo mukan mu amalanci juna da yarda da amincewarta. Amma yau din ba da son ranta na aikata mata ba fyade nai mata sabida ta sanar Dani akwai ciki jikinta Wanda batasan nawa bane ko naka..! Bai Kai aya ba yaji saukar naushi a bakinsa. Duka Daddy yake Kai masa ta ko ina yana hawaye tamkar zai aikasa lahira A haka mai gadi ya shigo a guje yana sanar da Daddy window din section dinsa a fashe dik yanda akai b arawo ya shigo gidan. Dan shi dawowarsa kenan daga masallaci ya tadda haka.

Daddy ya ci gaba da huci  Ga b arawon a nan. Ya Saba shigowa Shayibu ba tareda kayi la akari ba. Yau da dubunsa zai cika sai ya fasa window. Ya damk a sa ma shayibu yana fad in bari yaje ya duba section d insa. Ai kaw nan Daddy ya tadda an fasa safe d insa na cikin gidan an kwashe kud ad en ciki.

Koda aka mik a Auwalu ma  yansanda bai yi musun shi ya kwashe kud ad en ba. Ya ce da taimakon Fannah ya kwashe kud ad en dan su gudu su bar gari.

Daddy bai saurara daga b angaren Fannah ba. Musamman da ya tabbatar da gaske Auwalu tsohon saurayinta ne kowa yayi wann shaidar.

Sosai take kuka duk e gabansa tana girgiza Kai tama kasa cewa komai. Mai ma zata ce bayan an kulleta ta ko ina. Daddy yaci gaba da jinjina Kai yana dubanta  Ki sani wann shegen da yake cikinki ba nawa bane. Kuma har Abada kar ki taba danganta ni dashi. Kije can keda wancan Daniskan ku rainesa a gidan Yari. Yana ida fad in haka ya mik e yana hawaye sosai. Bai wata wata ba ya tura su duka biyun gidan Yari.  Yanuwan Fannah suka barranta da ita cewa basu ba ita. Ta tona ma kanta asiri ta cuci kanta. A prison Fannah ta raini abinda ke cikinta har ta haifesa. Bayan faruwan haka da wasu watanni Mommy ta fara nuna alamu na masu ciki. Batai gaggawan sanar da mijinta ba Wanda tsawon shekarun da suka diba tare suna jiran wann batu mai dad in ji tin kafin shigowar Fannah cikin rayuwarsu. Yau gashi ta samu juna. Tasan Engr zai farin ciki fiyeda lokacin da Fannah ta samu. Tai shiru tana tinanin da Fannah tana nan k ila da an fara k irga ma abinda ta haifa watanni.

Suna hira itada Asshe wani rana, nan Mommy ke zayyano ribar da taci bayan ta k ulla ma Fannah Makirci gashi ta fice cikin rayuwarta cikin ruwan sanyi. Tabbas kwalliya ta biya kudin sabulu.

Sam bata San Daddy ya shigo ba take b arin zance.

Daddy ya dubeta da mamaki  Kwaise.. Sharri kikai ma Fannah.?!

Sai Mommy ta mik e tana girgiza Kai  A a Engr dan Allah ka saurareni.

 Mai zan saurara bayan abinda naji da kunnuwa na.. Ki bud e baki ki sanar Dani.. Sharri kikai ma mata..? Kece kika shirya komai..?!

Cikin kuka Mommy ke jinjina Kai  Wllhi Allah shine shaida na Engr sharri kawai nace yai mata.. Wllhi ban ban bashi umarnin wani abu bayan haka ba..

Gijif ya zauna cikin kujera yana jin duniyar na juya masa yayinda Mommy ta rarrafo zuwa gabansa tana Neman afuwa.

Mik ewa yai ya fice ba tareda ya dubeta ba. Kai tsaye prison yaje amma koda yaje ta gama sentences d inta an kuma sallameta bayan ta haihu sann babu Wanda yasan yanda ta tafi. Shima Auwalu babu Wanda yasan yanda yake bayan Sallamansa daga prison da akai. Haka Daddy ya zauna yana kuka sharshar da hawaye tareda nadaman hukuncin da ya zatar ba tareda yayi bincike ko ya saurara daga Fannah ba. Gaba d aya Mommy ta rasa gane kansa tin daga wann lokacin. Baya mata magana baya kulata baya shiga sabgarta. Kasuwancinsa ta soma girgiza bayan hab akar da tai sabida halin k unci da damuwa da ya tsinci kansa ciki. Daddy ya koma tamkar baya rayuwa cikin wann duniyar. Ya daina fita ya daina magana ya daina mu amala da kowa da komai. A haka Mommy ke rainon cikinta cikin damuwa da k unci hopping idan ta haihu zuwan D an cikin rayuwarsu zai canza komai. Har zuwa lokacin da ta haihu Daddy bai dawo normal ba. Yana nan jiya iyau ba um ba um um. Bayan Mommy ta haihu ta shigo da jaririn cikin hannunta tana hawaye take nuna masa  See burinka ya cika Engr ka samu Magaji and I named him after you. Aliyu Aliyu Maitama.. Zai girma ya zama Engr kaman Kai. Zai girma ya zama d an da zakai alfahari dashi.

Tin bayan abinda ya faru bai kuma duban cikin idonta ba sai wann lokacin.

Mommy tana hawaye take dubansa cikeda Jin dadin yau yau ya kalleta. Amma sai taga ko kallon jaririn dake rik e cikin hannunta baiba balle ya karb e sa. Sai ma mik ewa da yai a ranan ya koma aikinsa gadan gadan. Baya shiga sabganta balle na D anta sai hidiman bunk asa Kasuwancinsa da yake. K unci da damuwa suka taru sukai ma Mommy yawa tinda taga wann lokacin Mommy ta shiga damuwa kullum cikin kuka da tashin hankali take bata kula jaririnta Wanda tinda taga mahaifinsa bai amshesa ba. A nata zaton zai zamto makamin da zatai amfani dashi ta kuma janyo hankalin mijinta gareta. Asshe ita ke rainon Haidar. Hasalima ita take kiransa Haidar bayan mahaifiyarsa ta sanya masa suna Aliyu har Haidar ya bisa. Asshe ita ke kula da Haidar tamkar itace ta haifesa. Madararsa d awainiyarsa komai itace. Mommy kullum cikin kuka da damuwan wofantar dasu da ita da D anta da Daddy yai take. Ta duk ufa Neman Fannah dan ta nemi yafiyarta amma Fannah was no where to be found. Sanda Asshe tazo aure ji tai kaman ta tafi da Haidar sabida son yaron da take da tsoron barin sa tsakanin iyayen da babu shi a gabansu. Damuwar gabansu kawai suke. Burin Mommy shine Uban ya kalli d an matsayin D a da ko wani Uba ke alfahari dashi yayinda Daddy ya ta allak a ga bunk asa Kasuwancinsa. Wann dalili yasa kasuwancin Aliyu Maitama ya fiye masa ahalinsa dan wann Kasuwanci shi yai keeping dinsa going a tunaninsa bayan abinda ya faru dashi. Shi ya zame masa tamkar therapy. A haka rayuwa take tafiya ma wad ann bayin Allah. A haka Haidar ya taso ya tsinci Kansa tsakanin iyaye biyu Wanda baisan wani Abu mai suna soyayya tsakaninsa dasu ba. Koda ya soma girma Mommy kullum cikin tilasta masa yake yai abinda zai birge uban ko zai alfahari dashi yayinda Daddy bai tab a ganin k ok arin Haidar ba har kawo girman sa.

Wann kenan.

(Kar mai karatu ya mance kacaukam labarin nan an Ginasa ne kan  ya ya da Allah kan jarabcesu da iyayensu da kuma iyaye da Allah ke jarabtansu da  ya yansu. Wasu mutanen ana sanyasu ne cikin rayuwar sashe matsayin jarabawa).

*
Ci gaban labari..


Haidar ya share hawayen da suka zubo masa  So that s the reason why he hates me.! Ya fad i haka Kansa a kife.

Mommy tai saurin girgiza Kai hawaye naci gaba da gangaro mata  No Haidar.. Your Dad doesn t hate you.. He loves you.. In fact inada tabbacin bayan abinda na masa albarkacinka naci bai koreni ba.. That s just.. his way of punishing me.!

 Well I don t care.! Ya fad i haka yana mai

39 / 52