Author : Ameera Adam Category : Read Hausa Novels
daga babban kogin ƙasar misira, wasu kuma suka ce tushiyarsa tana da mahaɗa da babban kogin maliya. Sai dai kuma mafi yawa daga cikin masana da masu bincike, sun tabbatar da cewa wannan 'yar ƙoramar ta haɗa tushe da dukka kogunan guda biyu, daga na Maliya har na babban ƙasar Misira. Sai kuma wani shu'umin wani ƙanƙanin kogi da yake cikin dajin Buhul, wanda aka ce daji ne da manyan aljanu da rauhanai suke rayuwa. Wasu sun ce Kakan Sarauniyar Humaira yana da kyakkayawar alaƙa da aljanun wannan yankin, domin har yana da wani babban amini rauhani yake da shi. A saboda haka tun Sarauniya Humaira tana ƙarama kakanta ya kan je wannan dajin da ita, idan ya kai ta sai ta shiga cikin ƙoramar nan ta yi ta wasa tare da sa'anninta 'ya'yan aljanun wancan lokacin.
Amma da labari ya faɗaɗa sai wasu suka ce wata lalura ce ta shigo da wani tsohon rauhani ta masarautarsu Sarauniya Humaira, a nan mahaifinta ya taimaka masa da maganin jinya har ya warke. Saboda mahaifinta tun yana ƙarami yake da baiwar sanin itatuwa da ganyaye domin warkar da masu lalura, kuma tun da rauhanin nan ya warke sai ya bayyana masa kansa, suka cigaba da abota har mahaifinta yake kai ta wannan dajin suna wasa da yaransa. Akwai tarin mabambamtan bayanai dangane da zuwan ƙoramar cikin fadar Sarauniya Humaira, wasu masana binciken tarihi suka ce a ziyarar da take zuwa dajin ne wani hatsabibin aljani ya ce yana sonta. Wasu kuma suka ce ba sonta yake ba, sadaukar da jininta zai yi ga wani boka da yake yi wa tsafi a wancan lokacin. Dalilin haka ya sa rauhanin nan amini mahaifinta, ya samar mata da haɗakar koguna ukun nan a cikin fadar mahaifinta. Wasu kuma suka ce ba haka ba ne domin dalilin yana ƙunshe cikin littafin 'Ruwa A Wuta' Wanda aka binne ta da shi, dalilin mutuwarta, da wasu abubuwan almara da take gudanarwa. Tare da tarin bayanan wasu al'amura na duba da ta yi kuma ta rubuta da za su faru a shekaru masu zuwa bayan mutuwarta. Sai dai shi kansa rubutun littafin an samu rarrabuwar kai game da shi, wasu suka ce Sarauniya Humaira ce ta rubuta littafin da hannunta. Yayin da wasu suka ce ta yaya za ta rubuta labarin mutuwarta? Bayan kuma tana raye, tun da an ce har dalilin mutuwarta da ƙalubalen da za a fuskanta a game da zuwa kabarinta duk ta rubuta. Waɗanda kuma suka yarda da cewar ita ta yi rubutun, sun ce ba abin mamaki ba ne tun da tana rayen ai tana da baiwar faɗar abin da zai faru a gaba kuma ya tabbata.
Sunan littafin 'Ruwa A Wuta' Yana da nasaba da ƙoramar fadar Sarauniya Humaira, a lokacin da Sarauniya Humaira tana raye idan ta so yin duba ko nishaɗi ta kansa a ɗebar mata wani ruwan daban na cikin masarautar ta zuba a cikin ƙoramar, tana zubawa sai nan take tsakiyar ƙoramar ta kama da wuta, kuma a zagaye da ita ruwan da ke cikin ƙoramar bai fasa kaɗawa ba. Haka kuma duk wanda ya yi ganganci taɓa wannan ruwan a nan take jikinsa yake sandarewa, daga nan numfashinsa ya ɗauke gabaɗaya. Kuma tun da wannan al'amarin yake faruwa, ba a taɓa jin Sarauniya Humaira ta furta kalma ɗaya game da hakan ba, kuma ba ta taɓa gargaɗi ko jan hankali ga mutane a kan su kiyaye wannan ƙoramar.
Tun daga ranar da aka tsinci gawar Sarauniya Humaira, sai aka ga ƙoramar tana ci da wuta. Sai ruwan ya fara kwarara daga cikin raminsa, haka ita ma wutar ta fara ƙaruwa. Ana tsaka da tsoron halin da aka tsinci kai, sai aka ji irin muryar Sarauniya Humaira daga sama tana shela da bayar da umarnin da a haƙa babban ɗaki mai girma, a kuma sassaƙa mafi gajartar bishiyar kukar da ke Masarautar, kamar yadda ake sassaƙar jirgin ruwa a fafe cikinsa. Sai a saka gawarta a ciki, akai ta ɗakin da ke tsakiyar ƙoramar a binne, tare da wannam littafin da suka gani.
A cikin kaso casa'in da labaran da ake kawowa, an ce Sarauniya Humaira musulma ce. Yayin da mahaifinta ya kasance ƙungurmin kafiri mai bin addinin gargajiya. Wasu kuma suka ce, ita ma tana bin addinin gargajiya saboda a ra'ayinta tana ganin don mutum ya yi haɗakar addinan da yake so ba kuskure ba ne. A lokacin da aka binne ta an ce mutanen da suka yi wannan aikin babu wanda ya rayu, tun daga wannan ranar duk wanda ya shiga ɗakin sai dai a nemi gangar jikinsa a rasa ba tare da an sake ganin wulgar ko mai kama da shi ba. Tun daga nan sai malamai, bokaye da 'yan tsibbu suka shiga fagen binciken abin da yake haddasa haka. Sai da ƙyar suka gano mafitar da za ta sa a kamo bakin zaren ga duk wanda yake da buƙatar shiga ɗakin gawarta, shi ya sa a duk lokacin da mutum zai shiga domin neman biyan buƙatar kansa, ya zama wajibi ya tafi da wanda zai sadaukar da jininsa, ma'ana suna zuwa ɗakin ya fara hankaɗa shi sai daga baya shi kuma ya shiga ya yi abin da zai yi. Tun da aka binne Sarauniya Humaira, ba a taɓa samun mahalukin da ya yi gangancin buɗe cikin kabarin ba. Saboda yadda kowa ya san hatsabibancin ɗakin, da mummunan al'amarin da zai biyo baya. Duk da a hakan ma yawan shigar da ake yi ya haddasa musu abubuwan masu yawa, daga ciki har da ambaliyar ruwa, mutuwar jarirai akai-akai da gurɓatar ruwan kogunan yankin. Tun daga lokacin ne aka haramta wa mutane shiga ɗakin, da niyyar neman biyan buƙata ko yin wani abu.
Sarki Dikko
Sarki Dikko yana nan tsaye yana nazari, ya ga bawa Bukar ya shiga hannunsa ɗauke da daron abincin dakawansa. Sai da ya russuna har ƙasa sannan ya ce, "Allah Ya taimake ka, Allah Ya ƙara maka lafiya. Barka da hutawa uban gidana maganin kukana, Allah Ya ja da kwana ya raya mana Yarima da Sarauniya lafiya."
Farincikin Sarki Dikko ya faɗaɗa har a fili, cikin murya ƙasaita ya ce.
"Bukar a kai daron nan a dawo muna buƙatar ganinku."
Cike da girmamawa bawan ya sake zubewa a ƙasa ya ce.
"An gama ranka shi daɗe, ni mai bin umarninka ne."
Murmushin cimma nasara Sarki Dikko ya saki, yana nan tsaye babu jimawa bawan ya dawo yana jiran umarninsa. Itace ya ce ya kunna, sannan ya nuna masa hanyar nufa tsohuwar fada, gaban bawan ne ya faɗi amma sai ya dake ya cigaba da bin umarnin uban gidansa har suka ƙarasa jikin siririyar hanya mai duhun gaske, wacce za ta sada su da tsohuwar ƙofar fadar.
"Rarr... ranka shi...daɗe... tsohuwar fada za mu shiga?"
Bawan ya furta bakinsa yana rawa cike da tsoro, kallo ɗaya Sarki Dikko ya yi masa ba tare da ya tanka masa ba. Nan take ya haɗiye kalamansa, yana jin zuciyarsa tana harbawa kamar za ta ɓullo daga ƙirjinsa.
Ƙofar jikin tsohuwar fadar ta yi ƙura sosai, har yana ta yanyame ta gabaɗaya tare da ƙananna ƙwari. Kallon bawan ya yi, da yake ya fahimci abin da yake nufi nan take bawan ya saka hannu ya fara cire yanar da hannunsa, sai dai kallo ɗaya za ka yi masa ka fahimci kwanciyar hankali ta yi bankwana da gangar jikinsa. Sai da ya gama cire yanar, sannan Sarki Dikko ya zura kuba ya fara cire sakatar ciki, wata irin guɗa suka ji cikin zazzaƙar murya mai daɗin sauraro. Sai dai ƙara da kauɗinta yana addabar kunne kamar zai tarwatsa shi, hakan ne ya sa daga Sarki Dikko har bawa Bukar suka toshe kunnuwansu. Sai da suka ji guɗar ta tsagaita, sannan ya cigaba da buɗewa, duk da zuciyarsa tana harbawa sama-sama.
Yana jin ƙofar ta buɗu ya tura ƙauren, nan take wata walƙiya ta haske idanunsu wacce ta sa suka hangi wata mace a tsaye sanye da alkyabba kanta yana kallon sama. Ganin haka ya sa hantar cikin Bawa Bukar ta kaɗa, cikin shammata Sarki Dikko ya hankaɗa shi cikin ɗakin. A karo na farko Sarki Dikko ya ji wata tsawa da ta nemi hargitsa kwanyarsa, duk taurin zuciyarsa sai da ya ji tsoro ya ɗarsar masa. Amma da ya tuna abin da yake tafe da shi, sai ya furzar da iska daga bakinsa wata sabuwar ƙwarin gwiwa ta mamaye shi. Tun lokacin da Sarki Dikko ya hankaɗa Bawa Bukar bai sake jin motsi ba, cikin sanɗa ya dinga takawa yana haske ɗakin da itacen ɗakinsa. Ɗakin ya yi ƙura sosai, duk inda ya taka sai ya ji sautinsa tare da tashin ƙura da yanar da yake cin karo da ita. Sannu a hankali ya fara jin tashin busar sarewa, sai kuma yake jin motsi daga cikin kowacca kusurwar ɗakin. Ajiyar zuciya ya sauke a ɗan tsorace, ganin baƙin al'amuran suna neman zautar da shi ya sa shi tunkarar ɗakin da aka saka gawar Sarauniya Humaira. Sai dai yana ƙarasawa wurin ya ga wutar cikin ɗakin kabarin ta kama, take ƙoramar da ke zagaye da ita ta bayyana. Kamar yadda ya samu labarin yanayin yadda aka ajiye sassaƙaƙƙiyar bishiyar kukar da aka saka gawar Sarauniya Humaira, haka ya gan ta har lokacin da yake komai na ɗakin ana hangowa daga waje. Sai kuma ya hango littafin da ya shigo ɗauka yana kallon kabarin, a lokacin ya faɗaɗa fara'arsa ya cigaba da kusa kai cikin ɗakin har ya ƙarasa wurin bakin ƙofar shiga ɗakin kabarin. Hannunsa ya kai kan ƙofar, lokaci ɗaya ya ji wani zum! Tamkar yadda wayar wuta take jan mutum, yarfe hannu ya gama yi ya sake miƙa hannunsa. Sai dai ga mamakinsa a lokacin babu abin da ya ji, kansa tsaye ya shiga cikin ɗakin da zummar ɗaukar wannan littafin. Bai yi tsammani ba ya ji jiri yana ɗaukarsa, yana shirin dafa bango sai gani ya yi ƙofar ɗakin da ya shigo ta shafe. Harshen wutar da ke gefen kabarin ta yi tsayi zuwa gabansa, a razane ya ja da baya yana sauke ajiyar zuciya. Yana cikin wannan yanayin sai gani ya yi hasken wutar ya ɗauke, daga wurin ƙafafuwansa ya ji wani irin ruwa mai sanyi yana kwararowa jikinsa har zuwa saitin maƙogaronsa.
Masarautar Judala
Ba iya Indo ba hatta ragowar bayin da ke tsaitsaye sai da tsoro ya mamaye su, cikin sauri wasu mata suka yi ta maza suka ƙarasa kan matar. Ɗaya ce ta shiga kiciniyar cire jaririya Batul, sai dai jin yadda jaririyar take shan maman cikin kwanciyar hankali ya sa ta dubi ɗayar ta ce.
"Allah sarki, dubi yarinyar nan ashe yunwa ce. Yanzu yaya za mu yi da ita?"
Cikin sauri ɗayar matar da ke shafawa matar da ke kwance ruwa ta ce.
"Maza cire ta Dago, ba ki ga halin da take ciki ba?"
Da sauri wacce aka kira da Dago ta shiga kiciniyar cire jaririya Batul daga jikinta, sai dai ita kanta abin ya ba ta mamaki yadda jaririya ƙarama take yunƙurin fin ƙarfinta. Ta ɗago tana shirin sanar da su halin da ake ciki, sai ta ji ta yi nasarar raba jaririya Batul da matar. Sai dai babban abin da ya sake ɗaga hankalinsu ganin bakin jaririyar kace-kace da jini, a razane duk suka ja baya. Cikin rawar muryar Dago ta ce.
"Ku taimaka ku raba ni yarinyar nan don Allah." Ta ƙarasa maganar hawaye yana zuba.
"Don Allah ki kula mini da Batul, tamkar yadda za ki kula da 'yar cikinki. Na damƙa miki amanarta, don Allah kada ki ci amanata."
Indo ta tuna kalaman Karima, jiki a sanyaye ta matsa gaban matar ta ce.
"Kawo ta."
Dago tana miƙa wa Indo jariraya Batul suka ga matar da ke kwance a ƙasa ta ɗago, gumi ne ya shiga keto mata tana sauke ajiyar zuciya.
"Wannan wacce irin irin yarinya ce saboda Allah, ku dubi yadda jini yake fita ko dai idanuna ne? Ke yarinya an ya kuwa ba ki da haɗi da maita?"
Wata gajeriyar mata ta faɗa a tsorace tana sake leƙa fuskar Batul da ke mamular baki, amma da yake hankulan mutane yana kan matar sai ba su bi ta kan Batul ba.
"Wallahi tun wuri ki koma wurin can ki ajiye musu 'yarsu, don wallahi yarinyar nan ba mutum ba ce. Idan kuma ba haka ba, wallahi za ki kuka da kanki."
Zinaru ta furta wa Indo cike da jan kunne, idanun Indo suka ciko da ƙwalla. Zuciya ta shiga raya mata a kan ta je ta mayar da jaririya Batul, tana cikin wannan nazarin ta ji ana yi wa matar sannu.
"Oh ni jikar mutum huɗu, sannu Zuwaira kin ji."
Wata 'yar uwar matar ta furta, Zuwaira da ta ɗago a galabaice ta ce.
"Ku kawo mini jaririyar nan, don Allah ku ba ni ita. Wallahi ita ɗin ta dabance, don Allah kada ku nisanta ni da ita."
Da mamaki suka dinga bin ta da kallo, Indo da Batul ke hannunta ta sake ƙanƙame ta.
"Ke yanzu ba ki dubi halin da kika shiga ba, amma kike ƙoƙarin gayyato wa kanki mutuwa? An ya kina cikin hankalinki kuwa Zuwaira? Ko da ma can haka kike shayarwa?"
Wata mata ta yi caraf ya karɓe zancan, Zuwaira ta dube su sai ta saki murmushi ta ce.
"Da kun san wace ce ita..." Sai kuma ta yi shiru, ta gyaɗa kai ta ce.
"Eh haka nake goyo na, wani lokacin idan ina shayarwa yana jini, idan hakan ta kasance har suma nake yi. Na taɓa tambayar wani mai magani, ya ce mini cuta ce. Ina gab da komawa karɓar magani aka kamo mu."
Lokaci ɗaya jikin mutanen wurin ya yi sanyi, tausayin Zuwaira ya mamaye su. Sai suka ɗauke mummunan zargin da ke zuciyoyinsu a kam Batul, jin Batul ta fara motsi ya sa Zuwaira ta dubi Indo ta ce.
"Miƙo mini ita yarinya na shayar da ita."
Girgiza kai Indo ta yi, don haka kawai ta ji ba ta gamsu da amsar da Zuwaira ta bayar ba. Cikin muryar kuka ta ce.
"A'a ina tsoron kada wani abu ya sake samunki."
Suna cikin haka, wata mace ta yi ƙasa da murya ta ce.
"Amma can kamar garken awaki ne, me zai hana mu tatso mata nonon akuya ta sha."
Kallon kallo aka shiga yi wa juna saboda tsoron kashedin uwar bayi, ganin haka ya sa Indo ta nufi wurin Dogarawan da ke can nesa da su. Tun ba ta buɗi baki ba, wani Dogari ya buga mata tsawa da cewa.
"Ke wanne irin kunnen tsiya gare ki, ba cewa aka yi ki zauna a cikin 'yan'uwanki ba?"
Baki yana rawa Indo ta ce, "Don girma Allah ku lamunce mini na tatsi nonon akuya zan shayar da jaririyat..."
Tun ba ta rufe baki ba, Dogarin ya zuba mata dorina a bayanta. Azaba da gigicewa suka sa ta yi baya ta faɗi, don kaɗan ya rage jaririya Batul ba ta bugu da ƙasa ba. Da ƙarfinsa ya ƙarasa gabanta ya sake ɗaga hannu ya zuba wa Indo dorinar dukan dokin, ta yi saurin sunkuya don kada ya samu Batul da buguwar da suka yi, ta sa ta yin shiru kamar ta san abin da yake faruwa.
"Au tare mata za ki yi? Shi ne kika zagayo ta bayana? Ai kuwa wallahi za ki gane ba ki da wayo."
Indo da sauran Dogaran suka ji ya faɗa yana waigen bayansa, ko kaɗan babu wanda ya ga kowa. Don haka ɗaya daga cikinsu ya ce, "Kai Mamman, wai lafiyarka kake magana kai kaɗai?"
Tun bai gama maganar ba, suka ga Dogari Mamman ya fara kai duka yana nausar iska. Tun suna ganin abin kamar wasa, sai suka rufa masa baya suna kiran sunansa. Daga haka suka ji ya saki wata gigitacciyar ƙara ya faɗi ƙasa yana shure-shure.
Ganin hankalinsu ya tafi kan wurin da Mamman yake, ya sa Indo ta yi saurin rarrafawa cikin garken awakin. A cinyarta ta zaunar da Batul, da saka hannu ɗaya tana tatsar nonon wata ƙatuwar akuya tana tara da ɗayan hannunta. A hankali take ɗisa mata a baki, nan da nan Batul ta shiga tsotsa tana ba ta har ta lura da ta ƙoshi, tana gama shayar da ita babu jimawa bacci ya yi awon gaba da ita.
Ajiyar zuciya Indo ta yi, ta zuba wa fuskar Batul ido, ta ɗaga hannu cikin muryar karaya da kai kuka wurin Ubangiji ta ce.
"Ya Allah ka ga kyakkyawar niyyata, Allah ka taya ni rainon wannan baiwa taka. Idan ma ba mutum ba ce kamar yadda zuciya take raya mini, Allah kada ba wa ahalinta ikon cutar da ni." A hankali ta shafa a fuska, sannan ta miƙe ta fito daga cikin garken awakin. Ta ƙarasa wurin ragowar bayin ta zauna, sai dai kallon da Zinaru take yi mata ya sake sanyaya mata jikinta. Haka suka ci gaba da zaman jigum-jigum har aka fara kiran sallar asuba, kuma a daidai wannan gaɓar labarin kisan wulaƙancin da aka yi wa gawar Dogari Mamman ta riske su. Indo ba ƙaramin kaɗuwa ta yi da jin irin kisan da aka yi masa ba, tana cikin wannan jimamin Uwar Bayi ta ƙarasa ta ingiza ƙeyarta da jaririya Batul ba tare da ta san dalili ba.
_MTN AND AIRTEL DATA AVAILABLE...!!🔥_
Monthly data — valid for 30 days
_📶MTN DATA_
• 500MB — 450
• 1GB — 700
• 1.5GB — 1000
• 2GB — 1,300
• 3GB — 1,900
• 5GB — 2,100
_📶AIRTEL DATA_
• 1GB — 750
• 2GB — 1,400
• 3GB — 2,150
• 3.5GB — 1,800
• 5GB — 2,850
• 6GB — 2,900
• 10GB — 5,600
𝙋𝙖𝙮𝙢𝙚𝙣𝙩 :
Opay — 7049439332
AFNAN