Author : Nana Kanwar Soja Category : Tknovels
akawa Commender Hafeez transfer aikin sa zuwa Kano tiket na jirgin Kano aka kawo guda ukku cikin mintuna talatin suka dushi airport dukansu Hajiya Hauwa ce a gaba hannu Abba ya sama ta ta dakata.
" Ya dai Abban ZEE "? kallo ɗaya ya mata ya kau dakai" no Hauwa ba zakiji ba daga ni sai ZALFAT da Hafeez da kuma MAI CIKI chan " yana nuna HABLAT da hannu suna haɗa ido ta sakar musu murmurshi " shi kuma ZAYYAN " da sauri ya rigi hannun Abba
"Please Abba kayimin rai wallahi bazan iya barin kusa da ZALFAT ba kar na kuma rasa ta "tausayi ne ya cikka rai na Abba "okay son kar ka damu daman ya kamata kaji gida don ka nitsu ka shirya sai ka taho " Hafeez ne ya murmusa "Abba ba komai a chan ma zaifi samu nitsuwar."
"To ai shikkinan yauwa su kuma wanchan da mara lafiya ya za'ayi dasu kinan Hafeez "? juyawa yayi yaga PAYAM dake kwance a bayan mota da kuma ANBAR sai Latu dake tsaye kusa da ita da sauri ya juyu " ya'laɓai ba matsala tunda a tare muka gansu ya kamata suma mu tallafa musu bayan sun samu nitsuwa kowacce ta samu dangin ta ".
Murmurshi Abba yayi waya latsa yasa a kunne magana cikin minti biyu sai ga wasu da uniform sun iso garisu " yalla'bai the plane is ready " da ƙwarin guiwa suka miƙi a hankali kowa ya shiga jirgin Abba ne ya tsaya ganin Hajiya Hauwa ta murtuƙi fuska shima haɗa rai yayi " Hauwa ke ɗauki ZEE nan ga sojojin nan ko kuma gida sai na dawo "
Yana faɗan hakan ya shiga ya barta fayau a tsaye tana ji tana gani ta glass nin gun jirgi ya ɗaga sai Kano kama kanta tayi ta rusa ihu "waiyoo Allah na shiga ukku a tsanaki wasu sojoji suka matso don tabbatar da lafiyar ta ashar ta waworo ta maka musu wane daga cikin su daki akwai zuchiya sauran ƙiris yakai mata bugu a fuska da sauri ɗayan ya jasa da "hi dudde matar General ce fa " so what dude " ya faɗa ciki da ɓacin rai direct gida suka wuce a inda ta tsunduma gida Hajiya Talatu wacce taki shirrin zuwa gidan ta ..
KANO
Suna isa airport manyan motoci suka hallara da wasu dakarun sojoji direct wani katafaren gida suka hallara duk sunyi shiru HABLAT ce taga ZALFAT duk da tasan da wuya ta mata magana ga kuma Amrat dake kusa da ita
"Wai sunan ke ZALFAT ko " ta faɗa cikin raɗa a kunnen ta Amrat ce ta tsora ido don ta kasa fahimta ZALFAT ce ta murmusa a hankali ta dube ta tayi shiru ɗan tsaki taja " ne wallahi dana ganki MAI CIKI CE sai da na razana musamman ma danaga kina ta liƙimai nace ko kishiya Abban Majhat yamin bansaniba ashe wanchan doctor ne mijin ke
"Dariya Amrat tayi don a wannan lokaci da ƙarfin ta ta faɗa ita ma ZALFAT nin dariya ta mata ganin haka ita ma dariyar taye " wallahi kuwa in gayyamu ko wani labarin hankalin na ya tashi sosai na ringa kuka ina birgima sai ya taho dani ko na hau sama na faɗo shine yazo dani don so naki naga MAI CIKI CE "
Duk dariya sukayi a wanan karon har dimple na ZALFAT ya lotsa Amrat ce ta motsa da cewa duk da ke MAI CIKI CE amman kike wanan abin yaran "? harara ta buga mata da cewa " amman ke baki da auri ko "girgiza kai tayi " murmurshi HABLAT tayi "shiyasa bazaki sani ba amman ya kamata ƴar uwar ke ta sanar miki duk mace da ta amsa mace komai shikkarun ta yarinya ce a gun mijin ta ya mata goyo ya mata wanka abinchi har a baki kedai bare wallahi aure yayi a a rayuwa ko ZALFAT "?
Nan ma dariya suka sa ZALFAT ce ta kwantar da kanta akan kafaɗar HABLAT sai ga wani siriirin hawaye a idon ta da sauri ta gogge tun kafin su a kanra " wai me sunan ke ne " murmurshi HABLAT tayi "a yanzu da na kasance MAI CIKI CE banda suna sai Umman Majhat " duk murmurshi sukayi ta chigaba da hirar ta ita ɗaya suna taya ta da smiling.
Babban falour duk anan suka haɗa zango sai dube dube HABLAT taki kamar mai neman abu Abba ne yayi gyaran murya nan suka mayar da hankalinsu akan sa " Hafeez muna neman taimako ka tunda Iyayyen ka suna nan cikin Kano da ka taimaka ka kawo su nan su zauna da yaran nan kaga babban hatsari ne barin su hakan nan ba tareda babba ba tunda duk fitta zamuyi duk da cewa ga wanan ita ma dai ba wata babba har chan ba "
Yana ' nuna Lattu da ta rufe illahirin fuskarta yanda ba wanda zai ga wacce ce ANBAR ce ta durƙusar da kanta tunda Abba yayi nuni da inda suki taka sa samun sukunin haka Abba ya tsara komai dake gidan mussaman aka kawo wata likita a wanan ranar domin kula da wanda basu da lafiya na kusa musamman shi PAYAM da har yanzu bai farfaɗo gaba ɗaya ba ,
Kafin dare komai ya hallara na abin buƙata Inna na zuwa HABLAT dake kwance tamkar a tsorachi ta miƙi da ɗan hanzarin ta tana farin ciki "kai Alhamdullah duk tunanin na mutanin mu sayar damu zasuyi irrin wanan katafaren gidan haka ai bazan iya kwana ba amman tunda ga Inna barchi harda minshari."
Ɗaki ɗaya Inna da ZALFAT sai Lattu daga ɓangaren ɗaya kuma HABLAT da Amrat sai ANBAR da PAYAM Hafeez da Zayyan sunwa kansu masauki don da farko Zayyan yasu zama da ZALFAT sai dai halinta daki basu mammaki na nan bai kushi ba sam taƙi yarda da zama a kusa dasu balle ta musu magana.
BORNO
Sanyi taki cikin shigar jajjayen kaya sai kanta da babo mayafi akai ta tunƙushi ƙafafuwan ta idon ta ta ɗaga sama nan suka haɗa ido da Hajiya Talatu murmurshi ta saki mata , Hajiya Talatu wata mata ce da ta kasance gajeruwa sai ƙiba ta sama gani taki duk duniya itace sarauniya mussaman a cikin gidan ta da taki da ikon komai sai abinda tace babo wanda ya isa ya ja mata birki don ko iyaye ta shakkar ta sukiye.
Kayanta ta cire ita ma ta sauya da irin tufafin daki jikin Hajiya Hauwa bata ce komai ba ta zauna a ƙasan hannu dama Hajiya Hauwa ta sa akan ƙafarta Hajiya Talatu ne ta haɗa hannun da mata suka rigi juna da hannu ɗaya ta jawo wane jaka suka haɗa hannu biyu biyu gun buɗiwa wani madubi ne suka zaro a hankali suka jingini akan dutsen da sukawa penti da red wasu surutai sukayi a tare sai ga hayaƙi na fitowa daga cikin madubin a hankali suka sa yatsan manuniyya suka shafa madubin nan da nan ɗakin ya fara wasu sambatu kayan ciki na girgiza girgiza ƙara rigi hannun juna sukayi duk da Ac daki ɗakin bai hanasu zufa a fuskar nan ta suba.
Wani farin mutum ne ya bayyana a madubin duk jikinsa da baƙa ƙin tabu sai ƙananan idon sa farin fatar sa kamar na baturen zogale duk wane abu daki jikin sa ya kasance red ne sai gashin kansa da ya barbarza har saman wuyar sa bakin sa ya buɗe ya tinzure da muguwar dariya nan bakin sa ya buɗu da ya kasance babo haƙuri ko ɗaya a cikin bakin nasa tsagaita dariyar yayi ya nuna su da yatsa
"Ke Hauwa !!! kinyi kuskure kijera sakamako tabbas wannan karon akaiw gagarumin matsala " hanjin cikinta ne ya kaɗa " na rantse zan maka komai komai kakiso zan tura maka ko nawa ne banason asiri na ya tuno inason a kashi min ZALFAT ta bar duniya ko nawa kaki so zan tura ma "
Ta faɗa jikinta na rawa nan tsayawa yayi chak ya turnu'ki da dariya " aikin ke ya kamala ke turu million goma zan turu Aljanna Bul Bul ( ta cikin littafin DUHU CIKIN HASKE ) da saƙo ke tabbatar kin sanyawa ZALFAT a cikin abincin da zata ce ɗayan kuma turare ne wanda aka samu shi daga zamanin daular Uthmaniya a lokacin mulkin Ziya'u ɗan Barda'u ke tabbatar kin fessa a dai dai ramin maciji sauran turaren ki sanya a jikin ke da zaran ZALFAT ta shaqa to ta tafe har abada bazata dawo ba sai kuma ki shirya haɗuwa da ita a ranar tashin alkiyama "!!!
"Wannan kuma daga cikin madubin ya harbi wani laya sai gashi ya faɗo ku tafe chan bayan gari ku sami jan ƙadangare ku buɗe bakin sa kusa wanan layar a cikin idan ku yi hakan aikin ku ya kamala " Hajiya Talatu ce tayi jarumta magana domin ita kam Hajiya Hauwa ta jima da sumewa a zaune
"Ranka shidaɗi gaggara badau uban ƙagararu kaci ɗaya kaci biyu kaci dubu ka zauna lafiya namiji uban mazaje komai wuyan aikin ka aikin ka yana tashi kuma yayi kyau yalla'bai ina zamu samu ramin maciji bazamu iya ba muna neman alfarmar ka daka aminci ka lamunchi da izinin ka da yardar ka wanan aikin ka baiwa aljannun da ka aminta dasu su aiwatar mana "
Bushewa da dariya yayi a wanan karon yayi shiru " aiki ya kamala ina ganin saƙo zaku ga naku saƙon yana faɗar hakan ya ɓacce ɓatt hannun su suka sauki nan suka cire kayan tare da ajiye wanan madubin a ajiya na musamman inda bawanda yasan da zaman sa ( sai ƙanwar soja kuma sai na ɗauko ahtooooo 🤣)
Ruwa Hajiya Talatu ta bata tana sha tayi ajiyar zuciya " hummmm ƙawata a wannan karon aikin mu na da wahala " kallon ta tayi "bazaki gani ba Hajiya Talatu kuɗin ne ma matsala ta yanzu don rabon da Alhaji ya bani kuɗi na manta ko na tambayi shi a banza ".
"What lallai Hajiya Hauwa kina wasa da lokachin ke meyasa baki gayyamin ba ai da bokan mu ya sabunta miki aikin ko hanun ɓera sai muyi masa ko zamu samu kuɗin ko? " zan gwada hakan but akaiw five million a account na idan ya dawo daga Kano sai musan abinye daga nan zanyi maganin shigiyar yarinyar nan mai siffar mayu " dariya sukayi duk suka tafa suka chigaba da hirar su ta yanda zasu warware matsalar dake gaban su ..
BORNO CLUB
"Haba Baby Zee kina nufin kumawa zakiye bazamu kwana ba why me yasa kike min haka ne anytime any day sai dai nayi ta fama daki and then kingi ke ɗanɗamin zumar ke you know i love you fa right" ya faɗa yana zura hannun sa cikin have vest na ta white da akawa adon stones a gaba a inda kafaɗanta yayi sama da rigar ɗayam kuma yayi ƙasa sai tsayin da bai rufe chibiyar ta ba , mini Jen's nata ta shafa a baya nan ta fitto da ƙaramar wayar ta,
" Am talking baby " nan duban sa tayi " you know what honey ba haka ba ne kasan "noo kullum haka kiki cewa and then yanzu Daddy yana Kano me abin damuwa Mommy ba faɗa zata ye ba '"look nifa ba haka naki nufi ba ka bari sai munyi aure just romance kawai " cikin nitsuwa da zaƙaƙuranchi yace " na amince".
Murmurshi yayi mai ɗan ciwo sanja waƙar akayi da waƙar turawa tamkar an muntsunita ta tashi ta fara tiƙar rawa duk ihu suka sa don rabon da Baby Zee tayi a rawa a club na su ya kwana biyu ƴan team nasu ne suka mara mata baya ganin hakan da sauri ya tashi ya sanya hannun sa a cikin aljjihu ya fitar da wani tablet ya jifa a cup juice da bear na kusa dasu ya ɗauka ya haɗa a cup's nin da ɗan basarwa ya isa gun ya kama west na ta ya mana a west nashi ganin hakan ta kwantar da kai a jikin sa volume aka sa sai tafi da aki musu akai akai suka fara taka rawa cup nin ya ɗauko ya bata cikin a zama ta shanye ɗaya hannu tasa ta amshi ɗayan ma ta kafa kai .
Hajiya Hauwa da Hajiya Talatu ko ya zata kaya tsakanin su da mugun aikin su?
Wai me ke faruwa da Lattu ne ne kam na rasa gani matsalar ta fa🤣?
Shin a wanan karon ZALFAT zata ƙubuta daga sharrin maƙiyan ta ko kuma zata kuma afkawa ?
Yau dai ga Zee a club da handsome nata ko ya zata kaya ?
Asha hutun mako lafiya ,ƙorafi ya amso na ƙara muku readmore don nasan mu da posting sai monday in sha Allah...
ALƘALAMIN ƘANWAR SOJA 🖋️💞🌹🤰🤰🤰🤰🤰🤰🤰
MAI CIKI CE
❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️
BY
NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️ 💞
From the writter of
(1) MIJIN MAGE
(2) FARASHIN SO
(3)RUHI BIYU
(4) BIYYAYA GA UWA
(5) DUHU CIKIN HASKE
(6) HANYAR RUWA.
🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, fad'akarwa, ilimantarwa da kuma nishad'antarwa_*
_(R.S.W.A)Ruwa kad'ai ke maganin k'ishi_
*Alk'alaminmu 'yancinmu*
PART 2
PAGE 37 & 38
The comedian sweet love story with full of sympathy.💔🔥😭
PRAY FOR PLASTINE🇧🇴 in our daily du'a may Allah help our sister's and brother's , ya Allah help all the Muslim's in the world🌍 amin.
بسم الله الرحمن الرحيم*
*وصلى الله عل النبي الکريم*
أللهم أ جرني ڢي مصبة و أخرني خيرا منها.
11 \ Nov \ 2023
********************************************
KANO
Zabura tayi taga ƙarfe huɗu na asuba ganin Amrat na barchi ta ɗan tsagaita ta shafa saman gadon "ohh komai na masu kuɗi daban ne irrin wannan gadon zai sa na manta ne MAI CIKI CE ga laushi sai kace bread ganin kamar ta motsa ne tayi shiru ta sauko toilet ta shiga ta kama ƙugu
" Wato idan ba don ina kallon film na masu kuɗi ba ai da na zuba ƙauyauchi a gidan nan tsarki tayi ta ɗauro alwala raka'a huɗu tayi ta zauna sai da ta kammala jiro adu'o inta nagari kyakyawa, ta miƙi zata tashi tonowa tayi ta dawo ta zauna hannu tasa sama
"Ya Allah na manta ka taimaka wa wanan baiwar Allah ZALFAT da ta kasance MAI CIKI CE lallai rayuwar ta tana cikin hatsari kamar yadda nasan labarin ta ya Allah ga kuma miji na naga ƴan mata ko'ina suna ta binsa da kallo Allah ka tsari min shi ya zama doddo a fuskar ƴan mata kai har ma da zawarawa,
Allah kai na ki rogo ga Majhat kasa tazo lafiya tayi kama da ne sanan ta ɗauko irrin lotsowar kumatun ZALFAT inason ta kasance dashi , ya Allah ka " ganin Amrat ta tashi tana kallon ta ne yasa ta