MAI CIKI CE BOOK COMPLETE BY NARNAH ƘANWAR SOJA.txt

Author :  Nana Kanwar Soja Category :  Tknovels

Chapter   14 / 15

39K to 42K   out of 43K words




" Kinga ko ashe masifar Rabi kam na rainin waiyo ne tawa soja mana kuma da alamar matar sace gashi ta tsinka mata mari har biyu Allah ya sama ita kaɗai ke labour da yaga matan mutane ta faɗa cikin raɗa " kedai bare sis da ta zagisa da taga ruwan bala'i yau mai ƙwatan ta sai ya shirya" basuji fitar ta ba sai motsin ƙofar sukagani











"Waiyo Allah Abban Majhat na mutu ka taimaka wa rayuwa ta nagama yawo ka karɓi cikin ka namaka al'kawarin bazan saki kwana da kai ba bare ma nayi ciki kaje ka aure mata ukku kai na baka lasisi huɗu ma kayi yo hauka naki waiyyyyyoooo " da sauri ya ƙanƙame hanunta sai hawaye yana











"Sorry my HABLAT ke daure kinje kifa matar soja ce ko ke daina ihu nan haka" what !!! ta faɗa da ƙarfi hanun ta tasa ta sharara mai mari " nabi matar soja da gudu kai na yaga barrack nin nasa a kundon bola bazan daina ihun ba ka cuci ne ka cuci rayuwata Allah ya isa tsakanin na dakai mugu azzalumi bazan ye shirin ba '"











Inna da ta iso takama baki da sallati "haba mai sunan larabawa adu'a zakiye kinje kin kusa ma suka ce " wallahi Inna yaron ke ya cuci ne daman haka haihuwar take Allah ya isa mun sunan turawa ne wallahi mutuwa zanyi nabi uwata munyi barchi wanan zalunchi ne "








ZALFAT da suka iso leqawa tayi ganin irrin kururuwa da HABLAT taki saida zuciyar ta ta buga ido ta walwallo waje sam doctor baisan ma ta zo hospital nin ba dasu Hajiya Hauwa da Amrat sai Zee suka hau mota suka iso , zufa ce ke malalowa "wai Abban Majhat wanan gadon shine ake cewa gadon azaba duniya duk mace da ta hau to tashiga aljanna ta fito duk zunubanta ma ai za_a kogee ko ?"








" HABLAT haka ne "lahaula lahaula lahaula wane azabbabin ihu ta buga nan doctor Khadijja ta iso da facemask a fuskar ta da wasu nur'ses " sorry fa Madam push ganin Hafeez tayi " oga kayi ha'kuri kujeramu a waje" ko bai mata gardama ba sam ya fitta sai Inna dake gun " doctor ce ko ko aljanna ce ke duba min zan mutu ko don Allah idan na mutu kice ina da ƙanjamau kar yaya Hafeez ya ƙara aure shikkinan wahalar ta ta tafe a banza kinan"











ZALFAT ce ta rigi mararta da bayan ta sai ga wani uban nishi da amai sai nan Zayyan ya ganta" ZALFAT are you fine "innalillahi wa ina iallhin raji'oun doctor zan mutu "!!!! sosai ya tsorata da sauri aka shigar da ita ɗakin HABLAT kusa da gado aka duba ta akace labour ne ta tsinki but bazata jima ha zata haihu duk suka taro a waje harda Abba da akawa waya a Borno cikin hanzarin yabi ta plane ya iso awa ukku ana abu ɗaya HABLAT ce tace akira mata Hafeez.














Yana zuwa tace zata mai magana sirri a kunnen sa kasancewar doctor Khadijja na duba ZALFAT "to HABLAT " yana matsowa takama kunne sa da mugun cizo da kyar ya ƙwace kansa yana fita aka kawo aidbox don bashi agajin gaggawa suka fitta sai ga haihuwa doctor Khadijja ce ta amshi baby a hanunta sai chanchara ihu takiye nan ta baiwa sauran nurse sun gyarah yarinya wane nishi ta kumayi da ƙarfe gaske sai ga wane baby tana haihuwa ta suma








" Twin's HABLAT waiyo don Allah nima na haihu nagaji HABLAT " da sauri aka bata agajin gaggawa aka fidda ta waje har an kimtsa yaron a kaishi ga dangin sa Hafeez ne ya leqasu twins namiji da mace HABLAT ta hafamin faɗuwa a ƙasa yayi sa sujjada yace "Alhamdullah!!!"















Kafin farkawar HABLAT har ZALFAT ta samu haihuwar ɗa namiji sak mahaifinsa doctor Zayyan sai murna sukiye baki ya kasa rufawa nan aka kaita ɗakin hutu inda ta aka kwantar da HABLAT a hankali ta bud'e idon ta tsaff ta sauke a ɗakin ba kowa daga ita sai ZALFAT da wata mata a kwance sai nurse guda biyu dake zaune a kan table na su.











"Sannu Madam kin farka congratulations kin samu twins Allah raya "amin " ta amsa cikin murmurshi da ƙyar ta sauki ƙafafuwan ta har yanzu suna kumbure but yayi sauki sosai" a hankali Madam" a ba komai to Alhamdullah" cewar Inna ga ƙawarki ma kinga ta nan ta haife yaro duk ihunki ne yasa haihuwar ta ya tashi








"Kai Inna ni kuma "ey mana gashi kin wa Hafeez rauni ma a kunne kikam hatsari ne zama daki idan kina naguda " baki ta zum'biro ta suni kai sai yanzu taji kunyar abinda ta aikata " Inna zan fita waje " nurses ina tambaya wai ina wanan murd'e nin mai murɗaɗin jiki Rabi ko wa taki da suna" ido suka haɗa " tana office nan kuzo ku kaine zan mata godiya" suna isowa harda Inna ZALFAT ma ta farka Alhamdullah











"Tana isowa Hafeez na murmurshi duk isowa garita sukayi sai dai ko dariya bata musu ba Alhaji Imam da isowarsa kinan yaga duk a tsaye lafiya kuwa "doctor ina yarana na " kafin nan HABLAT ta chukumu wuyar Rabi ta tsinka mata mari har sau biyu da sauri Hafeez ya bawa Alhaji Imam yaro " HABLAT lafiyar ke "








" Banda lafiya shin wacece ita ke kinsan zafin haihuwa kuwa ya za'ayi ina tsaka da duniya ko lahira zata tsinka min mari a fuska ta jaka ce ne aka gayyamin ke "what nosense cewar doctor Zayyan " tuni zuciyar Hafeez takai bugawa da sauri Abba ya jasa don yasan zuciyar sa ba abinda zai hana ya mata duka doctor Khadijja ce ta fito sai ha'kuri Rabi taki bayarwa amman a banza sai ga wani babban mutum ya fito ana taka masa baya hanya aka bashi a ya kutse da fuska doctor Zayyan yace











" A bata suspension na wata shidda "what cewar Hajiya Khadijja a taki ta cire facemask nata " sir am sorry kuyi mata afuwan sabuwa zuwa ce yalla'bai kuyi ha'kuri tama bawa su Abba haƙuri " duk sunyi shuru juya wa tayi taga ogan su da yazo Zayyan yayi magana dashi "sir please kasa baki hukuncin yayi tsanani tunda ta bada hakuri talakawa su ita ce takijan ragamar ahalin su wata shida tana hutu there is proplem "











A hankali Zayyan ya matso ya rigi hannun ta ido ta zalzalu waje tana kallon sa a hargitsi yace " Umma Khadijja kice ko gizo ce " duk kallon su tayi ɗaya bayan ɗaya Hannu tasa ta ture sa da sauri ta juya ta shiga office nata ta rufe wane sabon kuka ne ya kitto mata lokacin ɗaya ta hargitsa mayafinta harda gashin kanta " na tsani wanan ahalin fiyyeda yanda ( Ajeebah ta tsani AHALIN LASHKHAR , my next book in sha Allah)..













MAI CIKI CE THE LAST PAGE
25 \ Nov \ 2023





















"Yazid kar ka saurari su mu tafe gida kawai kaina na ciwo bana son ganin su mu tafe gida " shikkinan Aunty let's go" sai ɓoya takiye a bayan sa suka fito hannu yasa ya tsayar dasu nan ya miƙa wa Zayyan card suka shiga mota hawaye ta shari " yanzu Abba wanan ita ce mahaifiya ta me yasa taki gudu na " ? fashiwa da kuka tayi nan suka tsagaita suka kama hanyar gida suka chigaba da kula da masu jego.











BAYAN KWANA BIYU





" Duk abinda za'ayi ke tabbatar kinye ki taho Borno gobe domin mu samu mafita a gun sabon boka aikin sa tamkar yankar wu'ka ne ina tabbatar miki cewa duk sai mun rushe su yaza'ayi ace Khadijja ta dawo ga kuma Imam dole fa musan abunyi akan wannan al'amari"








Cikin zaguwa ta amsa da "to" waya sir Yazid yayi da Zayyan a safiyar Lahadi duk suka shirya manyan motocin ne suka ɗauki su har ƙofar wani madaidaiciyar gida nan suka farka" sanyi taki cikin blue atamfa da kalar hoda "Yazid komai na kammala wasu baƙi ne wanan wai "








"Murmurshi yayi kafin ya bata amsa yaji saukowa motoci su " sorry Aunty ki jira kawai ki gansu " duk isowa sukayi cikin farinciki da ganin ta nan taki ta ya mutsa fuska " Yazid abinda zakamin kinan " no aunty am sorry please " kafin tayi magana











ZALFAT ta faɗa jikin ta " Umma nice ƴar ke da kika haifa ki ka barni ina kewar ke Umma ke taimaka ko don ne ki saurari abinda muka zo dashi" ture ta tayi a jikin ta tana kallon ta suma duk tsayawa sukayi kamar gumaka " shafa fuskar ta tayi da kyau" Allahu Akbar rungumi juna sukayi sai lokacin ta fara samun sallama a ranta "kina raye basu kashi kiba " waye zai kashita cewar Abba".











" Am Abba ba kowa" cewar Hajiya Khadijja kallo kallo taki da Alhaji Imam " Alhaji baka mutu ba " ban mutu ba mu zauna sai nabaki labarin komai" nan suka sha ruwa suka labarta labarai su da ya shud'i duk sunje tausayin juna fiyyeda yanda abin yaki " shikkinan idan kun shirya akaiw gagarumin sanarwa da zan muku ranar Friday akaiw ɗaurin aure da za ayi a babban massalaci ga kuma wani ƙarin ma'auratar ko Hajiya Khadijja"?











Da tafin hannu ta rufe fuskar ta Hajiya Hauwa ce ta dube Zee " Alhaji to ya maganar auren Zee da Zayyan kuma ko shine bazatan "da sauri Lattu ta buɗe baki da cewa "ya za'ayi Zayyan ya aure ƙanwar sa bayan uban su ɗaya " duk ido suka bita dashi "karya ne wannan munafuka ya za'yi ya zama yaron Alhaji ke mahaukaciyar ina ne "








Da sauri ta Lattu ta rufe bakin ta kaff ta manta da cewa wai sirri ne "to ai Hajiya Hauwa ranar wanka ba'a ɓoyi chibiya duk daren da ɗewa dole maganar nan ya fito filli " tune ta miƙi zata chukumu wuyar Alhaji da sauri ya ja baya "kul a kul kar ki kuskura hannun ke ya taɓa ne Hauwa a gaban yaran mu ne nan ke rufawa kanki a siri kiye shuru tun kafin wasu sirrukanki ya fita akan kunnen yaran ke "











Shiru tayi da mammaki " wane sirri kenan wai meke faruwa ne " ba komai" cewar Zayyan "Mommy kuyi Hakuri ba wanan ya kawo mu ba "ubanka Zayyan nace ubanka to uban me ya kawo mu munafukai azzalumai ku gayyamin " a kafin ta ƙarasa magana Abba ya sharara mata mari tune HABLAT ta kama hanyar fita perlour ganin hakan duk sukayi waje yaran











"Alhaji ka mari ne agaban yara na" of course zaki rama ne a matsayin na ubansa shiyasa na mari ke bari ma kiji " nan ya kwashi komai ya sanar mata and then bari kije duk abinda kuki ƙullawa nasani sai dai nayi baƙin cikin da ki kayi nasara gun tarwatsa ahalin ɗan uwa na" yana nuna Alhaji Imam " bazan miki komai ba amman inason ki sani abinda bakiso gani shi zaki gani domin Allah baya barchi"











Yana gama faɗar hakan ta ɗau mayafinta sai waje kallo kallo tayi dasu hannun Zee ta kama su fita da sauri ta janye hannun ta don kukan ta da takiye yana damun zuciyar ta " bazan biki ba Mommy bazan saki binki ba zan zauna cikin ahali na tamkar yadda Ajeebah tayi juriyar zama a cikin ( Ahalin LASHKHAR) ba zanyi (BIYAYYA GA UWA ) ba tamkar yadda Sadam yawa Mommy sa biyayya ya aure ƴar maɗigo a rashin sani ba, zan zauna nayi ha'kuri jiran masoyi fiyyeda yanda AFIYYA ( FARASHIN SO) ta zauna jiran Ahmad , a takaice Mommy zan amshi jarabawa ta na rayuwa kamar yanda Khadijatul kubra (Mijin Mage) ta amsa ƙadarar ta, duk da cewa ina cikin tashin hankali da fargaba fiye da Sa'adha ( Ruhi biyu ) taki rayuwar tsoro ba" shin Mommy kin manta kin shagalar dani kin mantar dani nuna soyaya da tausayi kamar na Kamal da Rukayya ( DUHU CIKIN HASKE) irrin son da sukawa juna a matsayin su na ƴan uwa amman basusaniba sai ne da nasan ƴan uwa na kika rabani dasu daga ƙarshe na faɗa (MAKAUNIYAR SO) na rasa mafita tamkar Nadrah ashe soyayyar Yaya da ƙanwa ce " hannun ta riski ta juya da sauri ta faɗa jikin Amrat.








Baki HABLAT ta buɗi "wai ZALFAT kinje bayannai da tayi kuwa a ina tasan wanan labarun nima inason sani "Afra ce tayi murmurshi daki kusa da su " litattafan hausa ne na marubuchiyya Narnah ƙanwar soja dukkan su wasu labbarai ne daki ƙunshi da abubuwan mabanbanta ga kuma faɗarkawa kai kedai zaki samesu a duk kafufin social media" da kyau Afrah dole na cewa Abban Majhat inason ya samu min domin nima kar ayi bani "








"Wai tsayar mi kukayi ko taho mu tafe gida cewar Alhaji Imam"








Ranar Juma'a





Da ya kasance babban rana cikin a halin General yusuf a inda aka ɗaura auren Alhaji Imam da Hajiya Khadijja sai auren da ya ɗauki hankula mutane wato auren General yusuf tare da amaryar sa ANBAR daga ɓangaren guda kuma Doctor Isa da Amaryar sa Lattu( Sa'datu) a inda aka haɗa auren Sir Yazid da Amrat daga ɓangaren guda kuma anyi shagalin suna inda yaran Commender Hafeez aka musu suna da Muhammad Majid tare da Majhat sai yaron Doctor Zayyan inda ya samu sunan Alhaji Abubakar Imam sosai aka haɗa shagali a inda ya zama abin tattaunawa a social media..














" Nashiga ukku Hajiya Hauwa aure fa doctor Isa yayi ina zaman zaman na da miji na sadanin ke gashi nima amin kishiya "a'a dakata Talatu kin manta Lattu tsohuwar mai aikin ki ne , da kanki kika kureta tun lokacin da kika fahimci doctor Isa na mata shishigi ai ba'abin tada hankali bani kina ganin kalar masifar da nashiga ace na zauna da babban maqiye na a gida ɗaya ashe Zayyan yaron Genaral ne anya akaiw wanda ya fini tashin hankali kuwa "








"Don Allah rufe min baki " haka suka fara musayar magana masu zafi zafi hhhhhhhhhh har takaiga faɗa a tsakanin su da sauri ta kwashi jakarta da key " na fita na bar miki gidan ke Hauwa kuma zan dawo ɗaukar fansa" dariya Hajiya Hauwa tayi tana fita taja motar ta da gudu a rashin sani da kaɗuwa da ɓacin rai ta hau flyover ta saki hannun da zatayi hanyar babban mota ta hau kanta da kyar aka fito da gawar ta sai sallati mutane sukiye ganin irrin mutuwar da ya sameta














Bayan kwana bakwai..





Mussaman Abba yasa aka ƙara ƙawata gidan sa na Kano a inda duk suka tari a cikin gidan kowa da part nashi sai babban ɗaki da suka mayar dashi tamkar wane event room a kowacce ranar Saturday da Sunday anan ake haɗuwa komai yana tsari da ɗaku na acikin anan ake haɗuwa a tattauna cikin zaman lafiya suki gudanar da rayuwar su a inda doctor Zayyan ya kamalla gina asibitin sa ya dawo aiki a nan jahar Kano domin inganta ƙasar sa , sai Commender Hafeez wanda Abba yawa ƙarin girma a fillin aiki sanan kuma shima yana ɗaya daga cikin wanan ahalin dashi da Iyayyen sa duka don Abba yace suma sun zama one family,








14 / 15