Kanin Ajali Complete by Zeey Makawa

Author :  Zainab Idris Makawa Category :  Read Hausa Novels

Chapter   32 / 37

93K to 96K   out of 109.3K words

ya ganshi a garin
sai dai ya ki fadin yanayin daya ganshi a can din kawai ya furta Jamil mayaudari ne na kwarai.

Kowa yasa halin da Jamil ke ciki da wata acan sai dai an rasa wanda zai iya fada min gaskiya
a cikin su.
Haka muka tafi da rayuwa ina shan bakar wahala a gidan aure na banda tsayayen da zai
tsaya min tsaye kan alamarin.
Ba komai ne ya jawo min haka ba sai sanin halina da kowa yayi na rashin fahintan da banda
shi da kwanciyan hankali yasa kowa ya fita batuna yanzu.
Don mutum zai iya zuwa mi da magana ba zan bari ya tadhi ba sai na bata mashi rai ina
ganin kowa baiso zamana da Jamil din ne don suna kallo shi a mayaudari.
Ni ko hakan na min haushi a raina sosai don may yan uwa zasu saka min miji a gaba da
hattara da tsangwama shi kadai haka.
Ni dai ko yaya yake tunda bai kini ba ina son abina hakana a wautana hakan shine zaman
lafiyan da zamu dore a tare da yan diyan mu mu kadai.
Ashe abin ba haka yake ba yadda kake so da wuya ka samu hakan a wuri namiji ban taba
kawo wai zai iya kara aure ko hadani da wata ba a rayuwan mu.
Sam bani wanan tunanen a raina ko kadan don gani nake haka zamu tabbata dani dashi sai
yan diyan mu ba zai kara kallon wata mace ba, da sunan aure har kuma harsu haihu ma.
Na mance da abinda sharia ya dorawa maza kan tara iyali rashin shiga mutane ya cutar dani
sanin halin rayuwa na yauda kullun dake gudana ga al,umma yanzu.
Ko gidan mu zan iya share watanni ban lekasu ba duk da kamar a unguwa daya muke zaune
dasu ban damu da kowa ba suma basu damu dani ba tunda sunyi lurar dani ban fahinta ba.
Idan do ta anty ce tu farko da ban auri Jamil ba don ta fada kuma ya tabbata hakan da ta fada
gamay da mazajen namu.
Rashin karfi ga al,amarin namu da bata dashi ne yasa ta saka muna ido kamar yadda kowa ke
kallon mu yanzu kara zube don nakasa da muke dashi bamu daukan kowa a matsayin shi.
Mu dai mazajen mu sune uwa uban mu da muka dogara dasu muke gani zasu tsaya muna ga
komai duk mun ture kowa ga al,amarin mu har kanina Baffa haka baijin maganan kowa daga
iyayyen mu din.
Autan mu karamin mu ya kama dangin anty sosai ya mayar dasu yan uwan shi na jini suma
haka yana zuwa gurin yan uwanta kamar dan ta haifa da cikin ta ya koma.
Baka taba jin zancen shi kudin shi ma yana hannun baffa ko kwandala zai cire sai da yardan
baffa din don tsamay kowa da mukayi cikin al,amarin mu.
Suma din ido suka sa muna tunda sun gane muna zargin su da dukiyan mu da muke ganin
ya ishemu rayuwan duniya ba mai yarda ya rabe mu muce abin mu yake so yaci.
Duk da nasan ba kudin nake da shi ba bai sa na bi yan uwana na jini yadda ya kamata ba ina
ganin duk basu son mu sai diyan su suke so kawai.
Wanan ya kara ja muna bakin jini a cikin dangi ko ance abina ya tashi zakaga ana ja da baya
ba mai kullawa sosai sai yan gidan baba kabir dana zama ma kamar dole su.
Babu yadda zasuyi dani haka yaran su sune masu lekani jefi jefi don sun mafi zuwa wirina
akan yar uwarsu don haka kuma idan sun zo zan saka su aiki ko in aike su suje min ko na
tambaye su kudi su bani idan suna dashi duk da kanana ne sosai kuwa.
Jamil ya dawo inda ya kwatanci biyan kudin yan hayan gidan mu yayi a lokacin ya dawo yasa
su a gaba sai da suka bashi ba tare da sani na ba.
Sai bayan ya karba ne yake fada min sun bashi kudin ya karba nan na nuna mashi kuskuren

taba kudin da yake son yi don ba ni kadai keda kudin ba ya sani.
Nan ya hau fada yana fadin ko bani kadai bane ai nike wahala da gidan da sauran su da dai
naga yaki yarda da maganana na kawo ido na saka mai da kudin yayi yadda yake so dasu.
Ba a sati biyu ba da ya karbi kidin sai ga kira daga wurin kanina Baffa yana tambayana
lokacin biyan kudin yan hayan mu yayi fa.
Nace sun biya sati biyu daya wuce ko yace kudin suna ina nayi shiru ba abinda zance dashi
lokacin don ko banda su a gurina.
Nan ya shiga fada sai abinda ya fito a bakin shi dadai naga fadan yayi yawa ne nake fada
mai gaskiyan wanda ya karbi kudin bani bace.
Nan ya kara hawa yana fada sosai yace ba zasu yarda ba dole in biya wanan kudin idan
kudina sunzo na dauka wasa yake sai daga baya na ga da gaskiya yake maganan shi.
Shiko gogan da ya shigo na fada mai sa tsaki yaja tare da fadin baida hankali shi yasan
wahalan da akeyine kafin su biya kudin da zai fadi hakan.
Bajima ba ya tattara ya koma dama kudin ya kawo shi garin ya karba kuma mai zai zauna yi
kuma duk wanan tafiyan da yake da sunan yana zuwa neman kudi ne yake yin shi .
Muna nan a haka kira yazo min daga wurin baba ban tafi ba na daga yar wayan da kanina dan
wirin anty ya saya min nokia .
Kafin ya saya min wayan sai da nasha kwakwazo kada in sayar da wayan nan don ba zai kara
saya min ba idan na sayar yace.
Shina samu ina amfani dashi don wayan yana min rana sosai yanzu na kira Jamil dashi ina
fada mai baba na nema zan tafi.
Yace lafiya ko nace dashi sai dai idan naje zanji abin da ake nemana dashi din yace sai na
dawo zai kira na kashe wayan.
Na samu baba a gida bai fita ba baya mun gaisa ne yake fada min mutanen nan sun kirashi
zamu shiga sokoto ranan talata sgabiyu ga wata ke nan don haka in shirya tafiya don asuban ci
zamuyi .
Ina hanyan komawa gidana ne jamil din ya kirani yana tambayana idan naje nake fada mai
abinda baba din yace dani a gamay da kiran da yayi min din.
Yace okay kawai ya kashe wayan washe gari sai ganin shi nayi kwatsam ya fado min daki nayi
mamakin ganin shi don bai sanar dani yana tafe ba a lokacin.
Tafiyan dagani sai baba zamuyi shi don haka jamil din ya hau bakin shi da fadin in kula in sa
ido idan muje don in gane abinda ke gudana acan.
Yake fadin tafiyan da ake dani da Baffa yanzu don may za a cire shi idan ba wani manufa a
cikin tafiyan kuma yanzu.
Wanan maganan da Jamil yayi ya sake tunzura sauran yan uwana suka fara kananin magana
kamar yadda Jamil din ke son yaga ya samu kan mu yana juyawa a hannun shi sai yadda yayi
damu.
Abin mamaki sai kuma gashi mun koma hannun Jamil din don muna gama waya dashi washe
gari kwatsam sai gashi ya fado min da safe .
Babu ko kunya don jin zamu samu kudi jamil din ya dawo gari babu shiri nan ya fara kule kule
a tsakanin mu duk da rashin bashi fuska da basuyi sosai kamar farko.
Yanzun dai ya samu yadda yake so haka yasa ya share wuri ya zauna yana jiran tsamani don
baba yace kila da munje ance kudin zai fito ba da dadewa ba insha Allahu.

Jin haka yasa jamil din ya mike kafa yana jiran saukan su don ya kwallafawa kudin rai sosai
saboda halin da muke ciki a lokacin.
Ranan da zamu tafi shida kanahi ya tashi ya dora min ruwan wanka don kada in makara na
shirya ga abin karyawa daya sawo tunda dare ya aje min kamar wata basaraka dani can.
Munyi tafiya lafiya munje hannu muka sa ga wasu takardu da aka gabatar muna inda matar
ta yi min bayanin komai dala dala yadda zan gane komai da akeyi wurin.
Bayan mun gama muka dawo a cikin dare don bamu kwana ba saboda sokoto ne zone din
mu nan muka cika komai na karshe daga takardun mahaifin mu din na komai nasa.
Tun a cikin daren nan da muka dawo ya sani gaba da tambaya nikan ban gane ba yasa nace
mai ina ganin kudin milayan goma sha shiddane zasu fito muna.
Ihu Jamil din yasa yace kin ga shike nan ai mun warke idan wanan kudi ya sauka muna kuma
bamu ba sauran wahala kuma yanzu ai.
Duk yan uwana muna murna da yawan kudin da zai fito muna din kamar yadda nace dasu ga
abinda na gani a can cikin takardun da muka cika din a sokoto.
Yau da gobe muna zaman jiran fitowan kudin kowa ya saka rai yana jiran saukan su a cikin ko
wani lokaci da zamu jisu don an gama komai na fannin kudin da ya kamata ayi ko.
Jin shiru har sati uku ya wuce yasa jamil din ya fara jan tsuki yana bakar magana kan rashin
fitowan kudin akan lokaci ni dai ban tankashi ba iyakata ido dashi kawai.
Ranan sai ga wayan baba da rana tsaka yana kirana ina waje ban sani ba ina aikin girki sai
jamil ne ya dauki wayan a fitsaran ce ya amsa wa baba da fadin ina aiki idan na gama zan zo.
Hakan daya fadi yaba su baba da duk suka hallara suna jirana mamaki hakkuri irin na baba
ya shigo cikin gida yana fada ma matan shi abinda jamil din yace dasu a waya.
Ran anty ya baci sosai don shi baba kabir da hakkurin shi cewa yayi a barshi wani lokaci su
baba musa sai su dawo a raba kudin.
A hasale anty tace ai kudin ba ni kadai ke da hakkin su ba don haka ta tayar da yaro yaje ya
fada min da baki cewa nifa su baba ke jira duk sun hallara ko.
Yaron da yazo yasamay ni ina kwashe abinci yake fada min yadda ran baba ya baci da amsan
da Jamil din ya basu a waya ban tsaya jiran komai ba na fada daki na dauko hijjab dina yana
kwance a dogon kujera falo yace min.
Ina zaki kuma nace kiran dasu baba ke min don ance kowa yana nan yazo ni ake jira in zo ina
fadin hakan na juya na fita tare da kanina daya zo kirana muka tafi.
Tun shiga gidan naga bacin rai a fuskan su na nufi falo bayan mun gama gaisawa dasu ina
shiga baba musa ya tare ni da fadin.
An buga maki waya mijin ki yana fadin wai aiki kike wazai ci kudin naki bayan shi da zai
fadawa mutane maganan banza a waya tunkan a haife shi matan mu suke aiki ai.
Baba kabiru ne yaba baba musa hakkuri yabar maganan don fada yake min sosai kan Jamil
din da bai ganin kowa da mutunci a cikin su yanzu.
Baya baba kabiru yayi bayani sai aka fara gabatar da kudin wanda milayan hudu ne da dubu
dari takwas bayan wanda aka cire dari uku akaba wa yanda sukai muna hidima acan sama.
Ga yadda komai ya koma sai da hanya yanzu idan kana son abinka yazo hannun ka kuma
baba bai yi hakkan ba sai da yardan mu dukan mu.
Nan na fara ajiyan zuciya ina saukewa a fili don ba haka mukai tsamani ba bani kadai bace
har kanina baffa a cikin halin da yake ke nan don bamuyi tsamanin ganin kudin a haka ba.

Muryan baba ne yaci gaba da bayani kan kudin inda yace idan an hada kudin dana farko sun
kama miliyan goma sha daya ke nan cif.
Ya rufe da addua ga iyayyen mu da nasu mahaifiyar aka shafa sai dai har lokacin bamu a
cikin hayacin mu ko kadan.
Sai baba kabir ne ya farga da halin da muke ciki yake tambayan mu ko yaya akayi sai kanina
Baffa ya kalle ni yace kiyi magana mana ke.
Nace ni mai zance yanzu tunda haka aka bamu da sauri baba kabiru ya tambaya yace yaya
akayi ne ko kudin basuyi maku bane?
Baffa yace baba kudin nan fa miliyan goma sha shidda ne zasu zo muna ke ko ba haka kika
gani ba a can kika sa hannu ?
Na gyara zama ina fadin hakana na gani an rubuta da matar ta ban takarda da muka sa
hannu.
Innalillahi baba kabiru ya fara maimaitawa a hankali yana girgiza kanshi tare da dauko wayan
shi yana bugawa lokaci guda cikin tashin hankali.
Baffa kanina yace don may ba zakiyi bayanin abinda kika gani kika sa hannun ba a gaban
kowa kina wani noke noke da kai kuma.
Baba musa ne ya tambaya nawa ke kika saka hannu a ciki a can a takardan nace miliyan
goma sha shidda ne na gani a rubuce na bashi amsa daidai lokacin da aka amsa kiran da baba
kabir yayi ga wayan shi da ban san wanda ya kira a wayan ba lokacin.
Anan kuma yana jin abinda na fada ya furta subbahanallahi hadiza kiji tsoron Allah ki fadi
gaskiya nace.
Wallahi baba shi nagani a rubuce ni ba wani ya fada min ba don har matar da ta bani takardan
nasa hannu ta nuna min nagani.


ZAINAN IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Jamil bai dawo ba sai da ya share wata shidda cif a can ko wanan
dawowan don sallah karama daya gaba to ne yazo.
Yadda ya tafi haka ya dawo min babu kudin gadona babu karuwa daga gare shi ni na tashi ga
tutar babu ke nan yanzu.
Duk cikin abinda yake min wanan sai yafi ci mun rai fiye da sauran don kudin gadon yafi tsaya
min a rai.
Ya dawo yana wani daure min fuska ko magana ya hadamu cikin tsawa zai mun magana da
karfi yana daka min tsawa .
Ganin haka yasa naja baya dashi sai dai ranan kanwata da sukazo gida sallah tazo gidan mu
shine ya fito suna gaisawa da ita.
Har ya jefoni a cikin zancen su harda fita ya sayo masu kayan sanyi na jika makoshi kamar
wani na kirki dashi.
Bai jima ba ya fita ya barmu gidan sai da ya fita take fadin kai mijin nan naki kamar wani na
kirki idan yana wasu halaiya.
Murmushi nayi bance da ita komai ba sai na dauko mata wani zance na daban wanda ya shafi
hiran gidan mu sai muka shagala.

Can lokacin sallah yayi ta mike ta fita don yin alwala ina Allah Allah ta tsaya iya falo kada tace
zata shiga min kuryan dakina.
Sai dai banyi sa,a ba don tana shigowa duk da na shimfida mata abin sallah a falo sai ta shige
kuryan dakina direct don cire unders din ta.
Kira naji ta kwala min daga dakin na dauka na wani abu ne sai na shiga tana cewa dani ina
gadon ki anty ta tsare ni da idanuwan ta.
Kasa amsa mata nayi lokacin take fadin yanzu har gadon kwsncin ku sai da wanan
mayaudaron mijin naki yasa kika sayar wai may kika mayar da kanki for god sake ?
Wallahi ban ganin laifin shi naki nake gani yanzu don kece mai bashi kwarin gwiwan yayi maki
duk wani abinda yake maki..
Haka nazo nake jin wanan kangon da muka saya don gaba mu samu madogara wai ya sayar
da naki ya tafi da kudin .
Tsaye nake daga kofa ina sauraren ta ban san lokacin da na tafi baya ba suuuu zan fadi tayi
saurin rike min hannu daga ciki.
Falo ta fito dani tana fadin wai may ye haka ko dama baki da labarin ya sayar da kangon gidan
da aka sai maki ne tana fadi tana kokarin zama a kusa dani lokacin.
Wasu hawayen da sukaki tsayawa suke zubo min dafa idanuna lokaci guda na kasa controling
din su in mata bayani.
Taci gaba da fadi dama tunda nazo naji wanan zancen hankalina ya tashi gaki da yara mata a
gaban ki yanzu kin san lalurar diya mace da kashin kudi ne komai na ya mace kudine tun tana
yarinya.
Duk bayanin da takeyi ban iya bata amsa ba ko daga kai in kalle

32 / 37