Masarautar jordan Book 2 Complete By Mai Dambu

Author :  Mai Dambu Category :  Read Hausa Novels

Chapter   31 / 37

90K to 93K   out of 109.3K words

Dafe goshina nayi ina jin hudubar su, miko min wani bag.

Buɗe bag d'in tayi sai ga kayan mata, kauda kai nayi nace.
"ajiye su no need domin ban sami uban gayyar ba, bani da ikon tura wani abu a jikina ko shan
wani abu ba."

"Toh ai sai ki tashi a tsaye gurin kwatar kanki."

Haƙa suka yi ta bani shawara, nima dai ba laifi na ɗauka.
Washegari..
Muka tashi da bikin taya murnan dawowar Ashraf, anyi hidima da rana, da dare kuma akayi
dinner wanda nayi dana sanin, zuwana jordan da sanin Ashraf d'in ga baki daya. Dan a daren
ya gabatar da Zoyah da Natashah a matsayin matan shi. Kura mishi ido nayi a hankali na zare
zoben hannuna, lokacin da muka je taya shi murna, rungume shi nayi sannan na kai bakina dai
dai, kunnen shi nace.
"Nagode sosai! Bazan d'aga hankalina ba balle ace kishinka nake, zan Barka da manta amma
ba yanzun ba, ga tsiyarka da kabani shekara hud'u baya."

Lallubar hannunshi nayi nasa saka mishi, sannan na bar inda yake na dawo mazaunina,
muna kallon juna, ido cikin ido.

Tunda ta bar gurin jikin shi yayi matukar sanyi, shi yayi haka ne dan ya rama rashin jin
maganar shi, bawai dan ya wulakanta kimarta ba. Dafashi Natashah tayi cikin jin haushin tace.
"Wacece Zoya?!"
Banza yayi mata idanunshi na kaina, ya rasa abinda zai yi dan wanke kanshi.
Haka taron ya watsa, Inda kabilar banu Hussain, suka tafi da farin cikin aurar da yar su a
matsayin matar sarki, tunda dama ya amshi auren tun baya yanzun ne zai cika alkawarin da ya
dauka.

A daren yaso ganina amma fir naki zuwa da ya dame Ni da kira na ajiye shi a bakin jadawali.
Hankalina kwance.

Washi gari... Su Ummi da yan uwana suka tattara suka barni cikin kad'aici da damuwa,'.

Tunda muka dawo daga raka su, na had'a kan yarana muka shige d'akina, ban kuma fitowa
ba, sai da karfe sha biyu naje na daura mana abincin rana, ina gamawa na juye mana na wanke
komai sannan na koma d'akina.

Duk abinda yarana suke so zan musu a d'akin, da dare ina jin yazo bakin kofata yana bugawa,
Ni kuwa nayi banza dashi.

Dan dole ya hakura, da asuba muka had'u, Ni zan shiga kitchen shi kuma ya fito d'akinshi da
Natashah a bayan shi, tsayawa nayi ya wucce tana zuwa zata wucce na riko hannunta, cikin
harshen English, nace.
"Wannan ne karo na karshe da zan ganki a shashina, idan kika bari nayi ido biyu dake Next
time, wallahi sai na tafasasshen miki fuska da mai me zafi."

Na fad'a a matukar haukace, tsoron yadda na buga mata tsawa yasa ta fashe da kuka, zuwa
yayi ya zare hannunta yayi a cikin nawa.
Ya fitar da ita, kitchen na shiga ina girki raina na kara ɓaci, yana cikin soya dan kwalin turawa
ya shigo kauda kaina nayi, har kitchen ɗin ya shigo. Tare da hard'e hannunshi a kirji shi yayi.
Yana son min magana amma naki bashi fuska, jan kujera yayi ya zauna.

"SAFINAH!!"
Kamar bana kitchen ɗin, na kuma cigaba da aikina.
"Kiyi hakuri don Allah!? Nasan nayi miki kuskure, asalima sabida mu kika fuskanci matsalolin
rayuwa don Allah Kiyi hakuri."

Ina gama had'a komai na na dauki tiren abincina nayi gaba, ba tare da na kalli inda yake
ba.

Ina shiga daki na rufe bammm, dan dole ya hakura da bina, dan na fahimci bina yake son yi.

Wasa wasa, na shiga Gara Ashraf son raina, Natasha kuwa shegiya dama nice na bata fuska,
yarana kuwa kakarsu ta rike su, dan suke dauke mata kewa.

Ablah ta iya zama dan har ta fara rarrafe, bikin shi da Zoyah an saka wata shida masu
zuwa. Sosai nake kame kaina da kimata, a wata jumma'a na kai ziyara gidan Bayi, inda muka
zauna munyi hira yaushe gamo, banga Azrah ba na tambaye su suka ce Basu san inda taje ba.
Tun ranar da Malikah ta turo a kirata ba a kuma ganinta ba. Hankalina yayi mugun tashi, tuni
nasaka aka fara bincika min inda take.

Sannan na rubuta mishi sako da abinda yake faruwa, da kuma cire wasu abubuwan da bai
zama dole bayi mata su yi, na nemi Ghaniyu na bashi ya kai mishi.

Na zuba ido naga amsa sai bai turo ba, dan haka na share batun shi.
A hankali komai ke tafiya. Abinda na tura mishi, sai gashi na Ghaniyu yake gaya min. Irin
abubuwan da sakona ya sauya.

........ Amma a tsakanin mu babu dad'i, dan kamar yadda ya horani haka kuma nake,
mishi kuma bana jin komai a raina, sai dai shi yafini shiga damuwa, dan na hana shi sakat bana
bashi komai sai tsabar miskilancin wanda na koya a hannun shi.

Tsakanin Natasha Nah suma ba zaman lafiya, Ni a yanzun na kyale shi yaje ya dangwala
zandariyar shi a na matanshi tukun kafin ya banbance aya da tsakuwa.

★★★
Bikin da aka saka sai gashi har ya kusa, Kwashe mu yayi zuwa Dubai, dan har lokacin bawai
mun shirya bane, sai dan ya had'a ni da Ummina ta kirani tayi ta bani hakuri, shine nake girki da
shi. Ta gurin kwanciyar aure ne fa, muke rigima dan da karfin bala'i yake samun hakkinshi, a
ranar farko sai da yaji min ciwo, nayi kuka har na godewa Allah, daga ranar ya kuma dasa wutar
rashin jituwar,

Tunda muka isa Dubai Natashah ta fara laulayi, bata ko ina bud'e idanunta. Dole kuka
tattaro muka dawo Jordan, kamar mahaukaciya haka ta koma, dan cikin ba karamin gigita yar
banza yayi ba. Da taji uban wahala rokon Ashraf tayi suje a zubda cikin.

Kota kanta bin takanta bayi ba, ya cigaba da shirin auren shi, Ni tsakanina dashi ido, ya
bini ya bini har ya gaji, idan yazo niman hakkinshi kuwa, rufe idanuna nake nace.
"Kaci wanda ya rage kabar min tunda baiwa ce Ni mara yanci."
Jikinshi ne yake sanyi, dan haka baya abinda ya kawo shi sai ya fita yaje gurin Natashah.
★★★
Bikin shi da Zoyah ya tara mutane, daga makotar ƙasar daga gidan ma sun zo min, kwanansu
biyar suka koma, amarya ta tare a shashinta na kusadamu.

Tunda yazo ranar da aka kawota, shigo min sai da muka yi sati guda bamu saka shi a
ido ba.

Sai ranar na takwas, ya shigo min yana, zuba kamshi. Cigaba nayi da koyar da Yarana, da
gudu suka mike ya bud'e musu hannu suka shiga, rarrafawa Ablah tayi itama ya rungume ta.

Tsotsar baki yake, yana min kallon kasa kasa, dan rigar atamfiffe ce a jikina, doguwa
wacce akayi ta fitter gown, ko ya na motsa sai naji idanunshi.

Mik'ewa nayi na bar falon, ciro chocolat yayi daga aljuhun ya mika musu.

D'akin ya biyo ni, ina tsaye a jikin, jin hannunshi a tsakanin k'uguna, ya janyo Ni jikinshi,
cikin damuwa yace.
"Don Allah ki yafe min! Nayi kuskure sosai kuma a shirye nake na gyara."
Janye jikina nayi daga gare shi, nace.
"Yanzun da ka fahimci mata suna suka tara ko!? Ashraf kenan! Ni kawai ka sallame Ni, tunda
ban isa mace ba kuma ban kai mace ba, Ni ba yar mulki bace, asalima Ni ba yar kowa bace, na
shigo rayuwarka, dan haka kaja tsuman rayuwarka nima na riƙe nawa don Allah ka rabu dani."

Girgiza kai yayi cikin damuwa yace.
"Wallahi bazan iya ba! Kece rayuwata! Wannan silent din da kike min yana cutar da ruhina, don
Allah ki barmu, mu rayu a duniya d'aya. Wallahi na gaji na gama hakura da abinda ya faru, ke
kawai nake buƙata."


Murmushin gefen baki nayi sannan nayi magana kasa kasa, nace.
"Kai da kake da sabuwar budurwa dal kai ka fasata me zakayi da second hand"

Janyo Ni jikinshi yayi cikin nutsuwa yace.
"Kowacce mace da irin halittar amma taki halittar dabance."

"Heyyy! Ashu! Ai haka ne yasa kayi sati guda a cikin gida kamanta da shanyar ka da ka zuba
a rana. Ka dame sabon rami ka manta da wasu tsofin ramuka."

Juyo Ni yayi jikinshi na rawa, Yace.
"Wallahi ba haka bane, bai dace na fita ba barta bane shi yasa na zauna "

"Sabida su a gaban iyayensu ka auro su ko!? Ni kuma a layi ka auro Ni, babu daraja dan ina
sonka na sabawa kowa nawa, Ashraf kaje kawai idan naga yuwar zama da kai, zan nime ka."

Ƙamar wanda aka watsa mishi wuta haka yake cira, riko hannuna yayi na zame tare da
girgizar mishi kai na, nace.
"Please kafita min."

"Don Allah Safinah kiyi hakuri, wallahi bazan kuma ba."
"Wallahi zaka kuma, ai nima haka nayita binka ina baka hakuri kaki saurarona, karshe nima da
na fara,a nan d'akin kayi amfani da karfin ka, kabiya bukatar ka, dake Ni ba yar kowa bace, idan
nayi abu jikinka na rawa zaka kira Ummina ka gaya mata, Ashraf jeka Ni bana son ganin ka
Don Allah idan na hucce zan nime ka......"

Dafe keyarshi yayi cikin tashin hankali, ina gama gaya mishi haka na shige ban daki na
saka kuka, Wallahi ina masifar son Shi. Bana jin zan iya dakatar da kaina dole ya biya kuskuren
shi, sai dai son shi da kewarshi suna damuna, sosai sai da nayi kuka na koshi sannan na fito

abuna, baya d'akin sai dai wani takarda da ya bar min, ɗauka nayi na bud'e.
_Idan na isa dake ki shirya zamu wucce Paris da karfe biyu na rana, Ablah da Yayi ta zasu
zauna a gurin Ammyn na_
Sau shida na karanta sannan na ajiye....
[3/19, 8:35 PM] Mai Dambu: number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda
yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne
150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Masha
Allah*

4️⃣3️⃣
Bai kuma min magana ba nima kuma ban damu nayi mishi ba, har muka iso Paris, motar Hotel
d'in ce tazo ta daukemu.

Disney land Hotel ita ce hotel mafi girma da kudi a kasar, dan haka itace ya kama. Tunda muka
shiga d'akin yake nuna da wani kallo kasa kasa, ban damu ba sai ma shiga ban d'akin da nayi
abuna nayi wanka da alola nazo na fara dibi dubin niman gabar, tashi yayi ya anshi abin sallar
ya shimfida min, sannan ya dawo baya na ya saka hannunshi duk biyu ya dawo dani bakin
gado, sannan ya shiga ban daki yayi alola da wanka, sam Ashraf bashi da kunya, yana zuwa ya
cire towel ɗin ya bud'e jakar shi, ya dauki wani ya ciro basic tees shirt tare da slim jeans, ya
saka, sai turaren sannan ya tawo gabana ya mika min hannunshi, saka hannuna nayi cikin
nashi, sannan ya mikar dani,
          Gaba yayi Ni kuma na tsaya a bayan shi, yajamu sallah. Hmm idan nace Ashraf bai yi ba
nayi karya domin ita kanta karantun sallah, ana bin ka'idar tajuweed. Kowani harafi ana bashi
hakkinshi. Har muka idar ina ina jin sautin karatunsa a kunne na.

   Kwanciya nayi a bakin gadon idanuna a lumshe, ban lokacin da yake maganar a kawo abinci
ba, sai gashi da abincin ya kawo, ya ajiye min, sannan ya tab'a cinyata, buɗe ido nayi na kalle
shi.
"Abinci!"
       "Na koshi!"
           Riko hannuna yayi cikin nutsuwa, yace.
"Wai ya kike so nayi da rayuwata ne?!"

   Juya mishi bayan nayi dan bana son magana. Duk sai ya rasa inda zai saka ranshi yaji dad'i,
Ni kaina nasan ina kewarshi, amma dole na yakince shi a rayuwata, na nesanta kaina dashi.

   Damu na da yayi da magiya ne yasani tashi na zauna tare da jan tiren na fara cin abincin a
yangance, ina ci ina yatsina fuskana. Shi kanshi shagala yayi da kallona,  d'ago kaina nayi
muka had'a ido, tura mishi abincin nayi tare da barin gadon na buɗe jakata na dauki cantainer
da na zubo madara na dauki garin kuka na zuba a cikin dan kofin da suka had'o da abincin, na
zuba sannan na zauna na dama, yana kallona har na shanye sannan na mike zuwa ban daki na

wanke hannu da kofin, sai lokacin yake cin abincin da na bari.

          Share shi nayi na duba cikin kayana, na dauko long sleeve toh na mata, sai cargo pant.
Na saka sannan na koma na kwanta, a hankali barci ya dauke ni, ban farka ba sai wajen tara
shima sabida zazzaɓine ya rufe Ni, na fara rawan sanyin sakamakon ciccikowar da nonona
yayi, yana zogi ga ruwa na zuba. Yana kwance  bai san halin da nake ciki ba. Har wajen karfe
goma, da naji wahala ta ishe Ni nakiraka sunan shi.
"Ashu! Ashuuuuuu! Ashuuuu"

        Kamar a mafarki yaji muryana, da sauri ya hauro gadon.
               Ya d'ago ni fad'awa nayi jikin shi, na fashe da kuka. Dan ki su Aanih sune suka bar
nonon wannan kuwa cireta akayi da karfin tsiya.

           "Menene SAFINAH! "
    "Ashuuuuuu! Nonona suna zogi ga zazzaɓin."

  Cikin sauri ya cire min rigar jikina, sannan ya kalli yadda suka cika tam, kifa kanshi yayi ya fara
tsotsa a hankali, rike kanshi nayi tare da girgizar mishi kai nace.
"Don Allah! Ka bari bana so."

      Kwantar da Ni yayi ya zare min wandon jikina, sannan ya shiga shagalinshi. Sosai yake
tsotsar nonon har ya zuke, sannan ya rungume ni yana sauke ajiyer zuciya, dukda zazzaɓin
jikina sai da naji ya saukar min da kasala, sake lafewa nayi a kirjinshi, hannuna yana kan
nipples dinshi, ina murzawa.
           Matse min ɗuwais yayi, na sauke ajiyer zuciya, shafa bayana yayi sannan ya d'ago
fuskana, kallon cikin idanun juna mukayi take abinda ya faru ya dawo min, ban san lokacin da
na sauka kan shi ba, tare da jan duvet din nayi kwanciyata.

                 Dawowa yayi ya rungume Ni, muka cigaba da barci a hankali, ga zazzaɓin na sauka.
Kara alerm din wayar shi ta farka damu, ina manne a jikin shi. Jan hancina yayi na buɗe
idanuna.
"Lokacin Sallah yayi,"

  Zare jikin nayi na tashi daga gadon na nufin ban daki nayi wanka da alola, ina daura towel sai
gashi ya shigo.

      Fuskana na b'ata sannan na matsa ya shigo, zan fita ya riko ni, yana fad'in.
"Don Allah Ni dai gabar ta isa haka, wallahi shirunki yana hana zuciyata sukuni."

    Banza nayi dashi na kwace hannuna na fito, kafin ya fito har na idar da sallah na,

         Kasancewar mun iso Paris ana sanyi, Twill pants da Paris shirt ya saka, Ni kuma ya duba

min wata trench coat nashi ya bani nasaka da, wata tight jeans, ya bani nasaka bayan na shafa
mai,

    Kwanciya nayi sabida har lokacin zazzaɓi yana damuna, duba jakata yayi ya dauko min turba
da wata bakar gyale ya mika min.
"Ki tashi muje kasa muci abincin sai mu wucce kiga likita."

          A hankali na mike, mika min hand glove yayi sannan ya duba jakar yaga na zo da cover
shoe, ya saka min. Sannan ya mika min hannunshi, hararar shi nayi tare da mik'ewa nayi. Ina
kunkuni,

          "Nagode sosai da zagina da kike yi."
      Hararar shi na kuma yi tare da cewa.
"Ai zaginka bazai wadatar ba,  ina ba rufe ka nayi da duka ba."

               "Allah zaki iya duka na!? Na zata baki da ƙarfin dukana amma tunda zaki iya

31 / 37