Gawa Tafe Book Compelet Zahra Star

Author :  Zahra Royal Star Category :  Read Hausa Novels

Chapter   10 / 13

27K to 30K   out of 39K words

ba.

Wata irin zabura tayi sai gashi ta hankade Zombie d'in da son kai mata cizo.

A hargitse ta mik'e tsaye tana kallonsu Anam cike da tsananin mamaki take nunasu da yatsa, bakinta na rawa take fad'in.

"Kece nake gani ko kuwa kawai gizo ne kike min?".

Wani irin kuka Anam ta saki ganin yadda Farida duk ta firgice ta fice daga hayyacinta, duk ta rame lokaci d'aya hatta kayan jikinta wani wajan ya yage, bakinta a bushe k'amas.

Jikinta na rawa ta k'araso inda Faridar take tana zuwa ta rungumeta da k'arfi kawai suka fashe da kuka a tare.

K'arar sakin Bindiga suka ji ne ya d'an tsorota su, sauke ajiyar zuciya sukai ganin Captain Harun ne ya harbe wannan Zombie d'in da Farida ta hankade shine ya mik'e yana son kawo masu hari.

Captain Harun yana gyara Bindigarsa yana kallonsu Farida da Anam dake nanik'e da juna, yana d'an kallon yanayin yarinyar kamin ya ce.

"Ina kika baro sauran abokan tafiyar taki?".

Sakin Anam tayi, saima yanzu ne itama Anam d'in jin abunda ya ce ya soso mata inda yake mata k'aik'ayi, da kuma take son fara tabbayar ta kenan.

Kuka kad'an ta saki tana kallon Captain Harun wadda lokaci d'aya data kallesa sai da gabanta ya d'an fad'i.

Cikin muryar data gaji da kuka da kuma wahala ta ce.

"Wani tsautsayi ne yasa muka rabu dasu, ko na ce kaddarar sai mun had'u daku ce ta rabo ni daga cikin y'an uwana. Tabbas munga bala'i kala-kala, wadda mun rasa y'an uwanmu da dama a wannan tafiyar da........ Maganar da take son fad'a ce ta katse ganin yadda Anam ke girgiza kanta a mugun zabure ta fara ja da baya tana cewa.

"Dan Allah karki ce min Hanan ta mutu itama, Karki ce min na rasa y'an uwa na gaba d'aya".

Rik'e hannunta Farida tayi tana gunjin kuka ta ce.

"Baki rasa Hanan ba, saboda lokacin da muka rabu dasu Hanan na nan cikin k'oshin lafiya, ban san dai abunda zai faru dasu zuwa gaba ba, amma mun rasa Amal da wasu y'an mata da muka zo dasu".

"Amalllllll"

Anam ta fad'a da k'arfi.

Zuciyarta na bugawa da k'arfin gaske wadda tashin hankalin da take ciki yasa lumfashinta k'ok'arin d'aukewa gaba d'aya, sai k'ok'ari take ta fisgo shi amma yana k'ok'arin d'aukewa.

Tana k'ok'arin zubewa k'asa Doctor Fahat yayi hanzarin tareta kusan shida Captain Harun ne suka je tare tan kar takai k'asa, ganin haka Harun ya sakar masa ita kawai yana d'an matsawa gefe, domin yaga yadda Doctor Fahat d'in ke rawar k'afa a kanta.

Yana kyarma yasa bakinsa cikin nata don sun taimaka mata wajan jawo lumfashin nata ya dawo dai-dai.

Da kyar ya samu ta dawo da lumfashin nata, sai jansa take a hankali zuciyarta na bugawa a hankali yanzu.

Tashi yayi da ita a jikinsa kawai ta fashe da kuka tana kallon Farida itama data gama rud'ewar abunda ya sami Anam d'in a yanzu jin cewa sun rasa Amal.

Captain Abbakar dake gefe yana kallon yadda Captain Harun ya d'auke kai a lokacin da yaga Doctor Fahat yasa bakinsa cikin na Anam. Murmushin mugunta yayi yana jin dad'in abunda ya faru, duk d'aukarsa ko son Anam d'in yake, shifa bai da wani buri yanzu sai na ganin bak'in cikin Harun, ko yaga yana rasa duk wani abu da yake so a rayuwa.

Abbakar tunda ya d'ora idonsa akan Farida yaji tayi masa haka kawai Farida taga mutum sai shishshige mata yake, tana kallonsa yadda ya wani fiddo ruwa daga aljihon wandonsa yana mik'a mata, yana binta da wani irin kallo. Amsar ruwan kawai tayi jikinta dan d'an rawa, da kuma mamakin irin kallon da yake mata, wadda take ganin yayi yawa.

Duk abunda yake Harun na ankare dashi basarwa kawai yayi yana ba banza ajiyarshi........

EPISODE 14

A hankali Al'ameen ya sauke Hanan dake jikinsa baccin wahala ya d'auketa.

Wani waje suka tsinsu kansu ga dare ya tsala.

Baki a bushe Anjali ta ta d'an waiga tana duban wani gida k'arami na katako wadda aka ginasa da itace irin kamar na shak'atawar nan, ta cikinsa zaka iya hangen komai dake wahakana a waje.

Da d'an gajiya a muryarta ta ce.

"Ga wani gidan katako can muje mu sauka ko mun zamu sukunin hutawa, kar wasu Zombies muna zaune ko bacci ya sacemu su kawo mana farmaki bamu sani ba".

Kusan gaba d'ayansu suka mik'e suna nufar cikin gidan katakon dake kallonsu.

Suna bud'e k'ofar kamar jira ake kawai suka ga Zombie mace a gabansu a d'uke tana cin naman wata mata, d'uke take akanta sai yagar namanta take tayi mata kaca-kaca bakinta kuwa yayi jage-jage da jini.

Ita kanta kwayar idonta an cire d'aya kwarin idon nata babu kyan gani yayi wani irin bak'i.

Wani ihu Hanan ta saki tana runtse idonta da k'arfi.

Faruk ne ya d'auki wani table dake tsakiyar parlon gidan ganin ta nufo inda suke tana gunji tana wata irin tafiya a jinkice kai a lauye sai lasar jinin daya b'ata mata baki take.

Kallon fuskarta kad'ai ya isa yasa Kwakwalwar mutum hargitsewa, shi yasa Hanan fasa k'ara tana runtse idonta k'irjinsu sai dukan tara-tara yake.

Gabanta Faruk ya shiga bai tsaya wani Sanya ba wajan d'aga table d'in nan yana sauke mata shi a saman kanta, table d'in ne ya tarwatse akanta gilas d'in table d'in ya fasa mata kai, wani ihu ta saki ta zabe k'asa tana shure-shure, amma bata suma ba bare mutuwa.

Sake d'akko wata kwalba yayi wacce ya gani yashe a k'asa kamar ta giya ya sake kwad'a mata shi a saman kai, sai lokacin ta daina motsi.

Wata wawar ajiyar zuciya Anjali da Hanan suka saki suna kallon gawar Matan gudu biyu.

Faruk da Al'ameen da kyar suna kyama suka kinkimesu suna fitar dasu waje.

K'ofar gidan suka gark'ame suna zubewa akan kujerar parlon.

Hanan dake yashe a k'asa sai sauke lumfashi take bakinta a bushe bata san lokacin data mik'e kamar wacce aka tsikara ta shiga kitchen d'in parlon tana d'akko ruwa ta b'alle marfin robar ruwan ta d'aga ta saka a baki, bata sauketa ba sai da ta shanye ruwan robar nan gaba d'aya.

Dafe cikinta tayi da d'ayan hannunta d'ayan kuma tayi saurin dafe bango dashi, domin wani jiri ne taji yana neman kayar da ita, ga cikinta da yayi wata muguwar k'ullewa sosai.

Suna kallon abunda ke faruwa da Hanan d'in amma ko wannan su da akwai abunda ke damunsa.

Anjali ce ta mik'e da kyar itama cike da gajiya mai tsananin gaske ta kamota ta zaunar da ita cikin parlon.

Da kyar ta lallab'a ta shiga kitchen d'in tana duba abunda zata iya dafa masu domin su d'anci ko yaya ne, domin sun kusan kwana biyu ko uku basu sa wani abu a bakinsu ba, hatta ruwa kuwa.

Wata Taliya ce ta gani cikin leda wacce ba irin tamu ta nan bace, da kyar ta samu ta samu kayan had'i ta dafa a haka dai ba wai dan zatai dad'i ba, domin ko ishashshin magi babu, sai wani magi data gani na ruwa a cikin wata robar magin dashi tayi anfani.

Sai biskit data gani a kitchen d'in da lemoka ta d'akko masu tana ba kowanne daga cikinsu.

Kamar mahaukatan da yinwa tayi ma mummunan kamu haka suke cin abincin da sauri suna tusawa kamar za'a kwace masu shi.

Hanan tana kallon yadda suke cin abincin ba abunda ta tuna, sai lokacin da suke a gida, lokacin da gatansu, har idan ba'ai masu yadda suke so ba su wulakanta mutum wadda yake a k'ark'ashinsu.

Wata muguwar nadama ce ta sake rufeta, kai ba ita kad'ai bama hatta su idan ka kalli yadda suke cin abincin had'e da hawaye dake zubar masu zaka san sun jigata iya jigatuwa, sunyi nadama sunyi laushi ainun.

Hawayen dake mata zuba ne tasa hannu ta share tana tuno Farida, ai bata san lokacin data rushe da kuka ba, tana ture abincin dake a gabanta kwata-kwata ma ji tayi ya fice mata a rai.

Ba wadda ya hanata kukan, suma hawaye suke wadda su sautin kukan ne kawai ba'a ji.

________________________

"Yanzu Farida babu ta yadda za'ai ki iya tuna hanyar zuwa inda su Hanan suke?, ko kuma wata dabara daban".

Cewar Doctor Fahat, yana rik'e da Anam har yanzu da take hawaye.

Farida dake shan ruwan da Captain Abbakar ya bata ta d'an sauke robar ruwan tana satar kallon Captain Harun wadda gaba d'aya idan yana waje haka kawai take tsintar kanta cikin rashin sakewa a waje.

Gashi daya zuba mata idanuwan nan nasa ji take kamar zata nutse a waje.

Kauda idonta tayi daga satar kallon Captain Harun d'in, dashi ko yana kallon kowa daga cikinsu hatta ita d'in da take satar kallon nasa, yana sane kuma yana ankare da ita.

Har saida Abbakar ya d'anyi gyaran murya yana wani d'aure fuska ganin kamar Captain Harun take kallo.

"Tabbayarki ake kina kallon wani waje daban fa".

Fad'ar Captain Abbakar yana wani sake matsowa inda take sosai.

Y'ar ajiyar zuciya ta saki tana duban Doctor Fahat ta ce.

"Bazan iya gane inda suke ba, sai dai akwai wani albishir da zanyi maku, kamin rabuwarmu mun had'u da wani mutum wadda ya ce shine ya d'akko ku a airport kuka rabu dashi a bisa cewa shi bazai biku zuwa wani asibiti da yayi ce maku za'a iya samun mafita a can, to ina da tabbacin suma yanzu zasu iya neman hanyar asibitin domin had'uwa da ku".

"Yes hakan yayi dai-dai gara da Allah yasa kuka had'u da wannan mutunan, to amma shi ina mutunan yake?".

Cewar Doctor Fahat.

K'asa Farida tayi da kanta tana cewa.

"Yana gama gaya mana ya had'u da ku, wani Zombie ya shammacesa ya kashesa, koda muka rabu dasu suna bak'in cikin mutuwar mutanan domin bai gaya masu ta inda zasu fara neman asibitin ba".

Shuru kowa yayi suna jimamin mutuwar wannan bawan Allahn.

Captain Harun ne ya mik'e ganin Abbakar zai k'ara mata wata tabbayar haka kawai yaji yana jin haushin maganar da zai mata ya ce.

"Ya kamata mu bar maganar nan haka, kamata yayi mu fara neman hanyar isa ga asibitin nan da ake ta maganarsa".

Wani mugun haushi ne ya kama Abbakar yana cije baki yabi bayansa da harara ganin yadda ya wani juya ya ci gaba da tafiyarsa, ba yadda ya iya suka bi bayansa ganin yana son b'ace ma ganinsu.

Ganin dare yayi yasa suka yada zango cikin wani babban shago na shopping babban shago ne sosai wadda yake da k'ofofi daban-daban.

Suna shiga kowacce k'ofa Captain Harun ya bada Umarnin su rufo ta gudun faruwar wani abu.

K'ofa ta k'arshe ce wacce Captain Abbakar zai rufe yana tsaye yana kallon kowa da ke rufe k'ofar daya nufa, tashi ce ya saki wani murmushin gefen baki na mugunta yana d'an turota sai yayi kamar ya rufeta yasa sakatar k'ofar, alhalin baisa Sakatar ba, kawai jawota yayi, ya dawo inda suka samu waje suka zauna.

Farin ciki ya sake rufe Abbakar ganin inda Harun yaje ya zauna, yaba k'ofar baya ta yadda ko abun cutarwa ya fara shigowa daga k'ofar shine wadda zai fara cin karo dashi.

Ba wadda yasan muguntar daya k'ulla.

Dare ya tsala sosai baka jin motsin komai sai abunda ba'a rasa ba.

Wasu daga cikinsu bacci ya fara figarsu, Captain Harun ya dad'e bacci bai d'aukesa ba, baida niyar baccin amma da yake bacci b'arawo ne bai san lokacin daya fisgeshi ba.

A dai-dai lokacin da baccin ya fara d'auke Captain Harun a lokacin ne kuma k'ofar da Abbakar ya bari bud'e Zombies guda uku suka shawo kai suka shigo k'ofar, domin suna tab'a ta kawai ta bud'e su kuma suka danno kai cikin shagon.

Abun nasu kamar jira suke suka fara d'ad'd'aga hanci suna mugun jin k'amshin Bil Adam a cikin shagon.

Zan iya cewa k'amshin suka rink'a bi suna nufar inda su Captain Harun suke.

Suna gaf sa hannuwansu jikin Captain Harun wani har ya fara kamo masa rigar wuyansa, kamar an tsikari Farida ta motsa kawai ta bud'e idonta, idon nata bai sauka a ko ina ba sai akan Captain Harun, ganin abunda ke shirin faruwa a mugun zabure ta mik'e had'e da tashin hankali mai tsananin gaske, jikinta na rawa kamar wacce aka jona ma wutar NEPA, ta zabura tana fasa wata gigitacciyar k'ara ganin saura kad'an wani ya kai bakin akan wuyan Captain Harun d'in, k'arar data saki ce ta farkar dasu gaba d'aya.

Wani irin tsalle tayi tana ture Captain Harun ya fad'i k'asa ita kuma Zombies d'in ta shige a tsakaninsu suka rik'e mata hannu suna sun kai mata cizo da tsiya.

A zabure ya mik'e shima yana zaro ido waje yana mamakin ya akai har Zombies suka shigo shagon baccin yasan tabbas yasa an rufo ko wacce k'ofa.

A zabure ya fara lalubar Bindigarsa jikin na rawa, amma wayam babu Bindigarsa babu alamarta.

Cike da k'arin mamaki yake sake lalurbarta, ganin sai b'ata lokaci yake ga Zombies da keta kokowar da tsiya da arzik'i sai sun dannama Farida cizo danma tana da k'arfin hali sai artabu suke.

Captain Joha ne ya kira sunan Captain Harun yana wulla masa tashi Bindigar ya cab'eta, ya fara harbin wani a cikinsu.

Kamin ya sake sakar ma wani harsashi kawai yaga Anam ta kwad'e wani ya sume.

Wani murmushin gefen baki ya sake ya sake sakar ma d'ayan da yayi saura a wajan.

Ta gefen ido yake kallon yanayin da Captain Abbakar ya shiga na tsananin bak'in cikin rashin nasarar da baiyi ba, kuma tuni ya harbo jirginsa, tuni yasan shine yabar k'ofar can a bud'e, tunda yaga shine k'arshen rufe k'ofa, kuma shine yaje rufo k'ofar da Zombies d'in suga gani a bud'e suka shigo, yasan kuma shine ya sace masa Bindiga, domin kamin ma ya gama tunanin nazartarshi Captain Joha ya zaro Bindigar da aka wullar da ita can nesa da inda suke, shima kuma Captain Joha d'in tuni ya gane ba munafikin da yayi hakan sai shi.........

EPISODE 15

Jaho ne ya matsa inda Abbakar yake yana cin kwalar rigarsa cike da takaicinsa yake cewa.

"Ko na rantse babu tantama kaine wadda kabar k'ofar can a bud'e wallahi".

Cike da b'acin rai shima da borin kunya ya yakice hannun Joha daya ci kwalar rigarsa yana wani hak'ik'ancewa da fad'in.

"Kana da tabbacin ni ne zan barta bud'e?, ko kuwa ina sane ne zan barta a haka ne?, nidai nasan na rufe k'ofar bandai san ya akai ta kasance a bud'e ba, dan haka baka shaidar cewa nine na bartan a bud'e".

wani mugun haushinsa Jaho ya sake rufe masa zuciya kamin ya d'an matsa baya kad'an dashi yana fad'in.

"Wallahi Abbakar kaji tsoron Allah, Allah Kaine zaka barta a bud'e, akwai abunda kake shiryawa na sani, idan ba kai bane taya za'ai Captain Harun ya nemi Bindigarsa ya rasa?, ban tashi ganinta ba sai saitin inda ka zauna ka wullar da ita can inda babu wadda zai iya lura da ita, idan ba hankali kasa kana neman nata ba baka tab'a ganin saitin inda ka wullar da ita d'in in.......

Captain Harun ne ya d'aga masu hannu kawaii alamar baya son a ci gaba da zancan.

Idan ka kalli fuskar Abbakar ko alamar nadama babu saima wani ciccika yake yana batsewa, shi kar a k'ara kawo masa raini ko cewa shine yayi.

Suna cikin haka suna sake jin gunji Zombies sun fara shigowa ta k'ofar, dan har yanzu a bud'e take, kwata-kwata sun sha'afa da su sake rufo k'ofar.

Farida ce ta saki k'ara ganin sunja hannun wata Soja mace, dake gefen inda Captain Harun yake tsaye.

Itama matar ihu ta saki Bindigar dake hannun ta fad'i k'asa shi kuma Zombie d'in da yayi nasarar kayar da ita k'asa suka fara kokowa ita dashi, sai k'undun bala suke ita dashi sai so yake ya danna mata cizo ga duk inda yaci nasarar samu a jikinta.

Yadda suke kokowar ne farcensa dake da masifar tsini da kaifi ya karceta a tsintsiyar hannunta, wadda dukkansu basu lura da ya karceta har ita d'in, burinta dai ta kub'uta daga hannunsa kar ya illata ta.

Da wani irin sauri Captain Joha yasa bullet cikin Bindigarsa yana mik'a ma Joha tasa, shima gyara tasa ya d'anyi kamin su uku su fara ba Zombies d'in da suka riga da sun shigo wuta, wadda ya danne Sojar nan mace ya fara sakarma harsashi.

Yana fad'uwa jikinta da saurinta ta mik'e tana wullar dashi daga gefenta.

Jikinta na rawa sosai take shafa jikinta.

Captain Abbakar ne ya fara lura da uwar karcewar da yayi mata nan take ya fara nuna masu.

Ai ko yana nunawa ta kalli wajan ai bata san lokacin data rushe da wani uban ihu had'e da kuka mai k'arfi.

Gaba d'ayansu tausayi ta basu.

Captain Harun nason magana kawai suka ji k'arar Bindiga, d'aga kan da zasuyi gaba d'ayansu kawai suka ga Sojar nan ta d'aga Bindigar dake jikinta ta saita tsakiyar goshinta ta sakarma kanta bullet.

Farida ce ta saki kuka a wajan ta d'uke tana kallon yadda ta kashe kanta hankalinta ya k'ara tashi ainun saita tuno Jasmin itama.

Tana nuna gawar Sojan mace tana fad'in.

"Wai mi yasa suke haka ne?, haka fa Jasmin k'awar Amal ita ma da aka karceta ta kashe kanta, mi yasa why why why dan Allah".

Ta k'are maganar had'e da k'ara fasa wani uban kukan.

Ba wadda ya iya bata amsa sai ma k'ok'arin ficewa suke daga Shagon.

Ganin bata da niyar tashi ta bisu yasa Captain Harun da Abbakar har suna rige-rigen zuwa inda ta d'uke tana kuka kusan a tare suka isa inda take suna mik'a mata hannunsu alamar ta kama ta mik'e.

Wata uwar harara Abbakar yake dank'ara ma Harun, Harun d'in na sane dashi, ya basar yana sake mik'a mata hannun nasa.

Ita dai Farida hannunta kawai ta mik'a bata san hannun waye ta kama ba.

Ashe Hannun Harun ta kama ya mik'ar da ita, ganin yadda jikinta ke rawa tafiyarma bata da kuzarin yinta, yasa Harun saka hannunsa a k'unginta yana d'an duk'awa kad'an sai

10 / 13