AUREN KATIN KASA BOOK 1 PDF HAUSA NOVELS BY PINKY DARLING

Author :  Pinky Darling Category :  Tknovels

Chapter   5 / 16

12K to 15K   out of 46.7K words

sauran duk suka wuce sama, kallonta yayi sannan yace “wayazo jiya wajen ki? har kika fita amota, ina ganin ki simi simi ashe ke munafuka ce ko” raurau tayi da ido, gudun karya mazga mata mari yasa tayi saurin cewa “yaya dan school dinmu ne fa yazo ya kawo min text book din dana ara mashi’’….kallonta yayi yasan sarai karya takeyi s ‘’be careful all of my eyes are on you’’ sannan ya nunfasa yace “go in and call those thrash out here,’’ sanin waenda yake nufi yasa ta mike ta wuce dakin su amra, kodata shiga ta gansu azaune suna yankan kumba babu ko sallama ta kalli amra sannan tace “ki tattara qannenki kuje yaya yana kiranku yana parlor”.. tana kaiwa nan tayi fucewar ta..Jin haka yasa suka mike amra ta zura hijab dinta salima kuwa mayafi kawai ta yafa sannan suka fito atare salim yana biye dasu, koda suka isa cikin parlour zama sukayi akasa sannan suka gaishe sa bayan ya amsa masu sannan yace ‘’ ke amra gobe idan zakuje school haladu sai dunga kaiku ah adaidata sahu keda kannenki sannan zai dunga dauko ku, banason kuna cudanya da kanne na, already na fada ma daddy zaku iya tafi’’ godiya sukayi mashi sannan direct suka wuce daki koda suka shiga daki salima na aje mayafinta gefe tace ‘’kai wannan abu yayi min dadi, ni wallahi sun taimaki rayuwar mu, mteww har wani cewa yake wai baya son muna cudanya da yan uwan sa” dariya amra tayi sannan tace ‘’aina fiki jin dadi salima yanxu kona gama makaranta hankalina zai kwanta sbd yanxu zan samu kwanciyar hankali baza ah dunga dukanku akan latti ba,..dariya duk sukayi sannan sukayi shirin bacci.

Bangaren Ibrahim kuwa yana shiga daki yaga hilma zirr haihuwar uwarta akan gadonshi tana jiran shugowarsa, saida yadan murmusa sannan ya lashe lebensa wanda suke nan baki wuluk cigarette duk ya kodar da fatar leben, karasowa yayi har gaban gadon yazo ya tsaya sannan ya fara tube rigar jikinshi sannan ya sabule wandonsa itakuwa ganin haka yasa ta ware kafafunta don ya samu access direct, ganin haka yasashi hanzari tube sauran sannan ya afka mata ‘’innalillahi wa inna ilaihi rajiun, yaya da kanwarsa Allah ya shirya ko tun yaushe suka fara haka Allah kadai yasani muje zuwa……

Washe gari karfe bakwai daidai haladu yazo da napep dinshi wanda yake haya duk weekend idan habu ya karba aiki, aikuwa abin mamaki yau kusan sune suka fara zuwa school din displine master har mamaki ya dunga yi daya gansu,wunin ranar kuwa cikin farin ciki sukayi don kuwa mama rabi ta zuba masu abinci akula dumamen jiya da yawa haka suka hadu da break suka zauna ah class dinsu amra sukaci sukayi nak abinsu. Karfe biyar daidai haladu yazo ya daukesu sai gida, koda suka dawo dakinsu kawai direct suka wuce.

Saida sukayi wanka suka chanza kayansu sannan suka wuce kitchen domin taimaka wa mama rabi wajen yin dinner, koda suka shigo tana ta faman tuqa tuwo da alamu kwashewa ma zatayi, amra ce ta taimaka mata da kwashe tuwon while salima kuma ta fara juya miyar egusi da ta kammala saida suka gama tsaf suna hira tare da mama sannan suka shiga jera komai ah dining table koda suka gama jerawa, abincin su mama rabi ta basu sannan suka wuce dakin su, akan carpet suka zauna sukaci abinci sukayi nak, amra ta kwashi kwanukan ta wuce kitchen anan ta tarar da mama rabi tana wanke wanke, karba mata amra tayi sannan itakuma ta fara share kitchen din,..banko kofar kitchen din da akayi ne yasa afurgice suka juyo itada mama rabi ganin ya wahab yasa suka hada baki wajen cewa ‘’sannu da zuwa ina wuni’’ bai amsa masu kalli amra yace ‘’ke biyo ni sama inason ganin ki yanxu’’…jin haka yasa amra tsurewa hankalinta atashe duk tunanin ta wani laifin tayi mashi, shikuwa yana fadin haka yasa kai ya fice, binshi abaya tayi hartazo daidai stair case tunawa da bata sanya hijab ba yasa ta wuce daki direct nan ta tarar da su salima sunyi barci, hijab dinta kawai ta saka sannan ta fita, saidata tsaya abakin kofar dakin nasa sannan tayi knocking tare da sallama, jin shuru yasa ta kara knocking ‘’come in’’ jin haka yasa ta murda handle din kofar ta shige ciki, yana nan zaune gefen gadon shi ganinta da hijab yasa yace ‘’ dazu da wannan abin na ganki a kitchen?’’ ganin abinda yake nunawa yasa tace ‘’uhm dama yaya yana nan kusa dani aikin da mukeyi ne yasa na cire”, shuru yayi yana latsa wayan shi…takai kusan tsawon minti goma atsaye tana kallonshi, duk cikin gidan babu wanda yakeda muni kamar wahab, bashi da kyau kwata kwata gashi baki ga wani uban saje daya aje babu ko kyan gani, gashin kwata kwata baya mashi kyau ko kadan, ganin irin kallon da take mashi yasa ya dago ya kalleta sannan yace ‘’you like what you see?” Sunkuyar da kanta tayi sannan tace ‘’sorry yaya’’ kallonta ya sake yi sannan yace ‘’cire hijab dinnan’’ jin haka yasa hankalinta ya tashi dakewa kawai tayi sannan ta soma cirewa, kallonta yayi tundaga sama har kasa ya hadiye mugun yawu sannan yace “ki shiga toilet dina ki wanke shi tass kar inga digon datti ko daya,’’ wucewa tayi sum sum sannan ta fara kiciniyar wanke wa, saida ta dauki kusan minti goma sha biyar sannan ta fito ganinshi kwance yasa tace ‘’na gama’’ baiko kalli inda take ba yana lullube cikin bargo sannan yace ‘’jeki’’ wucewa tayi har bakin kofar sannan ta sanya hannu ta murza handle din kofar, jin yaki buduwa yasa ta juyo da zummar yi mashi magana ta ganshi tsaye bakin gadonshi ya rike kugu tsirara babu komai ajikin sa…a razane ta kwalla uwar kara, da sauri ta juya tana fuskantar kofa jikinta na kyarma, aikuwa ganin haka yasa ya tako har inda take sannan yace ‘’I have one last job for you now kafin na barki ki fita”

jin haka yasa ta fara karanto addu’oin tsari tsinkayo muryarshi tayi yace ‘’give me a blow job now!!!’’ ….runtse ido tayi sai hawaye, babu abinda take tunowa sai baya, wannan ne karo na biyu da hakan ta faru, dukda wanchan lokacin bata da wayo amma Allah ya kubutar da ita kuma allah ya goge mata memory din

abun amma yanxu sai abun ya dawo mata sabo, kuka ta fashe dashi sannan tace ‘’dan girman Allah da yayi ka don darajar Allah ka bude min kofa na fita’’ wata muguwar dariya ya babbake sannan yace ‘’oh I see now you remember,now zo kiyi min abinda nake buqata’’ hankali atashe ta ta fara neman agaji karshe ma dai gadonshi ya koma ya zauna ya wangale qafa yana jiranta, ganin kukan babu abinda zai tsinana mata yasa ta shiga tunanin mafita, wuff ta mi’ke kamar mai aljanu sannan ta babbake da dariya harda tafa hannu, kallonta ya tsaya yi da mamaki, ganin haka yasa ta kara bada himma ta toge dankwalin kanta sannan ta rike kugu ta daidai natsuwar ta sannan ta fara Magana cikin wata murya daban ta zaro idanuwanta waje daman idanun nan kwalkwal sai kyalli sukeyi sannan tace ‘’ Mun rantse da rabbi samawati wallahi wallahi wallahi abdul….wahab idan baka bude mata kofar nan ba zamu kasheka anan wajen, tsayawa yayi yana kallonta babu abinda yake tariyowa sai lokacin da tayi wani irin rashin lapiya na aljanu, idan aka bata mata rai, Ganin ya tsaya yana kallonta babu wani progress yasa ta rarumi wani flower vase daga gefe sannan ta kara zaro ido tace”billahillazi idan ka bari na irga uku saina fasa maka kwakwalwa da wannan,ganin yarinyar nan cutarta ta dawo gadan gadan yasashi neman gajeran wandonshi, da sauri ya dauko keys daga gefen bedside drawer sannan ya wulla mata gabanta yace ‘’dan darajar Allah kuyi hkuri ga makullin nan, yana kaiwa nan ya kwasa aguje ya wuce toilet ya kullo’’, saida taga shigewarshi ta tsugunna ta dauka key din ta bude kofar da sauri, tunawa da flower vase din hannunta yasa tayi saurin bugata aqasa nan take ya fashe, Jan rigar ta tayi sama sannan ta kwasa aguje ta bar dakin saida tazo daidai dakinsu sannan ta tsaya ta fara babbakewa da dariya saida tayi mai isarta sannan ta wuce cikin dakin, wanka tayi ta fito ta sanya kayan baccinta ta kwanta gefen salim, tunanin drama din data shirga adakin ya wahab ne ya fado mata saida tayi dariya mai isarta sannan tace shege ga iskanci ga shegen tsoro da wata yar cilleliyar tsuliyarsa babu kyan gani, kai wallah ya wahab anyi dan iska shine babba amma yafi kowa kan gwangwani insha Allah karshekanka bazai yi kyau ba, rufe idonta tayi barci barawo ya kwasheta.

***Auren Katin Kasa ***

(Unexpectedly falling)

Free page….

Chapter 15-16

Ta bangaren wahab kuwa ya tsorata muraran, sbd ya tuna akwai wani lokaci da lalurarta ta tashi ya kirata dakinsa da niyar lalata da ita lokacin ma ko qirgen dangi bata fara ba aikuwa duk kankantarta tayi mashi dan banzan duka gashi shedanun basu da Imani basaso abata mata rai tunda ga ranar bai kara shiga harkarta ba har ya koma kasar waje, toh yauma gashi an tapka abin kunya…

abinda abdul wahab bai saniba shine, tun lokacin da hakan ta faru tsakaninsu bata kara yin lalurar ba dalili kuwa shine akwai lokacin da kaka larai tazo ganinsu, a lokacin ne ta kawo mata wani magani wanda tunda tayi amfani dashi bata kara rashin lapiyar ba.

Da kyar ya fito daga toilet din yana leqe leqe, saida ya tabbatar bata dakin sannan ya futo ya kulle dakin ya kwanta hankali a tashe.

 

Washe gari kuwa normal ta tashi suka shirya da kannenta da wuri domin yau zasu fara CA test sannan kuma asatin ne zasu fara rehearsal na wani competition da za suyi da Turkish international school wanda shima kafin azabi school dinsu saida akayi yi competitions tsakanin schools din dake jahar gaba daya kuma alhamdlh an zabi school dinsu da wasu makarantu biyu wanda zasu kara da Turkish international school din, kuma duk wanda yaci acikin student din any of the school yana da gagarumar kyauta wadda sai alokacin competition din za ah fada. Amra nada kwazo sosai domin duk class dinsu itace ke zuwa ta biyu, inda zatafi burgeka shine kwakwalwar ta tafi ja wajen karatun addinin musulunci, idon tana karatu bazaka so ta daina ba. Yau test hudu kawai sukayi sannan aka tashe su, koda suka koma gida yau ma kamar kullum babu abinda sukayi suna zaune adakinsu ganin ma zaman bazai yuwu ba yasa suka fito backyard domin yin wankin kayan su,

Zama sukay a bakin fanfo ita da salima, ita ke wankewa salim yana daurayewa, salima kuma tana shanyawa, suna cikin wankin sukaji saukar motorn dady da tasu Ibrahim.

Bayan sun gama wankin suna cikin tattara buckets din da sukayi wankin dashi saiga khady ta biyo ta kitchen, tsayawa tayi tana kallonsu, wani tunani ne ya fado mata ta koma cikin gida sannan ta fito hannunta dauke da undies dinta, tana zuwa dab dasu ta watso masu undies din,

kallonta salima tayi afusace tace ‘’malama meye haka kika watso mana kayanki’’…ko kallonta khady batayi ba ta kalli amra sannan tace “ku wanke min su yanxu, sannan kijama wannan mara kunyar qanwar taki kunne niba sa’ar tsarar ta bace ko kema kinmin kadan ke hatta uwarku ma’’ …jin haka yasa salima daukan ragowar ruwan da suka tsane kayan datti zasu zubar ta watsa ma khady ajiki, a qule ta fara magana ‘’idan zaki zagemu ko zaki ci mutunci mu kiyi amma karki kuskura karki sake kice zaki zagi iyayen mu’’ kallonta kawai khady tayi sannan tace ‘’ayau yau dinnan ba gobe ba saina ci ubanki sannan saina nuna maki cewa ku ba komai bane face yayan riqo’’ aguje khady ta tafi bakin bishiyar tsakiyar backyard din gaban gidan ta buga Ma kanta sau biyu har saida jinni ya tsatso sannan ta wuce ta gabansu tana kecewa da dariya ganin haka yasa hankalin amra yayi matuqar Tashi ta maida kallonta ga salima ta fara Magana ‘’yau mun shiga uku salima kin jawo mana bala’i innalillahi, salima na

fada maki kome zasuyi mana ki daina tankawa amma ke bakyaji yanxu allah kadai yasan mai zataje tace Munyi mata..’’ jikin salima ne yyi sanyi tabbas tayi nadamar biyewa khady, yanxu watan cin ubansu ya kama ganin haka yasa amra kwasar undies din ta fara wankewa saidata wanke tass har an kira sallar ishaï sannan suka dunguma suka shiga ciki basu tadda kowa ba aparlor hakan yadan kwantar masu da hankali, daki suka wuce direct sukayi sallah sannan suka zauna kowannen su ya zabga tagumi, suna nan zaune sukaji saukar motorn daddy dasu iya Ibrahim da wahab, ganin haka yasa hankali amra ya sake tashi.

Suna nan zaune har salim yayi baccin wahala tsabar yunwar da yakeji amma yana tsoran fita ya karba wajen mama rabi ita kuma yau tun bayan sallar magrib ta kwanta sbd wani irin zazzabi daya rufeta.

Hayaniya suka fara jiyowa a parlour hakan yasa hankalinsu ya tashi matuka, tashin hankalin da ba’a sa mashi rana, suna nan zauna aka banko kofar salim agigice ya tashi, ya Ibrahim ne ya shigo idon nan nashi babu kyan gani, fadowa yayi dakin gadan gadan sannan ya damko hijab din salima ay kuwa me zasu yi banda innalillhi, babu abinda amra ke fada sai “dan Allah kuyi hkuri nice na nayi musayar yawu da yaya khady don darajar Allah kuyi hkuri’’ ..baiko saurareta ba yaja salima har tsakiyar parlor inda su dady da mama kareema da khady sai wahab suke atsaye kowannen su fuskarnan babu annuri Sai faman furzar da huci suke kamar sunje yaqi,

khady kuwa tana lafe akan kujera tana nishi kamar wadda keyin naquda, ganin anja salima waje yasa amra kallon salim sannan tace duk abinda zai faru karka sake ka fito kaji salim” amsa mata yayi da toh sannan ta saka kai ta fice.

Karasowa tayi daidai inda aka wanchakalar da salima wanda idonta ya cuko tab ta kwalla kallonsu daddy yayi sannan yace “don ubanki badaru me Khadija tayi maki kika fasa mata kai? ‘’shuru sukayi chan amra tace daddy wallahi bamu fasa mata kai ba itace ta…. Karaf kareema ta tari nunfashinta tace “don ubanku karya zata maku inace taje ta sameku kuna wanki tace ku taimaka ku wanke mata undies dinta shine kuka zagi ubanta kukace bashida Imani sannan kuka buga mata kanta iye?’ jin irin karyar da aka shirya masu yasa salima cewa ‘’mai karya dai dan wuta ne’’ kallonta daddy yayi sannan yace “dan ubanki badarun matsiyaci waye yake maki karya iye, toh kuwa yau zaki gane kuskurenki.. kai ibahim ka kaita storage room karka fito saika tambatar da ka balle hannun mara kunya kafin ka fito’’’jin haka yasa azafafe Ibrahim ya dunga janta kamar dabba har storage room, hankalin amra fa ba karamin tashi yayi ba za’a illata yar uwarta ay kuwa aguje ta bishi kafin ta karasa ma ya rufe kofar storage room din, babu abinda yake sai jibgar salima tun tana rokonshi da Allah ya kyaleta harta sume, saida ya tabbatar ta jigatu sannan ya fito ya rufo kafar yasa key din a aljihun sa, kuka dai amra tayi kuka harta godema Allah, su kuwa kowannen su wucewa part dinshi yayi hankali kwance.

Bangaren salima kuma sumewa tayi dalilin bugun cikinta da ya Ibrahim yayi

tun daga lokacin ta fita hayyacinta. Amra kuwa annan zaune bakin kofar ta zauna zaman dirshen tana kuka tana rokon Allah akan ya tsare mata yar uwarta, gashi storage room din ana dadewa ba ayi amfani dashi ba don babu komai aciki sai karafunan motoci da tsofaffin gas cylinders da aka gama amfani dashida ake ajewa idan sun tsufa. Anan suka kwana har safiya amra bata samu damar koda rufe ido ne ba babu abinda take sai kiran salima amma shuru, tsoronta kada ace kashe mata kanwarta sukayi, karshe dai dakin mama rabi mai aiki ta wuce lokacin tana kan sallaya tana lazimi batasan wainar da ake toyawa ba, ganin amra ta fado dakinta kamar wadda ta susuce idonta yayi rudu rudu tsabar kuka yasa ta mikewa tace ‘’ke amra lapiya meya faru?’’ hankali atashe amra ta labarta mata komai sannan tace mama rabi sun kashe ta sun kashe min yar uwata na shiga uku.

Saida mama rabi ta kwantar mata da hankali sannan tace inada extra key wanda ake barmin sbd ijewar kayan da suka lalace bari na dauko muje mu bude ta, cikin sauri mama rabi ta lalubo key din suka wuce direct dakin, suna budewa kuwa hankali atashe suka ciccibi salima wadda har yanxu bata farfado ba,jikinta duk ya kumbura hawayen fuskarta harya bushe, daki suka wuce da ita anan mama rabi ta dakko ruwa ta yayyafa mata aikuwa tana bude idonta ta fara kuka muryarta adishe ta fara sammabatu “adda wannan wace irin masifa ce maysa baku bari na mutu ba, adda kashemu mutanen nan zasuyi basa son mu innalillahi’’

Rungume ta amra tayi, hawaye sharr afuskarta, dakyarta lallashi kanta sannan daga salima da taimakon mama rabi ta wuce da ita toilet saidata gaggasa ta sannan suka fito daki, kaya ta dauko ta saka mata sannan ta kwantar da ita, kitchen ta wuce ta hado mata tea me dan kauri ta bata saidata tabbatar ya shanye sannan ta dauko pain killer da suke ajewa a locker sannan ta bata. kallon salim tayi wanda ya gama takurewa da alamun da yunwa ya kwanta yasa taji tausayi yan uwanta duk ya rufeta, Har lokacin hawaye bai daina saukowa daga idanun ta ba,saidata taimakawa salima tayi sallah sannan ta kwantar da ita, ta jawo mata bargo. Tashin salim tayi wanda duk ya takure agefe guda tayi domin suyi sallah koda suka idar shima tea din ta hado ta bashi yasha, kwanciya sukayi basu tashi ba sai wajen nine saboda rashin baccin da basu samu sunyi ba, ganin lokacin school ya kure yasa suka fasa kawai daman taso salim shi yaje school din ita kuma ta zauna ta kula da

5 / 16