Author : Ameera Adam Category : Read Hausa Novels
zan fara saidawa. Ki saka mini albarka da bakinki mai albarka."
Ya furta yana miƙa mata kwandon turaren da glass ɗin yari, fara'arta ce ta faɗaɗa. Cikin jin daɗi ta shiga kwarara masa addu'a, sai da ya gama amsawa sannan ya ce.
"Zuba mini abinci."
Hararar wasa ta yi masa ta ce, "Kai da amarya take jiranka, ko ka manta ne?"
Guntun tsaki ya saki, yana jin wani tsantsanin Zuwaira.
"Ni fa na gaji da kara tun da ba ku san zuru ba, na ga alamar idan na yi shiru sai ta gama da kai tukunna."
Suka ji an furta a tsakiyar kansu, a tare suka waiga suka ga Zuwaira riƙe da labule fuska a murtuke.
"Mene ne haka Zuwaira?"
Malam Hasan ya furta, kamar jira take yi ya dire ta ce. "Kwanana na biyo, tun da na ga ana ƙoƙarin cin amana ta. Don ma dai a banza abin yake wai an tsikari kakkausa, tun da ba iya ƙyanƙyashe ƙwan take ba..."
Tass! Malam Hasan ya ɗauke fuskarta da mari, sannan ya nuna ta da yatsa rai a ɓace ya ce.
"Idan ganganci ya sake biyo dake ta cikin ɗakin nan sai na tattaka ki." Da sauri Rakiya ta sha gabansa ta ce.
"Haba Abban Fatihu, me kake yi haka?"
Yana shirin ba ta amsa Zuwaira ta fita da sauri tana sakin kuka tamkar wacca aka ba wa saƙon mutuwa.
"Innalillahi wa inna'ilahir raji'un! Ka ga za ka janyo mini ko? Rakiya ta furta, Malam Hasan ya furzar da iska mai zafi ya ce.
"Kada ki damu don Allah, na sanki sarkin tsoro ce."
"Hasan! Hasan! Za ka fito ne ko kuwa sai an ba ka izinin fitowar?"
Inna ta furta cikin ɗaga murya, kusan lokaci ɗaya Rakiya da Malam Hasan suka dubi juna. Suna nan zaune suka ji an ɗaga labulen ɗakinsu.
"To sake shi baƙar munafika, tun da ba kwananki ba ne sai ki ba shi dama ya yi gaba." Inna ta faɗa tana wurga wa Rakiya harara.
"Ga ni zan fito yanzu."
Malam Hasan ya furta, tun bai gama rufe baki ba Inna ta nuna masa hanya ta ce.
"Fita mu je na ce maka, shashasha bawan mace."
Babu yadda ya iya, haka ya bi bayan Inna jiki a saluɓe, don ba ya son ya sake wata maganar ya ja wa Rakiya wani sabon zagin ko baƙar magana.
Tamkar raƙumi da akala haka ya bi bayan Inna har suka fita tsakar gida, ɗakin Rakiya ta nuna masa ta ce, "Maza ka shiga wurin amaryarka, idan ka ga dama kada ka taɓuka abin arziki. Sakarai kullum kana can wurin da babu ƙaruwa ballantana mamora."
Jiki a sanyaye ya nufi ɗakin Rakiya bakinsa ɗauke da sallama ciki-ciki, yana shiga Rakiya ta yi farat ya tare shi cike da kissa da kisisina. Tsaye Malam Hasan ya yi yana kallon ikon Allah, don rashin kunyarta ba ƙaramin mamaki take ba shi ba. Ya san dama ba za a taɓa haɗa kunyar budurwa da ta bazawara ba, amma kuma ko kaɗan bai fuskanci haka daga wurin mahaifiyar Fatihu ba, domin ita ma a bazawara ya aure ta.
"Barka da zuwa angona."
Zuwaira ta furta tana dafa ƙirjinsa, mamaki ne ya sake mamaye shi da ya ga ta ware kamar ba ita ce ta fita tana zabga ihu daga ɗakin Rakiya ba. Bai amsa mata ba, sai gefen gado da ya zauna yana haɗe fuska. Ganinsa hannuwa suna dukan cinya ya sa ta wurga masa tambaya, kwata-kwata ya manta da sayen wani naman kazar amarci. Don wannan auren ya yi ne kawai da zummar ko Rakiya za ta samu salama a wurin Inna. Abincin da Inna ta girka Zuwaira ta miƙa masa, kamar ba zai karɓa ba sai kuma ya ci loma biyu ya ce ya ƙoshi. Zuwaira da kanta ta dinga jan Malam Hasan cikin kissa da kisisina har mai afkuwa ta afku a tsakaninsu. Don haka koda gari ya waye ko ƙofar ɗaki Zuwaira ƙin fitowa ta yi, wai ba ta jin daɗin jikinta don a dole ta nuna wa Rakiya wani abu ya gifta a tsakaninsu. Da safe koda Malam Hasan ya fito zai shiga ɗakin Rakiya fir Inna ta hana shi, a cewarta ba kwananta ba ne don haka ba ta da haƙƙi a kansa ranar. Yana ji yana gani ya tafi tallan turaren, don kwandon turarensa ma sai Inna ce ta ɗauko masa.
Sannu a hankali zaman Rakiya da Zuwaira ya fara sauya salo duk da dama ba zaman daɗi suke yi ba. Sai Zuwaira ta ɓullo da duk ranar girkin Rakiya tun rana za ta fara kwanciya ta ce ba ta da lafiya, idan yamma ta yi sai ta haye gado ta rufa da bargo. A kan dole idan Malam Hasan ya dawo Inna take tilasta masa kwana a wurin Zuwaira. Saboda wani lokacin cewa take ana tsorata ta, ko ta ce motsi da giftawar mutum take gani. Tun yana ɗaukar abin kamar gaske har ya fara fahimtar makirci ne, damuwarsa ta ninku musamman da yake buƙace da matarsa Rakiya. Don a ƙalla ya kai sati uku ƙwarara bai kwana a ɗakin Rakiya ba, ko da rana bai isa ya shiga ɗakinta ba sai Inna ta fara yi musu masifa. Watarana Inna ta fita unguwa, yana zaune a bakin kasuwa ya ga wucewarta. Farinciki ne ya lulluɓe shi, don haka cikin sauri ya ɗauki kwandon turarensa ya wuce gida. Ya ci sa'a Zuwaira ba ta tsakar gida, don haka ya faɗa ɗakin Rakiya. A kwance ya same ta idanunta suna kan silin, da yake ta yi zurfi a duniyar tunani ko motsinsa ba ta ji ba. Sai da ya kira sunanta sannan ta kalle shi, da sauri ta miƙe tsaye kamar ta ga sabuwar hallita. Malam Hasan ya zuba mata idanu ganin lokaci ɗaya ta zabge duk ta rame, a hankali ya fara takawa wurinta Rakiya ta matsa da sauri ta faɗa jikinsa sai ta ji kuka ya ƙwace mata. Kukan da ta ɗauki kwanaki tana son zubar da hawayensa ba ta samu sukuni ba, tausayinta ya ji har cikin ransa. Ya saka hannu yana bubbuga bayanta, cikin so, ƙauna da tausaya ya ce.
"Ki yi haƙuri farincikina."
Sai da ta share hawayenta ta ce, "Ka fita kada Inna ta dawo."
Bai iya amsa mata ba, sai janyo ta da ya yi ya sake riƙe ta tsam. Tana son ƙwace kanta amma ta kasa, ya sunkuya saitin fuskarta ya furta.
"Na yi kewarki, kullum da tunaninki nake kwana nake tashi. Ban san ya zan ɓullo wa Inna ba."
"Mu cigaba da haƙuri, watarana sai labari."
Rakiya ta furta a sanyaye, don shi kansa ba ƙaramin tausayinsa take ba. Girgiza mata kai ya yi ya ɗago da fuskarta ya ce.
"Ba zan iya ba Rakiya, saboda ina shiga haƙƙinki. Ya zama dole na nemar mana mafita."Ba ta amsa masa ba, ya cigaba da aika mata kalaman soyayya masu kassara jiki, a hankali yake aika mata da saƙon soyayya mai cike da kewarta. Rakiya mace ce da ta san kanta, don haka ta shiga mayar masa da martani. Kowannensu sai da ya nuna wa ɗan'uwansa ya yi matuƙar kewarsa, don yadda ta ga Malam Hasan ya birkice mata sai ka yi tsammanin babu mace a kusa da shi duk tsawon kwanakin da suka ɗauka.
"Ka tashi ka gyara jikinka ka fita lokaci yana tafiya."
Rakiya ta furta masa, ga mamakinta sai ji ta yi hawaye ya gangaro daga idonsa.
"Me ya faru kuma?"
Ta tambaye shi muryarta tana rawa, don ta fahimci dalilin hawayensa.
"Ina sonki matata, ina ƙaunarki farincikina. Idan na fita yanzu ban san lokacin da zan sake jin ɗuminki ba, a cike nake da kewarki zuciyata ina jin kamar kada na matsa daga kusa da ke."
Yadda yake magana ne ya kashe mata jiki, amma gudun kada a samu matsala ya sa ta shiga tausarsa. Suna nan maƙale da juna suka ji sallamar Inna, tamkar waɗanda suka ga mala'ikan ɗaukan rai haka suka firgice lokaci ɗaya kowannensu gabansa ya shiga faɗuwa.
Tun shigowar Inna gidan ta hango takalmin Malam Hasan a ƙofar ɗakin Rakiya, don haka rai a ɓace ta ƙarasa ɗakin cikin masifa ta bankaɗa labulen ɗakin. Ta windon uwar ɗakin ta hango su da yake a gadon Rakiya a saitin windon yake. A kunyace su Rakiya suka ja zanen gado suka rufe jikinsu. Inna ta ja dogon tsaki cikin masifa ta ce.
."Ke dai wannan an yi jarabaiyar yarinya, yanzu don masifa da rana tsaka ma sai da kika yaudaro mini ɗa? Ki bar shi ya tafi nema amma kin kanainaye shi a ɗaki, wato kin samu dama na fita ko? To ka tashi ka fito ka je ka yi wanka ka fita nema, shashasha sai kace ba shi da wata matar don jarabar tsiya."
Inna ta yi furucin da ƙarfi, jin Hasan ya amsa ciki-ciki ya sa ta ce.
"Za ka fito ko sai na fito da kai da kaina?"
A kunyace Malam Hasan ya zura wata doguwar rigarsa ya fito, ya nufi banɗaki yana jin ɗacin ɓacin rai a zuciyatsa.
Ummou Aslam Bint Adam🌚
07062062624
[15/05, 18:55] Ameerah Adam: *GAMMON RAMA*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
Gargaɗi: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ba tare da izina ba.
Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba, idan ya yi daidai da yanayin labarinki/ka arashi ne.
SHAFI NA SHIDA
ABBAN FAUWAZ
Da sauri mutanen da ke ƙofar gidan suka ƙarasa wurinsa suka shiga kiran sunansa, sai dai ganin ba ya numfashi ya sa aka yi gaggawar ɗaukarsa zuwa asibiti. Tun da Tani ta ji abin da ya faru ta saki sabon kuka da kururuwa, da farko abokan Abba cewa suka yi ta bari su je asibiti su ga yadda yanayin jikinsa zai kasance tukunna. Amma ganin yadda Tani ta ɗaga wa mutane hankali ya sa a kan tilas aka bar ta ta tafi asibiti. A lokacin da ta ƙarasa bacci yake yi ana ƙara masa ruwa, tana nan zaune bayan wani lokaci ya buɗe idonsa ya zuba wa fankar da ke wulwulawa ido kamar yana ƙidaya adadin gudun da take yi.
"Sannu Abban Fauwaz!"
Tani ta furta tana matsawa gabansa, a hankali ya dube ta cikin sanyayyar murya ya ce.
"Tani ina cikin tashin hankali."
Lumshe idonta ta yi cikin nuna damuwa ta ce, "Bari na fara kiran likita ya duba jikinka Alhaji. Saboda jininka ya hau, don haka suka ce idan ka farka a sanar da su."
"Tani babu buƙatar kiran likitoci, don lalurar da ta afko mini babu likitan da ya isa magance mini ita."
Abba ya furta da muryar damuwa, riƙo hannunsa Tani ta yi ta ce.
"Komai ya yi tsanani maganinsa Allah."
Abba ya jinjina kai sannan ya ce, "Wannan haka yake, amma abin da nake so ki fahimta. Irin wannan guguwar da ta taso mini, irinta ce wacce ake cewa gobara daga teku maganinta sai Allah."
"Alhaji har yanzu riga kake ɗinka mini babu wuya, ban fahimci inda maganganunka suka sa gaba ba." Tani ta furta masa tana tsare shi da ido. Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce.
"Kuɗin da na ara kwanaki, waɗanda na zuba a kayan da aka tafi da su kwatano da Ghana ne suka halaka."
"Innalillahi wa inna'ilahir raji'un!"
Ta furta a hargitse cike da tashin hankali ta ce, "Ban fahimci sun halaka ba Alhaji?"
Abba ya furzar da iska mai zafi ya ce, "Kayanmu ne aka kama su, sakamakon an samu ƙwayoyin hodar iblis a cikin wasu daga cikinsu, Alhaji Ɗan gaske ya ce mu yi ta addu'a idan ba a nemi masu kayan ba domin hukunta su."
"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel! Alhaji wannan wacce irin jarrabawa ce? Yanzu ya za ka yi da kuɗin wurin Alhaji Dikko?"
Tani ta furta masa, jim ya yi yana nazari sai ya ɗago ya ce. "Wallahi ban sani ba Tani, ban san yadda za mu kwashe da shi ba." Zumbur! Ta ga ya miƙe, cikin sauri ta riƙo shi ta ce.
"Yi a hankali Alhaji, ko a kira likitan ne?" Girgiza mata kai ya yi ya sauka a kan ƙafafuwansa sannan ya ce.
"Gida zan tafi."
Duk yadda Tani ta so hana shi fir ya ƙi amincewa, sai da ya fita harabar asibitin ya ci karo da abokansa waɗanda suka kawo shi asibitin. Bayan an gama biyan kuɗaɗen da aka kashe suka wuce gida.
A washegarin abin da ya faru, sai da ta tabbatar da Abba ya fita, saboda tun a ranar Alhaji Dikko ya fara doka masa waya don ya ji makamar wurin da kuɗinsa za su ɓullo. Saboda ya ji labarin abin da ya faru da Abba a wurin mutane da dama. Abba ya tafi wurinsa ne domin ya ba shi haƙuri, ya kuma nemi alfarmar ya ɗaga masa ƙafa zuwa wani lokacin kaɗan.
Uwar ɗaki Tani ta shiga ta ciro wata lamba a takarda, sai da ta kwafe lambar a wayar sannan ta latsa kiransa. Daga can ɓangaren ta ji an ce, "Kunama mugunyar ƙwaro, ga ki da harbi mai kai mutum ƙasa." Murmushin jin daɗi ta yi, kanta ta ji ya ƙara girma. Cike da isa ta ce, "Kuma ko a yanzu kasuwa ta tashi ɗan koli ya ci gwagwgwaɓar riba." Shi da ita duka suka bushe da dariya. Yadda Tani ta shagala ne ta manta da Fauwaz yana cikin gidan, Fauwaz ya fito zai fita ya ji tana cewa.
"Amma ya aka yi wannan tarkon namu ya kama shi yanzu? Ni fa na ɗauka sai tura ta kai bango. Ka san fa duka kuɗin da ya ranto na saka shi ya zuba a waɗannan kayan da yake shi mahaukaci ne." Daga can ɓangaren ya ce, "Ki ce ya ɓallo wa kansa ruwa. Yanzu kusan nawa ya ranto?"
Shiru Tani ta yi tana nazari sannan ta ce, "A ƙalla za su kai miliyan uku, kuma daɗin da na ji maganin wurin malamin nan da ka karɓo mini bai karye a jikinsa ba."
"Ke fa bala'i ce Tani, amma ki ɗan ɗaga masa ƙafa mana." Mutumin ya furta yana sakin murmushi, ita ma murmushin ta saki ta ce. "Wallahi tallahi ko Alhaji zai yi yawo tsirara ba zan rangwanta masa ba, don tun kafin yarinyar nan ta mutu tuni na yi masa farraƙu da su. Tsakaninsa da su sai tswangama, kuma duk abin da na faɗa ta zauna."
"Sai da ke 'yar kunama."
Ya furta cikin kanbabawa, jin haka ya sa ita ma ta amsa suka kwashe da dariya sai ta ce.
"Lighter ka ƙara riƙe wuta fa, saboda daga wurin Alhaji Dikko kai tsaye tashar jirgin ruwa zai nufa." Amsa mata yi sannan ta ce za ta kira shi gada baya.
Fauwaz da ke jin duk tattaunawar da Tani ta yi, duk sai ya ji tausayin mahaifinsu ya kama shi. Duk wani haushi da ƙullatar da ya yi masa ya saɓe, sai ya sake jin tsoron Tani ya sake mamaye shi. Duk yadda yake fasalta rashin imanin Tani sai ya ga ashe ta doke harsashensa.
'Yanzu ta ina zan fara nusar da Abba wace ce Tani?'
Fauwaz ya raya a ransa, ganin ba shi da tsayayyar mafita ya sa shi barin wurin ya shiga ɗakinsa yana tunanin yadda zai ɓullo wa al'amarin.
Tun daga wannan ranar kwanciyar hankali ta yi ƙaura a wurin Abba, ban da Tani da a zahiri take nuna masa tana cikin damuwa amma a baɗini ta fi kowa farinciki da al'amarin da ya same shi. Sai dai kuma ba ta so al'amarin ya faɗo a daidai wannan gaɓar ba, don tana gudun kada kwaɓarta ta yi ruwa tsululu asirinsu ya tonu.
A ɓangaren Fauwaz ya samu sauƙin tsauwalawarta da ta Abba sosai, saboda kusan kullum mahaifin nasa ba ya zama a gida. Yau yana tashar jirgin ruwa yana fafutukar a saki kayansa, gobe yana ƙofar gidan Alhaji Dikko. Ita kuma Tani ya rasa abin da take ƙullawa kusan kullum da mahaifinsa ya fita take shurar takalminta ta fita.
Ana cikin haka ne wani a cikin tashar jirgin ya ce zai yi masa hanyar da kayansa za su fito, amma sai ya biya kuɗi kusan dubu ɗari biyar. Jin haka ya sa Abba ya kasa zaune ya kasa tsaye, haka ya dinga buga-buga tsakanin abokan kasuwacinsa na goro ya ranto kuɗi dubu ɗari biyar. Tun da Abba ya byar da kuɗin, mutumin yake yi masa yawo da hankali. Yau yace ba ya nan gobe ya ce an tura shi wani gari, daga ƙarshe ma har ya daina ɗaukar wayarsa. Ana cikin haka Alhaji Dikko ya tayar masa da ɓalli, don har hukuma ce ta shiga tsakaninsu. Don haka Tani ta shawarce shi da ya sayar da gonakin da ya saya idan ya so sai ya biya kuɗaɗen da suke kansa.
Kai tsaye lambar Gambo dillali ya nema, amma sai ya ji ta a kashe ba ta shiga. Da yake a buƙace yake da kuɗi kai tsaye 'yan dillalai ya nufa yana nemansa. A nan mutanen wurin suka jaddada masa cewar ya bar garin, sakamakon dama can asali ba ɗan jihar Kano ba ne. Buƙatar da ke tafe da shi ya sanar da su, a nan Shamsu dillali ya shige masa gaba wurin tallata ƙaton gonakin nasa. Ko sati guda ba a rufa ba cikin hukuncin Ubangiji aka yi dace da samun mai saya, bayan da suka je aka duba gonakin suka yi ciniki ya ɗebo takardu ya miƙa masa. Da yake sun ga a buƙace yake da kuɗi bai wani ci riba da gonar ba, don kusan yadda ya saye su haka ya sayar da su. Yana karɓar kuɗin kai tsaye ya kai wa Alhaji Dikko ko gida bai koma ba, ya kuma nemi alfarmar ya ɗaga masa ƙafar sauran zuwa wani lokacin. Sai da suka yi rubutu a gaban wani ɗansanda kowa ya saka hannu sannan Abba ya wuce gida.
Tun bayan fitarsa Tani ta cika fam da farinciki, a lokacin Fauwaz yana ɗebo ruwa yana zubawa a drump. A wani zuwa da ya yi