GAMMON RAMA BOOK COMPELET AMEERA ADAM

Author :  Ameera Adam Category :  Read Hausa Novels

Chapter   4 / 12

9K to 12K   out of 33.6K words

hallaka shi."

Wani irin sabon kuka mai cin zuciya Rakiya ta saki, sai kawai ta fice daga gidan tana jin tamkar zuciyarta za ta tarwatse saboda ɓacin rai. Da wanne za ta ji? Da rashin Fatihu da take jin sa tamkar ɗan da ya ratso ta jikinta ko kuwa da baƙaƙen maganganun ƙazafin da Inna take jifanta da shi? Duk da maganganun Inna ba baƙi ba ne a wurinta, amma na ranar sun fi dukan zuciyarta domin a lokacin ji take yi ko mahaifin Fatihu Malam Hasan ba zai kai ta jin raɗaɗin da take ji na mutuwarsa ba.
Malam Hasan yana ganin Rakiya ta fita ya bi ta sauri yana kiran sunanta, hakan ya sa Inna ta yi saurin ɗagowa ta shiga ƙwala masa kira.

"Hasan! Hasan! Ba za ka rabu da ita ba ka zo ina yi maka magana."
Cike da zuga Zuwaira ta ce, "Ina zai zo zuciyarsa ta tafi Inna, ai wallahi sai kin yi da gaske a kan Yaya don ni wallahi ban taɓa tsammanin abin ya yi tsamari haka ba."
Inna ta zuba hannuwa biyu a kumatu cike da jimami ta ce, "Zuwaira kin ga ya fifita waccan juyar a kan gawar ɗansa ko?"
Zuwaira ta saka hannu ta ɗauki gawar Fatihu ta saka a wani ƙaramin ɗaki da suke ajiya shirge-shirgensu. Inna ta zauna a kan turmi zuciyarta tana ci gaba da tafasa, don a wannan karon ji take yi sai dai Hasan ya zaɓa ko Rakiya ko ita.

Duk yadda Malam Hasan yake sauri sai da ya haɗa da sassarfa sannan ya cim ma Rakiya yana ƙwala mata kira.
"Rakiya! Rakiya don Allah ki tsaya mana."
Cike da ƙunan zuciya da ɓacin rai ta waigo tana faɗin.
"Me zan tsaya na yi Baban Fatihu? Me zan zauna yi a wurin da ba a ƙauna..."
Kukan da take dannewa ya ƙwace mata, wani abu ne ya soke shi a maƙoshi cike da lallashi ya ce.
"Don girman Allah ki yi haƙuri Rakiya, ni da ke duka mun san halin Inna ba baƙo ba ne a wurinmu. Me zai sa ranki ya ɓaci tun da kin san halinta?"

"Me ya sa raina ba zai ɓaci ba ko ni ba ɗan'adam ba ce ba ni da zuciya a ƙirjina? Me ya sa har yanzu Inna ta gagara fahimtar ni ba irin yadda take tsammani ba ce? Me ya sa ba ta iya ɗaga mini ƙafa a wannan gaɓar da zuciyata take cike da ɗacin rashin Fatihu ba. Kasan komai fa Baban Fatihu, ka san dai ba zan iya salwantar da rayuwar ɗanmu Fatihu ba..."
Sai ta sake fashewa da kuka, a sanyaye ya matsa kusa da ita murya a tausashe ya ce.
"Na san komai Rakiya, na san ba a kyauta miki ba. Kuma duk wanda kika ji an ba wa haƙuri an cuce shi ne, na tabbata watarana Inna za ta fahimce ki yadda ya kamata."

"Zuwa yaushe kake tunanin Inna za ta ƙaunace ni? A shekara goma da aurenmu ba ta so ni ba sai daga baya?"
Rakiya ta jefa masa tambayar cike da tausayin sabuwar rayuwar da za ta fara tare da Inna. Malam Hasan ya riƙo hannunta ya ce, "Don Allah ki zo mu je ciki, waɗannan maganganun za mu tattauna daga baya."

Sai da Malam Hasan ya sake rarrasarta da kalamai masu taushi sannan suka koma cikin gidan. Lokacin da suka shiga Inna ta cika fam, suna zuwa gabanta cike da zafin rai ta ce.
"Hasan! Hasan!! Hasan!!!"
Gabansa yana faɗuwa ya ce, "Na'am Inna."

"Sau nawa na kira ka?"

Ya shafa kai a hankali ya ce, "Sau uku Inna."

"To idan ni Kulu, ni na ɗauki cikinka na yi naƙuda na haife ka a yau sai ka saki wannan tsinanniyar yarinyar." Inna ta furta tana kafe shi da ido. Duk da a wannan lokacin ɓacin rai ya sa Rakiya tana son rabuwa da Malam Hasan, kalaman Inna ba ƙaramin tarwatsa nutsuwarta suka yi ba.

"Hasan a yanzu daga Allah sai kai, ku kaɗai kuka zama gatan Rakiya. Don Allah duk rintsi kada ka salwantar da amanarta da na damƙa maka."
Malam Hasan ya tuna kalaman mahaifin Rakiya waɗanda ya yi su yana gab da barin duniya. Nan take ƙwaƙwalwarsa ta sake tarayo masa da kalaman Inna, cikin girmamawa ya ce.
"Don Allah Inna ki yi haƙuri, abin bai kai da haka..."

Tass! Inna ɗauke fuskarsa da mari, ba Rakiya ba hatta Zuwaira sai da abin ya matuƙar ba ta mamaki. Inna ta nuna shi rai a ɓace ta ce.
"Na riga da na gama magana, idan kuma ba za ka sake ta ba. Ka je ka ban yafe haƙƙina da ke kanka na mahaifiya ba."
Cikin firgici Malam Hasan ya ɗago yana kallon Inna, ba ta tanka masa ba ta shige cikin ɗakin rai a ɓace.

Ummou Aslam Bint Adam🌚
07062062624
[12/05, 17:48] Ameerah Adam: *GAMMON RAMA*

©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Gargaɗi: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ba tare da izinina ba.

Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba, idan ya yi daidai da yanayin labarinki/ka arashi ne.

SHAFI NA HUƊU

Da wani irin sanyin jiki Rakiya ta matsa kusa da shi, ta zuba masa ido tana karantar mummunan yanayin tashin hankalin da yake ciki ta ce.
"Koda wasa kada ka yi ja-in-ja da mahaifiyarka. Tabbas ana sake mata, amma duk duniya babu mai maye maka gurbin mahaifiya. Ba tun yau Inna take gwada mini ƙiyayya ba, amma a wannan gaɓar ta zarce kowanne lokaci."
Rakiya ta ja gefen hijabinta ta share hawayenta sannan ta cigaba.
"Ban ga laifin Inna ba, domin kowacce uwa tana son ganin zuri'ar 'ya'yanta. Ni kuma kalar ƙaddara ta kenan ta rashin haihuwa, sai dai ba yin kaina ba ne..."
Kuka mai ƙarfi ya ƙwace mata, Malam Hasan zai yi magana ta katse shi da cewar.

"Baban Fatihu ka bi mahaifiyarka, ni kuma zan tafi duk inda Allah Ya ƙaddara zamana zai ƙare a can."

"Ba za ki tafi ko ina ba Rakiya."

Malam Hasan ya furta cikin hargitsattsiyar murya mai cike da zallar ɓacin rai, sannan ya ɗora da cewar.
"Koda ace ba ki kasance matata ba, haƙƙina ne na kula da ke matuƙar ba kya ƙarƙashin wani."

Za ta sake magana ya riƙe hannunta da ƙarfi suka fita daga gidan, kai tsaye gidan Kawu Sani suka ƙarasa. A lokacin da suka shiga Kawu yana tsaye a bakin ƙofar ɗakinsa yana rufewa, kallo ɗaya za ka yi wa su Malam Hasan ka fahimci kwanciyar hankali ta bijirewa gangar jikinsu.

"A'a, yau Hasanu ne da farar safiya haka?"
Kawu Sani ya furta yana ɗan faɗaɗa fara'arsa. Murmushin yaƙe Malam Hasan ya saki ya ce, "Mune Kawu, barka da safiya."
Kawu Sani ya amsa sannan suka gaisa da Rakiya wacce fuskarta ta yi jajir saboda kuka. Iya matarsa ce ta ƙarasa suka gaisa, tana shirin kai su ɗaki Malam Hasan ya ce.

"Kawu dama ba zama muka zo yi ba, akwai maganar da take tafe da mu."

Kawu Sani ya girgiza kai ya ce, "Hmmm Kulu ce ko?"
Malam Hasan ya gyaɗa kai sannan ya kwashe duk abin da yake faruwa ya sanar da shi. Ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, cikin faɗa-faɗa ya ce.

"Indo wai yaushe Kulu za ta yi hankali ne? Wanne irin rashin hankali take son aikatawa haka? Yara sun rasa ɗansu ko gawarsa ba a binne ba take ƙoƙarin sake saka su a wani tashin hankalin."
Iya da ke gefe ta furzar da iska mai zafi ta ce.
"Wallahi a kullum lamarin Kulu yana sake ba ni mamaki, wai me ya sa wasu iyayen suka fi ƙuntatawa 'ya'yan da suke fi yi musu biyayya? Saboda Allah ina adalci a cikin hukuncin da ta yanke, rayuwa da mutuwa duk a wurin Allah suke, sai kace ba ta san ƙaddara ba."
Kawu Sani ya girgiza kai ya dubi su Malam Hasan ya ce.

"Ku wuce mu je gidan, wallahi idan Kulu ba ta yi wasa ba sai ranta ya yi mummunan ɓaci."
A ɗan sanyaye Malam Hasan ya ce. "Amma Kawu don Allah kada ta..."

"Kada ka damu na san yadda zan ɓullo mata."
Kawu Sani ya katse shi, sannan suka wuce can wurin Inna.

Lokacin da suka ƙarasa gidan a soro suka ci karo da Zuwaira, tana ganin Kawu Sani ta haɗe fuska murya ciki-ciki ta ce.
"Sannu da zuwa Kawu..."

"Wuce ciki mu je baƙar munafuka."

Sum sum sum Zuwaira ta juya ta shige ciki, tun daga tsakar gida Kawu Sani ya fara ƙwala wa Inna kira.
"Kulu! Ke Kulu ko sai na shigo ɗakin?"

Inna ta fito fuskarta a cunkushe ta ce, "Ga ni Yaya."

Kawu Sani ya janyo hannun Malam Hasan ya ce, "Maza zo ki tsine masa, na ce ki zo ki tsine masa sakarai wacce ba ta da hankali. Wato so kike ki sabauta yaron nan ko ki saka masa hawan jini ki tsugunnar da shi ko Kulu?"

Inna ta sake haɗe fuska ta ce, "Yaya kai ne ba ka san abin da ya faru..."

"Idan ba ki yi mini shiru ba sai na ci mutumcinki, wai Kulu yaushe za ki gane Allahn da ya busa miki numfashi, Shi ya dasa miki ƙwan da kika haihu ba tare da sisin kwabo ko wayo da dabararki ba? An ya Kulu kina son ki wanye lafiya kuwa?"
Gabaɗaya shiru suka yi wurin ya yi tsit, Kawu Sani ya nuna Zuwaira da yatsa sannan ya ce.
"Ke kuma daga yau, idan na sake jin kin faɗa wa Rakiya wata magana ke ko kallon banza kika yi mata wallahi tallahi sai na tattaka ki." Ya waiga wurin Inna ya ce.
"Yanzu zan samu mai gari da Malam Liman a suturta yaron nan, zuwa nan da dare za mu zauna mu tattauna."

Kawu Sani ya juya zai fita, har ya je bakin ƙofa ya waigo ya ce. "Idan kun ga dama bayan na fita ku cigaba da rashin mutumcin da kuka saba. Kai Hasan zo mu je." Ajiyar zuciya a fili Malam Hasan ya saki, jiki a sanyaye ya rufa wa Kawu baya suka fita.

Bayan fitar Kawu daga Inna har Zuwaira babu wacce ta yi mata magana, ganin haka ya sa Rakiya ta ɗan samu ƙwarin gwiwar shiga ɗakin da gawar Fatihu take. Tana tsoma ƙafa cikin tsawa Inna ta ce.
"Kada ki sake ko da wasa ki taɓa mini gawar jikana. Idan kin so kuma kin ga dama kina iya haihuwar naki, tun da ke dai kin zama ƙaddara wacce ba ta da zuciya."
Shiru Rakiya ta yi sannan ta fito bakin bishiyar darbejiyar da ke tsakar gidan ta zauna. Tana nan zaune Zuwaira ta fita ta fara sanarwa da maƙota, cikin ƙanƙanin lokaci maƙota da abokan arzikin Inna da suka cika gidan. Sai dai a yadda Rakiya ta lura kowacce mace ta shigo da irin wulaƙantacan kallon da take jifanta da shi. Wanda hakan ne ya alamta mata ruwa ba ya tsami banza, don ta tabbata akwai maganar da Zuwaira ta sanar da su a kanta.

"Don Allah ki dubi yarinyar nan kamar mutuniyar arziki, yanzu wa zai ce za ta iya aikata rashin imanin nan haka."
Rakiya ta ji wata tsohuwa ta furta ƙasa-ƙasa, tana cikin nazarin kalaman tsohuwar ta sake jin wata ta ce.
"Ke kuma Tatu kamar ba ki san karuwancin matan birni ba? Yoo shi ma Hasan ɗin ai an ce ba banza ta bar shi ba."

Wata tsohuwa da ke kusa da Inna, wacce kana ganin yanayinsu za ka fahimci ita ce babbar aminiyar Inna ta karɓe zancen da cewar.
"To Allah na tuba kya ce ita, ai ki ce ubanta tuni ya gama da Hasan. Abin da tun bai san kansa ba ake ba shi a ruwa da abinci yake ci me ya rage kuma? Ai wallahi matuƙar kika cigaba da zama Kulu za ki zaunau ganin idonki."
Inna ta sake yin tsumu abin duniya yana sake damunta, cike da sanyin jiki ta ce.
"Abuwa ya zama dole na ɗauki matakin da ya dace."

"Atoh ke da ɗanki amma wata juyar banza ta fi ki iko da shi ina dalili."
Abuwa ta amsa cike da taƙama tana jifan Rakiya da mugun kallo, don yadda take ɗaga murya da gayya take faɗa don Rakiya ta ji. Suna cikin tattaunawa Malam Hasan da wasu maza biyu suka yi sallama domin ɗaukar gawar Fatihu. Kai tsaye ƙaramin ɗakin da aka suturta shi suka shiga, lokacin da Malam Hasan ya rungumo Fatihu suka haɗa ido da Rakiya. Wani sabon kukan ta fashe da shi, duk yadda ta so tausar zuciyarta sai hakan ya gagara.

"Yaya haka kawai nake jin kamar ba zan rayu da Fatihu ba, don Allah ga amanarsa nan, ki yi masa duk abin da mahaifiya za ta yi wa ɗanta. Domin na yarda da ke, kuma Fatihu ɗanki ne. Zan so ki tuna da wasiyar nan tawa a ranar da Fatihu ya zama magidanci, a ranar da za ki aurar da shi domin wannan ranar ita ce mafi mafarinciki ga kowacce mahaifiya."
Kalaman bankwanan da mahaifiyar Fatihu ta yi mata a baya suka faɗo mata a rai, cikin wata irin murya da ba ta yi zaton kalaman za su fito ba ta ce.
"Shi kenan ba zan ga auren Fatihu ba? Shi kenan yadda na rasa Hafsatu mahaifiyarsa shi ma na rasa shi? Na rasa Fatihu mai ɗebe mini kewa kenan Baban Fatihu?"

"Ban yi zaton Ruƙayyar da na sani mai sanin hukunci da dokokin Ubangiji za ta cigaba da furta waɗannan kalaman ba. Na yi tsammanin ke ce mutum ta farko da za ta lallashe ni a kan babban rashin da muka yi." Malam Hasan ya furta mata haka a lokacin da ya ƙarasa gabanta da gawar a hannunsa.

"Ruƙayya!"

Ya kira sunanta da wata irin muryar mai taushi, wacce take bayyanar da zallar soyayya, kulawa da tausasawa. Ba ta iya amsa masa ba sai ido da ta zuba masa waɗanda suka kaɗa jajir tana hawaye, ya sake kwantar da murya ya cigaba.
"Yana da kyau ki tuna, Ubangijin da Ya ba mu Fatihu yana iya ba mu ninkinsa a lokaci guda..."

"Amma ba da wannan juyar ba."
Furucin Inna ya katse shi, waigowa suka yi lokaci ɗaya suna kallon Inna. Matan gidan da suka shigo gaisuwa duk suka yi carko-carko, don tun lokacin da ya ƙarasa wurin Rakiya suka saki baki da hanci suna bin su da kallo. Wasu su ce ta mallake shi, wasu kuma su ce mahaifinta ne ya mallake mata zuciyarsa, shi ya sa yake mutuwar sonta ya gagara rabuwa da ita.

"Hasan kai muke jira fa."
Kawu Sani ya furta, ganin Inna ta yi tsaye a gabansu ya sa shi cewa.
"Lafiya dai Hasan ko da wani abu?"
Cikin sauri Hasan ya ce, "A'a babu komai mu je Kawu." Daga haka ya wuce suka fita da shi, sai dai har ya kai soro yana jin gunjin kukan da Rakiya take yi mai tsuma zuciya. Inna kuma ta koma ta zauna ƙawayenta suka cigaba da ƙus-ƙus suna zuga ta. Cikin lokaci ƙanƙani aka sallaci Fatihu aka kai shi makwancinsa, da yake rasuwar ƙaramin yaro ce daga mutanan ƙofar gida har matan cikin gidan ba su wani daɗe ba kowa ya watse sai tsirarun ƙawayen Inna da suke shirin ganin ƙwal uwar daka.

BAYAN SALLAR ISHA'I

Kawu Sani, Inna, Malam Hasan da Rakiya ne zaune a ɗakin Inna. Kusan kowannansu fuskarsa a haɗe take babu walwala, Kawu Sani ya dubi Malam Hasan ya ce.
"Idan na fahimce ka Hasan, tun da har zaman can ya gagara za ka dawo nan gidanka wanda ka gada daga wurin mahaifinka?"
Malam Hasan ya gyaɗa kai ya ce, "Kawu a can ɗin ne ba a samun cinikin faskaren sosai, dakon da nake haɗawa da shi yanzu sai a hankali, shi ya sa ma na yanke wannan shawarar ta mu dawo nan gida."

Kawu Sani ya dubi Inna da ta cika fam ya ce, "Kulu kin ji abin da Hasan ya ce ko? Da ma kuma wannan gidan kin san gidansa ne da ya gada a wurin mahaifinsa. Don haka zai dawo tare da iyalinsa, idan na sake na ji wata magana marar daɗi daga gare ki wallahi ranki sai ya yi mummunan ɓaci."
Sai da Inna ta furzar da iska mai zafi sannan ta ɗago ta ce, "Na ji duk abin da ka faɗa Yaya, amma kuma ni ma ina da sharaɗi."
Dam! Ƙirjin Rakiya da na Malam Hasan ya buga kusan lokaci ɗaya, Kawu Sani ya dube ta yana karantar yanayinta ya ce.
"Muna jin ki."

"Ka yi haƙuri Yaya ba rashin kunya zan yi maka ba, amma dai Hasan ɗana ne. Kuma ni da kai ba ma samun kowacce irin matsala sai a sanadiyyar matarsa. Amma ƙiri-ƙiri an shanye..."

"Kulu ba na san ƙananan maganganunki marasa lissafi."
Kawu Sani ya katse ta a ɗan tsawace, wani abu ne ya sake tokare Inna. Ta haɗiyi yawu mai ɗaci ta ce.
"Sharaɗina mai sauƙi ne Yaya, don gaskiya ba zan zuba ido rayuwar Hasan ta ƙare babu 'ya'ya ba. Duk cikin 'yan'uwansa shi kaɗai ne bai samu wani cigaban ku zo mu gani ba, ga Gali nan tare suka yi aure 'yarsa Suwaiba mai shekara goma har samari sun fara tsayar da ita. Don haka na yanke shawarar a wannan karon sai ya auri Zuwaira." Da wani irin firgici Rakiya da Malam Hasan suka ɗago suna kallonta cike da zallar tashin hankali.

GIDANSU FAUWAZ

Jim Abba ya yi yana nazari, cike da gamsuwa da shawararta ya ɗago ya ce.
"Maganarki a kan hanya take Tani, domin a makarantar allo ne kaɗai zai samu tarbiyyar da muke buƙata tun da ya riga da ya raina mu. Amma ban da lalacewa ta yaya yaro kamar Fauwaz da bai wuce shekara goma zuwa sha biyu ba har ya fara bin dare yana yi mana ɗauke-ɗauke."
Tani ta saki ajiyar zuciyar farinciki, amma sai ta ɓoye jin daɗinta

4 / 12