Author : Ameera Adam Category : Read Hausa Novels
[10/05, 07:21] Ameerah Adam: *GAMMON RAMA*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
Gargaɗi: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ba tare da izinina ba.
Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba, idan ya yi daidai da yanayin labarinki/ka arashi ne.
SHAFI NA ƊAYA
Tun da yamma ta yi, zuciyar Malam Hasan ta dare gida huɗu kwatankwacin kusurwar bangon Gabas, Yamma, Kudu da Arewa. Sakamakon kaɗuwa da mummunan tashin hankalin da ya baƙunci rayuwarsa da ta iyalinsa. Tafe yake jiki a saɓule tamkar kazar da aka jefa da wuƙa, haka ya ƙarasa kan layin gidansa hannuwa biyu suna dukan cinya. Hadari ne yake haɗuwa a garin, sassanyar iskar damuna mai saka annushuwa tana kaɗawa da ratsa jiki. Sai dai a ɓangaren Malam Hasan ba haka abin yake ba, domin wuyan rigarsa zuwa ƙirji, da gefen hammatarsa sun yi sharkaf da gumi. Har ya dafa langa-langar da ke tokare da ƙofar gidan nasa, sai kuma ya tsaya jim! Yana ƙura wa raunanniyar katangar gidan idanu tamkar yana son tantance kalar ƙasa da taɓon da aka gine dangar da su.
"Allah Ka kawo mini mafita, Allah Ka fi ni sanin halin da nake ciki Ka hore mini kada na tozarta ba don ni ba; ba kuma don halina ba."
Ya furta da wata irin raunanniyar murya, a hankali ya ɗaga ƙafarsa da ke sanye cikin matattun takalmansa da sun gama suɗewa ta ƙasa. Ya shiga cikin gidan bakinsa ɗauke da sallama, Rakiya ya hango zaune tana ba wa Fatihu abinci. Sai da ya ƙarasa gaban kwanon ya lura kwaɗon ƙanzo ne ta yi masa, wanda yake fari fat. Ba tare da ya samu sirkin ƙuli, magi da mai ba. Gishiri ne kawai Rakiya ta barbaɗa masa don ya ji daɗin ci a cikin bakinsa.
"Sannu da zuwa Mai gida, Allah Ya sa dai an dace."
Rakiya ta furta cike da damuwa, ajiyar zuciya Malam Hasan ya sauke yana sunkuyar da kai ƙasa ya ce.
"Rakiya lamarin nan sai godiyar Allah, amma sisi da kika sani babu wacce na samu rance. Kowa na tambaya da irin uzurin da zai kawo mini, daga ƙarshe ma sai na lura wasu kuɗin ne ba za su ba ni ba."
"Innalillahi wa inna'ilahir raji'un, Ya Allah ka kawo mana ɗauki."
Rakiya ta furta a sanyaye, zama Malam Hasan ya yi ya ce. "Amin Ya Rabbi."
"Yanzu Malam ya za mu yi? Ka san fa Alhaji Bashari ba ya saɓa alƙawari, ba kuma ya ɗaga ƙafa. Wallahi tun da ya ce a yau sai mun bar masa gidansa, babu makawa sai ya zo ya ci mana mutumci."
Rakiya ta sake maganar cikin damuwa, hannu ya zura a koɗaɗɗan aljihun da ke jikin koɗaɗɗiyar shaddarsa. Ya ciro garin kwaki da bai fi gwangwani biyu ba, sannan ya miƙa mata wani ɗan ƙullun suga ya ce.
"Ga wannan jiƙa mana mu sha, kafin mu ga abin da Allah zai yi da mu."
"To malam ko za ka kira shi a waya?"
Shiru Malam Hasan ya yi da jin furucinta, sai ya zaro wasu 'yan canji a aljihunsa na gaba ya ce.
"Wannan canjin da kika gani, wayar tawa na sayar wai ko Allah zai sa na samu rancan kuɗii na haɗa masa da su. Duka gabaɗaya ɗari takwas da hamsin na sayar da ita, tun da ta tsufa ta kwana biyu. Shi ne na sayo mana gari da suga, na ba wa Malam Idi biyan bashin da yake bi na. Yanzu kuɗin hannuna ko ɗari huɗu ba su kai ba, idan ya zo ya ji magiya da roƙon da zan yi masa shi kenan. Idan kuma bai haƙura ba, sai mu bar masa gidan."
Yana gama magana aka fara kiran sallar Magriba, miƙewa ya yi ya ɗauro alwala sannan ya fita masallaci. Fatihu mai kimanin shekarae biyu ya miƙe ya dafa ta cikin gwarancinsa ya ce, "Umma a kala."
Kwanon kwaɗon ƙanzon ta karɓa, ta tsiyayi garin kaɗan ta jiƙa masa sannan ta sake barbaɗa masa gishiri ta miƙa masa. Nan take ya hau ci, yana yi mata murmushi. Miƙewa ta yi ita ma ta jiƙa shi a kofi, ta yafici sugan ta zuba sannan ta fara sha a gaggauce saboda yunwa. Domin rabonta da abinci tun ɗumamen tuwon dawar da ta ci da safe.
Sai da ta kammala shan garin sannan ta ɗauki buta domin ta ɗaura alwala, a daidai wannan lokacin Malam Hasan ya shiga bayan ya dawo daga masallaci. Ganinsa ya sa ta ajiye butar, ta ɗauki dogon kofin sulbarsa na shan ruwa ta juye masa ragowar garin kwakin da ya yi saura ta jiƙa masa. Karɓa ya yi ya fara cusa wa cikinsa, duk da ba wani daɗinsa yake ji ba duba da tarin damuwar da ta cunkushe kwanyarsa. Alwala Rakiya ta ɗaura sannan ta gabatar da sallar Magriba, sallamar da za ta yi daga sallah ta yi daidai da sallamar da aka fara rangaɗawa a tsakar gidan. Kuma kusan a daidai gaɓar hadarin da ke haɗuwa ya shiga bayar da walƙiya haɗe da yayyafi sama-sama. Hakan ya sa ta yi saurin fita ta ɗauki zanen goyo ta goya Fatihu, sannan ta koma daga ƙofar ɗakinta tana kallon abin da yake shirin faruwa.
"Malam Hasan ya ake ciki?"
Alhaji Bashari ya furta a ɗage, yana bin sa da wulaƙataccan kallo. A sanyaye Malam Hasan ya dire kofin garin da ko rabi bai sha ba ya ce, "Sannu da zuwa Alhaji..."
"Riƙe sannunka, wannan ba shi ne abin da ya kawo ni ba, waɗannan kalaman idan na shiga gidana har gajiya nake da su. Ina maganarmu ta kwana? Da kuɗin ko babu?"
Alhaji Bashari ya watsa masa tambayar yana ƙure shi da ido, cike da karaya da sarewa Malam Hasan ya ce.
"Don girman Allah Alhaji ka yi haƙuri..."
"Kai Zage, Ƙaribu da Goje ku shigo don Allah ba na son ɓata lokaci ruwa ya fara saukowa."
Alhaji Bashari ya furta yana ɗaga murya, tun bai rufe baki ba matasan da ke ɗauke da siffar masu zuƙe-zuƙe suka shiga cikin gidan suna wuri-wuri da idanu.
"Allah Ya taimaki mai gida, a sa kai ne?"
Wanda aka kira da Zage ya furta yana cije gefen bakinsa, cikin isa Alhaji Bashari ya ce.
"Ku fito masa da duk wani abu na cikin gidan nan ku dire a ƙofar gida. Ku gaggauta saboda kun ga yayyafi ya fara sauka, ba na son ya taɓa ni don mura yake saka ni."
"An gama master, kai Ƙaribu sa ta sama."
Goje ya furta da muryar maye yana surar tabarma da kwandon wanke-wanken da ke gefen ɗakin Rakiya.
"Don Allah Alhaji ka rufa mana asiri kamar yadda Allah Ya rufa maka, don Allah ka ba ni iya yau kaɗai wallahi gobe gari yana wayewa za mu bar maka gidanka." Malam Hasan ya furta yana dafa ƙafarsa, da sauri Alhaji Bashari ya janye ƙafarsa kamar wanda kashi ya sauka a kanta. Cike da tsantsani ya ce, "Kada ka sake taɓa ni da wannan hannun naka Malam Hasan, ina fatan ka gane. Wallahi a yau babu abin da zai hana ni rufe gidan nan, zancan banza ma kenan. Mutane idan kuka samu gidan mutum kamar gadon iyayenku, dubi duk yadda kuka lalata mini gida. Ji gefen katangar nan yadda ta zube, kalli ƙofar banɗaki ita ma rawa take za ta faɗi. Ai wallahi ɗan baƙara na sake ba wa matsiyaci gida babu gaira babu dalili. Kai Ƙarubu, ku yi ku fito da kayan ɗakin mana."
Alhaji Bashari ya furta cikin kumfar baki yana baza babbar rigarsa, a sanyaye Malam Hasan ya tashi. Don tun da yake a rayuwa kusan ba a taɓa gasa masa maganganun da suka ci zarafinsa kamar wannan ba. Ba tun ranar ya san Alhaji Bashari mutum ne mai wulaƙanci ba, amma bai taɓa tsammanin wulaƙancinsa ya kai haka ba.
Rakiya da ke gefe goye da Fatihu ban da hawaye babu abin da take gogewa, suna nan tsaye carko-carko su Zage suka ciro yaƙunanniyar katifarta suka fita da ita. Cikin ƙanƙanin lokaci suka fitar da komai na gidan, da yake dama ɗakin Rakiya ba wani kayan kirki ne da shi ba, saboda ba wasu kayan ɗaki gare ta ba. Daga katifa, tabarmu, Ghana Must go ta kayan sawarsu, labule, kwandon wanke-wanke da kujera 'yar tsugunno. Sheƙeƙe Alhaji Bashari ya dubi Malam Hasan ya ce, "Malam Hasan za ku iya fita, tun da a yanzu dai ni da kai babu kare bin damo. Kuma ba mu haɗa iri ba ballantana ka ce kana da gado a kaina."
Malam Hasan da baƙincikin duniya ya mamaye shi ya dubu Rakiya ya ce, "Rakiya mu je, In Shaa Allah, ina da yaƙinin Allah ba zai tozarta mu ba."
Kamar Rakiya tana jira sai kuwa ta fashe da kuka ta ce, "Abin da ka yi mana Allah Ya yi maka kai ma, In Shaa Allahu yadda ka wulaƙanta mu sai Allah Ya tozarta ka."
"Dama ai tsiyar matsiyaci kenan, duk rufin asirin da na yi muku na ba ku mahalli kuke zaman haya ba ki gani. Ban da irinmu masu tausayi, waye zai ɗauki gida ya ba wa faƙirai faƙara'u alal lalurati gidan haya."Alhaji Bashari ya furta wa Rakiya.
"Kada na sake jin bakinki Rakiya."
Malam Hasan ya furta mata, harara ta wurga wa Alhaji Bashari sannan suka fita daga gidan. Malam Hasan yana fita Alhaji Bashari ya sa su Goje suka rufo ɗakunan guda biyu. Sannan suka fito waje ya datse ƙofar gidan da mukulli, a daidai wannan lokacin yayyafin da ake yi ya fara ƙarfi. A ɗan ruɗe murya tana rawa Rakiya ta ce.
"Malam ina za mu saka kayan nan?"
Damuwa ɗauke a fuskarsa ya ce, "Bari na ƙwanƙwasa gidan Malam Ado ko ya dawo."
Tun ba ta yi magana ba Malam Hasan ya matsa gidan ya fara bugawa, ya ɗan jima a haka sannan aka buɗe masa. Ganin Malam Hasan ya sa shi ɗan tsuke ta ce.
"Malam Hasan ne?"
Malam Hasan ya gyaɗa kai ya ce, "Eh ni ne, Dama Wani taimako na zo ka yi mini."
"Wallahi sisi ba ni da ita a yanzu Malam Hasan."
Malam Ado ya furta yana zura hannuwa a aljihu yana kaɗawa, wani abu ne ya soki zuciyar Malam Hasan. A ransa ya raya wato shi duk wanda ya gan shi ya san neman rancan kuɗi ya zo kenan.
"Ka san fa sha'anin damina dama sai godiyar Allah. Komai maleji ake yi da shi, ga kuma hidimar iyali."
Kalaman Malam Ado suka dawo da shi hayyacinsa, ajiyar zuciya ya sauke ya ce.
"Dama ba rancan kuɗi ba ne, kayana ne zan ajiye su idan babu damuwa zuwa nan da gobe ko jibi In Shaa Allah."
Zuro kai Malam Ado ya yi yana bin kayan da kallo, sai ya ce.
"To idan dai ba za su wuce jibin ba ai babu damuwa, ka san ni ma jibin nake son zubin kajin sallah."
Malam Hasan ya saki murmushin yaƙe, don ba shi da mafita da ta wuce hakan ya ce. "In Shaa Allahu zuwa jibin ma zan kwashe su, na gode sosai." Amsa masa ya yi sannan ya wuce ya fara kwaso kayan kaɗan-kaɗan, har ya kwashe su gabaɗaya ya shiga da su wani ƙaramin ɗakin gidan Malam Ado. A gaggauce ya fito bayan ya gama kwashe kayan, ya ƙarasa wurin Rakiya ya ce.
"Mu je."
Murya na rawa ta ce, "Ina za mu je Malam?"
Malam Hasan ya ce, "Gidan abokina Sale."
Rakiya ba ta amsa ba, saboda a duk lokacin da ta buɗe ba ki hawaye ne yake shatata daga idanunta. Da ƙafa suke tafiya kasancewar suna da nisa sosai tsakaninsu da titi, sai da suka yi kusan rabin tafiyar ruwa kamar da baƙin ƙwarya ya tsuge, hakan ya sa Rakiya ta zare ɗankwalin kanta ta sake rufawa a saman hijabinta don Fatihu ya samu sauƙin dukan ruwan.
02/04/2000
Unguwar Na'ibawa, Kano.
Alhaji Lawan mai goro zaune yake a ɗaya daga cikin kujerun da ke zagaye a falon, ƙatuwar television da DVD da ke kange a saman dubaidar ƙarfen ke fitar da amon hoton india mai motso na Mother India. Zaman saman kujerar ne ya gundure shi, don haka ya sauka ƙasa musamman da ya kasance lissafin kuɗi yake yi masu yawan gaske. Wayar gidan ce ta fara ƙara da ke kange a jikin bango, sai da ya ajiye kuɗin hannunsa sannan ya ɗauka.
"Salamu Alaikum, Gambo dillali."
Daga can ɓangaren aka amsa masa, "Wa alaikassalam, Alhaji Lawan na ji ka shiru fa, wai ko ka fasa ne mu sallama wa wani?"
Cikin sauri Alhaji Lawan ya ce, "Haba Alhaji Gambo, ka san ba za a yi haka ba, yanzu haka jimillar kuɗi sun kammala. Irgasu nake yi sai na ƙaraso na kawo maka, amma ina fatan za a ba ni takardu da komai a yau?"
Gambo dillali ya ce, "Takardu tun yaushe suke hannuna Alhaji, yanzu nan da yaushe za mu jira ka? Don mai gidan ɗazu ma sai da ya kira ni."
"Nan da awa ɗaya In Shaa Allahu."
Alhaji Lawan ya ba shi amsa sannan suka yi sallama, yana ajiye wayar Hajiya Tani ta shiga falon, zama ta yi a gefe ta zuba wa kuɗin idanu sai ta ce.
"Alhaji kuɗi sun kammala kenan, ai muna nan da kai watarana sai ka ce na faɗa maka waɗannan da za ka saya sai ya fi wanda ka sayar daraja? Ka ga idan ka samu yadda kake so, har shaguna nan gaba sai ka fitar. Sayen ƙasa ai babu faɗuwa sai riba."
Alhaji Lawan da yake cigaba da irga kuɗin gabansa ya ce, "Tani ta inda kike birge ni wallahi kina da dogon nazari da tunani, duk matar da za ta ba ka shawarar cigabanka ai ita ce matar zama. Wannan gonakin fa sai a yi gida da manyan shaguna biyar a ƙofar gida, kuma unguwar ba ƙaramar daraja gare ta ba. Karkarasa kuwa ai ba za ki haɗa ta da sashenmu ba, kuma duka gonakin duk girman filotai ukun miliyan ɗaya fa, don haka na sayar da gonata na haɗa don na saya watarana sai ki ji wani zancan ake ba wannan ba." Hajiya Tani ta jinjina kai ta ce, "Haka ne kam, Allah Ya sa albarka.
Alhaji Lawan ya amsa da Amin, sannan ya cigaba da irga ragowar kuɗaɗen gabansa. Sai da ya kammala irga kuɗin tas, sannan ya zuba a wata ƙatuwar baƙar jakarsa. Ya dubi Hajiya Tani ya ce, "Ni zan ƙarasa 'yan dillalan, tun ɗazu na yi waya da Alhaji Nasiru shi ne wakilina. Na san ba shi da ɓata lokaci ƙila yana can." Hajiya Tani ta numfasa ta ce, "To shi kenan Alhaji, Allah Ya taimaka. Sai ka dawo." Jakar ya ɗauka ya fita gareji, ya saka a cikin mota. Sannan Fauwaz ɗansa mai shekara goma ya buɗe masa ƙofar ya fita da mota.
Hausawa sabon titin 'yan dillalai da ke titin masallacin Murtala, unguwa ce da ke ɗaya daga cikin fitattun unguwanni da ke cikin ƙwaryar Kano. 'Yan dillalai, wani keɓantacce wuri ne da ke kan sabon titin. Wanda mafi yawa dillalai ne da ke hada-hada a wurin, wasunsu suna da wata sana'ar bayan ta dillanci. Yayin da wasu kuma suke zaune ba sa cas ko as, sai wannan dillancin kawai suka dogara da shi. Da yawansu ba samari ba ne, masu iyali ne wasu ma dattijai ne waɗanda suka ga jiya da yau a harkar dillanci.
Gambo dillali ɗaya ne daga cikin manyan dillalan da ke rayuwa a wannan wurin, kusan su biyar suka yi haɗakar kama shagon da suke zama. Sai dai mafi yawa sun fi zama a bakin shagon, saboda bishiyoyin darbejiya da ke rufe da wurin don haka ƙofar shagon ta fi cikin shagon sanyi. Harabar 'yan dillalai tana da girma babu laifi, domin a kan gudanar da kasuwamci kala-kala. Akwai masu sayar da abinci, masu fura, kanikawa, shagon teloli, masu gashin balangu, masu gyaran inji da mashina da dai sauransu. Amma rinjayar da dillalai suka yi ya sa ake kiran wurin da 'yan dillalai.
Daga masu zama a kan tabarmin harabar, wasu daga ciki ba su da aiki sai caca da bushe-bushen sigari, yayin da wasu daga ciki ko ƙamshinta ba sa son ji. Iya abin da ya kawo su shi suka saka a gaba, daga cikin dillalan da ke hada-hada akwai na gari masu yi domin Allah. Akwai kuma waɗanda suke cuta, ko su yi kaka-gida a kan fili, gona, kamfani, ko gida idan har ba a ba su abin da suka yanka na la'adarsu ba.
Lokacin da Alhaji Lawan ya ƙarasa 'yan dillalai a can ya tarar da amininsa Alhaji Nasiru, ba su ɗauki lokaci mai tsayi ba suka shiga motar Alhaji Lawan suka ɗunguma zuwa unguwar Karkasara. Kasancewar a lokacin unguwar ba ta cika ba, ya sa take shiru sai ɗaiɗaikun manyan gidajen masu hannu da ƙunbar susa. Wasu katafaren gonaki ne, wanda yake farkon layin. Daga gabansa da bayansa fili ne fetal, an yi masa alama da an riga an saya ba na sayarwa ba ne. Gambo dillali shi ya sake dinga nuna masa gonakin, yana sake kwaɗaita masa darajar unguwar. Har yake fasalta masa zai iya gidan bene sama da ƙasa, mai ɗauke da kusan ɗakuna goma, har a samu babban garejin da zai iya ɗaukar mota biyu, Alhaji Lawan sai murmushi yake yi cike da annushuwa da farincikin a wannan ranar zai mallaki manyan gonaki kamar waɗannan. Suna tsaka da duddubawa, Alhaji Wali shi da wasu mutane biyu suka ƙaraso, sai da suka gaggaisa sannan Gambo dillali ya gabatar da shi.
"Alhaji Lawan wannan shi ne Alhaji Wali, mamallakin waɗannan gonakin, a tare da shi akwai shaidun masu sayarwa." A karo na biyu Alhaji Lawan suka sake gaisawa, sannan ya fito da jakar kuɗi ya miƙa musu. Suka zauna suka fara lissafi tiryan-tiryan har suka kammala kuɗi ya cika cif, miliyan ɗaya. Takardun gonakin aka miƙa wa Alhaji Lawan ya saka hannu, Alhaji Nasiru shi ma ya yi sa hannu a wurin shaidar mai saya. Sai Alhaji Wali ya saka hannu