UWAR AGOLA COMPLETE HAUSA NOVELS BY MAMAN AFRAH.txt

Author :  Maman Afrah Category :  Tknovels

Chapter   11 / 15

30K to 33K   out of 44.2K words

da yamma, yadda zan gigitawa Hadiza tunani, don na ji hatta ƴarta Zainabar wannan da ba sona take ba tana cewa wai babanta ya fini iya wanka da gayu, gwara na nuna musu nima Kuluwa ce ta mini tsiya shi ya sa suka ganni da tsohon kaya!"



MAMAN AFRAH
09025576222
[4/15, 3:33 PM] MOM MASHKR & AFRAH: *UWAR AGOLA*


NA

MAMAN AFRAH

*Daga marubuciyar*
*Ruwa cikin cokali, ci ma zaune, malamin bogi, ƙazamin miji, Bonono ƴar zaman wanka, ruɓaɓɓiyar igiya ƴan adaidaita sahu, ƙara,in inna delu, jalli joga, Beelal, ungozoma da sauransu.*
09025576222


🅿️9️⃣


Tun da Malam Nura ya fara bayanin facin wando Ibra yake ta dariya, har ya gama faɗa masa amma bai tsagaita dariyar ba sai da abin ya ishi Malam Nura ya kalli Ibra cike da takaici ya ce

"Dalla Malam ba kyauta za ka yi ba kuɗinka zan cake na baka" Dariyar ta tsagaita ya ce

"Zan yi maka mana ai ka san ni da kai bata ɓaci, kawai dai lamarin ne ya bani dariya, yanzu duk kuɗinka abin ka sake ɗinka sabuwa ka zauna kana ta wannan lissafin, ka yarda mace ta maka aika-aika har burinta yake neman cika" Malam ya ce

"Burin Kuluwa in tozarta ni kuma ba zan tozarta ba kuma sai na yi bikin nan yadda ba ta so, kai dai ka yi ƙoƙarin fito mini da shaddar nan kawai" Amsa masa ya yi ya ajiye aikin da yake ya shiga yi masa nasan kamar yadda ya buƙata. Malam yana zaune a gefe aka yanki ƙasan rigarsa aka yi ƙasan wandon aka yanke ƙasan wandon yadin aka jona na shaddar. Bakin Malam Nura har kunne ganin kwalliya ta biya kuɗin sabulu yana kallon Ibra cike da girmamawa ya ce

"Ba gashi ba, ai wallahi da na san za a iya yin wannan dabarar da ko wajen ɗaurin auren ba zan je a haka ba" Ya faɗa yana karɓar wandon ya kara a jikinsa ganin ya masa yadda yake so ya biya Ibra kuɗin gyara har da ƙari. Ibra yana ta tsokanarsa ya ɗauki ledarsa ya nufi gida, lokacin gar an fara kiran sallar la,asar, Hadiza kuwa ya kira ta ya fi sau goma amma bata ɗauka ba, da ya gaji sai ya ƙyale ta. Babu abin da ya saka a cikinsa wuni guda, haka ya wuni a shagon ana masa gyaran sai da ya ga ya kammala sallah ce kawai take fito da shi daga shagon, ko da suka haɗu da Hudu a masallaci ma ya sanar da shi cewa yana can ana masa ƴan dabaru dariya ya masa saboda ya san kawai wandon nan ba zai saku ba.

Lokacin da ya shigo gidan, matan nan duk sun watse sai kaɗan, bai ga Kuluwa ba, shi ma bai nemi inda take ba saboda daman ba nemanta yake ba, a cewarsa tauraruwa mai wutsiyaci ganin ta ma ba alkairi ba ne. Ɗakinsa ya nufa ya rufo ƙofar cike da hanzari ya cire kayan jikinsa ya saka wandon ya ɗora rigar ya kalli jikinsa ya fashe da dariya a fili ya furta

"Hadiza daman rashin wando ne ya mini cikas yanzu za ki tabbatar da cewa wanka iya wanka Malam Nura ya iya" Ya faɗa yana sake kallon wandon tabbas ba a ganin saman yadin da aka haɗa daga sama, sannan waje da aka yi ɗinke-ɗinken ma ba a gani sai dai wanda ya yi kallon ƙurilla. Kayan ya cire ya linke, ya ɗakko wani kayansa ya saka don bai mayar da yadin Hudun ba saboda haushin yadin ma yake ji.


Ya gama kenan, Haule ta zo ta buga ƙofar ya ce

"Waye?"

Ta ce

"Ni ce fa ango na amarya Hadiza" Wani daɗi ne ya baibaye shi jin kiran da ta masa, duk da yana jin haushin yadda Hadiza ta masa a gaban mutane amma kuma da yake bahaushe ya ce, so hana ganin laifi, sai ya fara ganin laifinsa ne ba laifin Hadizar ba.

Yana washe baki ya buɗe ƙofar yana faɗin

".Na baki ɗan mutum da uwarsa" Dariya ta saki tana faɗin

"Ai ka cancanta ne ango, Allah dai ya sa an ɗaura a sa,a ya bada zaman lafiya" Da amin ya amsa har ya yi shiru ya ce

"Haule anya kina sona?"

,Haule ta ce

"Mai ya kawo wannan maganar?" ,

Malam ya ce

"To ai ke ɗin ce sai kike ta nuna kamar dai bakya kishina, amma ko kaɗan ne ai kya ɗan gwada min kishi" A fili ta ce


"Ai ka san ka so abin da mutum yake so ma yana cikin so"


A zuciyarta ta ce

'Ku maza mace ma ta yi kishin ku ta haɗa kanta da wahala, yanzu ba ga Kuluwa nan daga yin kishi kake neman nakasta ta ba, haka kawai ai gwara ma mace kar ta ɗora namiji a ranta hakan zai sa ta zauna lafiya'

Malam ya ɗan yi shiru ya ce

"Kuma fa haka ne"


Haule ta ce

"Yawwa, daman na ce ko a kawo maka abinci na ga baka zauna ba ma bare ka saka wani abu a cikin ka, ni kuma duk na damu" Dariya ya yi ya ce a zuciyarsa

'Namiji ɗan gatan mata, wato dai kai idan matarka ɗaya ce shikenan ba kowacce mace ce take bada kulawa ba, amma idan sun haura ɗaya sai abin da ka gani kowacce sonka take' ,A fili ya ce


"Barni Haule ai no yau ban ga ta zama ba an saci ɗan ɓarawo, babu batun cin abinci har sai na je na yi hoto da Hadiza kin san ranta ne ya ɓaci da bamu yi hoto tare ba da ta ganni da wannan yadin" Haule ta ce

"Ba dole ya ɓaci ba wataƙila ta shiryawa ranar ne"

Malam ya ce

"Shiri ma ai in kin ji ɗaya kenan, in banda wannan Kuluwar ƴar wahala ta kawo mini cikas har akwai wanda zai kaini wanka" Shiru ta yi bata ce masa komai ba, saboda ba ɗabi,arta ba ne yi da kishiya a bayan idanunta.

Sallama ta masa ta ce sai ya fito. Tana fita ya fito ya ga wani bokiti cike da ruwa, lokacin tsakar gidan ma babu kowa sai su Alawiyya suna cin abinci. Yana ɗaukan bokitin ya yo hanyar banɗaki, ya shiga ya rufo, Kuluwa tana kallonsa kuma ruwanta ne amma sanin akwai wata wutae tsakaninsu ya sa bata fito ba, domin ita hankalin ta kwance an yi ɗaurin aure ya je da tsohon kaya, kuma yanzu ma don zai je ya yi wanaka ta san sai dai ya saka wasu kayan aron.


Yana shiga ya yi wanka ya fito, ya shiga ɗakinsa ya saka sakata, yana goge jikinsa ya saka singlet, ya ɗakko rigar shaddar nan ransa fari ƙal ya saka ta ya saka wandon da ya zo ɗauree mazugin sai ya ga ƙarami ne Ibra ya saka masa, ɗazu ma da ya gwada saboda a ruɗe yake shi ya sa bai lura ba, wata zuciyar tana faɗa masa ya cire ya saka wani wata tana faɗa masa kawai kar ya ɓatawa kansa lokaci ya bari.

Maɓallin ya ɓalle ya ɗakko hularsa ya gyara karin ya goga mata turare ya saka, ya sanya turare a kayansa sosai ƙamshi ya cika ɗakin ya saka takalmansa ya je gaban madubi, ba ƙaramin kyau ya yi ba sosai ya yaba yana fatan Hadiza ta yaba fiye da shi a fili ya ce


"Ashe dai ina da fasahar da zan saka shaddar nan a ranar nan amma na zauna na je ɗaurin aure da tsohon kaya" Ya faɗa yana ɗaukan wani tsumma ya sake goge takalmin sa. Ƙaramar ledar da magungunan mazan sa suke ciki ya ɗakko, wanda Hudu ya faɗa masa sai ranar da amarya za tare zai sha, sannan ya ce masa a huɗu zai raba maganin, wata ƙaramar kwalba ce kamar ta magani, a jikinta an sake laulaye ta da leda a cikin ledar kuma wata ƙwayar magani ce guda ɗaya, ita ƙwayar Hudu ya ce masa a biyu zai raba, ita kuma na kwalbar a huɗu. Yana ɗaga kwalbar bayan ya buɗe sai da ya sha ya fi rabi, wanda ya bari bai fi kwata ba, ya ɗauki ƙwayar da aka ce ya raba a biyu ya saka a baki ya tsotse ita ma ya tsotse ta duka, ya mayar da komai cikin ledar ya ɓoye.

A fili ya ce


"Ba a bori da sanyin jiki, ai tun da dai amarya yau za ta tare ina na ga ta zama, ai gwara na shanye duka, shi ma na kwalbar da na rage saura da daddare kafin a kawo ta zan shanye tasss, don ba zan zauna ta raina ni ba gwara ta san babu raini a lamarin"


Ƙofar ya buɗe ya fito yana cikin kullewa Haule ya fito daga ɗaki, wata uwar guɗa ta carara tana faɗin


"Kai ma sha Allah, kyau iya kyau ango, wanka iya wanka, na Hadiza jan gwarzo, na Hadiza mai kyan mamaki" Ɗari biyar ya ciro ya miƙa mata ya ce

"Ki ba su Alawiyya hamsin-hamsin ki riƙe canjin" Karɓa ta yi tana masa godiya, sannan ta ce

"Malam idan an yi sallar magriba zan je gida, baba zan dubo bai ji daɗi ba duk da dai an ce jikinsa da sauƙi amma dai zan dubo shi"

Malam ya ce

"Subhanallahi, a ki je kya masa sannu kafin in samu in ɓulla" Amsa masa ta yi ya yi gaba abin sa.

Kuluwa wacce take ɗakinta jin guɗar da Haule ta yi ya sa gabanta faɗuwa, musamman kirarin da Haulen ta masa ya ƙonawa Kuluwa rai, amma haka ta taso domin ganewa idonta tun da dai bahaushe ya ce baba bori da sanyin jiki, tana leƙowa daga window abin da ya gani ne ya ɗaga mata hankali sa sauri ta dafe ƙirji tana zaro idanunta don su tabbayar mata da abin da ta gani zahiri ne ko kuwa gizo ne. Tabbas shaddar da ya ƙona wandon ta ce sanye a jikin Malam, kuma wandon ne take gani sannan shaddar sak ce a wandon daga gani ba haɗawa aka yi ba wato ba wata kalar shaddar ce aka samu wacce zanen ba ɗaya ba ne.


Ranta ne ya ɓaci sai dai bata da damar amayar da abin da yake cikin ta, tun da ta san yanzu ma da sauran rina a kaba tun da ba yafe mata ya yi ba.


Malam kuwa fita ya yi hannunsa ɗaya a aljuhu ɗaya yana riƙe da wayarsa da take ta ƙara. Yana fita Kuluwa ta fito tana huci kamar zakanya wani uban ƙamshin turare ne ta jo ya ziyarci hancin ta, ko ma ta ce ya buɗaɗe tsakar gidan, tsayawa ta yi ta kama ƙugu tana wani karkaɗa kai ta taɓe baki ta ce


"Oh ni Kuluwa duniya sabuwa Malam Nura sanye da sabuwar shadda mai tsada yana ƙamshi tamkar an yi ɓarin turare" Haule ta yi dariya ta ce

"Wallahi kuwa wai wajen amarya Hadiza zai je su yi hoto... Tun bata ƙarasa ba Kuluwa ta tari numfashin ta da faɗin


"Ke kam Haule Allah yaye miki, yanzu a gabanki mijinki ya fita ya tafi wajen wata banza, amma har kike wasa shi kina ce masa wani na wata can banza, bayan kin san a cikin gidan gani ga kuma ke, ai ko da me -da me biyu ta fi ɗaya ko a rabon gado!" Haule ta tsura mata ido ta ce
..."To ina ruwana ita ma ta yi ta kanta, kuma ai na ga matarsa ce, to ya ma kike so na yi cakumarsa kike so in yi mu yi dambe saboda zai je wajen matarsa, to wallahi ni ko wajen bazawara zai je ba zan wahalar da kaina ba"


Kuluwa ta ce


"Ke dai na lura wannan ɗan kuɗin da yake baki ne suke rufe miki ido sho ya sa bakya samun damar nuna kishin naki"

Haule ta yi wata ƴar bazawarar dariya ta ce


"Ai ko da me da me kurna ta fi magarya zaƙi, inaso ki sani ba wai ba na son Malam ba ne kuma ba wai ba na kishin sa ba ne, a,a kaina dai na shafawa lafiya game da lamarin maza, sannan abu na gaa kin san da neman kuɗi nake kaina da ƙafata ina sana,a to kuɗin na nasho da bai taka kara ya karya ba maganin matsalata zai min? Kin ga kenan kawai dai a bar kaza a gashin ta, ke da kika ɗorawa kanki kishin da mai kika tsira, ba don Allah ya rufa asiri ba da yanzu ƙafafun ki biyu ba sa jikin ki" Tana faɗar haka ta juya ta bar wajen.

Ran Kuluwa ya ɓaci jin Haule ta faɗa mata magana, tana yin ƙwafa ta ce

"Hummm ba Hadiza ba ko Hadizo ce ta zo ina nan ina jiranta, tun da dole a ci kasuwa da maƙiyi, kuma hangen dala ba shiga birni ne ba, in da Malam Nura ne kaska ne raɓi mai jini ki bar shi da gashi, ai mai kashe miciji sai ya yi niyya zai ɗauji sanda, a yi dai mu gani idan tusa tana hura wuta, mu dai mazaunai ne ko dan zama za a neme mu, mu zuba mu gani, matuƙar ta shigo gidan na ƴar kallo za ta zama, don ni ce da ragamar mijina, an aure min miji maimakon ta koma gidan mijin ta shi ne aka ƙi cin biri aka ci dila" Duk wannan karin magaanar da take Haule tana jin ta bata taka mata ba.



Malam Nura yana fita ya amsa kiran Hudu nan ya faɗa masa gasu nan zuwa, haka suka zo da wasu abokan nasa guda biyu suka ɗunguma zuwa gidan su Hadiza suna ta zuzuta irin kyan da ya yi.


Malam Nura ya murmusa ya ce


"Ni fa daman na faɗa maka Hudu sai na daka shaddar nan, amma dai har yanzu ina kan bakana idan ka samu mai saye ya zo na fansar masa" Hudu ya yi ƙasa da tashi muryar kamar yadda Malam ya yi lokacin da zai faɗa masa ya ce

"Waye zai sayi wannan shaddar wando da ɗori ɗori" Shiru ya yi sai kuma ya ce


"Ai idan aka samu mai son banza tsaf zai saya yake maleji, tun da nima ai sauƙi zan masa tun da na san wandon haɗi-haɗi ne wato yadi da shadda, wa ya ga haɗin gambiza" Ya ƙarasa faɗa yana dariya.

A ɓangaren Hadiza ita kaɗai ta san irin ɓacin ran da ta ƙunsa, ranta ya sosu game da abin da Malam Nura ya mata abin ya fi mata ciwo ma da ya kunyatata a gaban ƙawayen ta bayan ta gama shirga musu ƙarya. Ta san ko ƙaramar hauka za ta yi Malam Nura ba zai sake ta ba amma dai ta ƙudurta a ranta cewar ba za ta tare yau ba ko ana muzuru ana shaho,a ƙalla sai ta shafa satika ba ta tare a gidansa ba sai ta gama bashi wuju-wuju sai ya san ita ya tozarta.


Haka ta wuni suƙuƙu ranta a ɓace, don Zainaba ma sai da ta ce mata


"Inna wai ya na ga angon bai saka sabon kaya ba, kika ce tare ya siyo mana shaddar, wallahi ko kaɗan bai yi kyau ba kamar dai ba ango ba, sauran abokan nasa duk sun fishi yin kyau, ai daman babana ya fishi iya gayu shi ya sa na ce ki koma amma kika ƙi" Harara ta zabgawa Zainaba kamar idanun ta za su faɗi, da sauri Zainabar ta bar wajen tana ƙunshe dariyar ta.


Da yamma kasancewar ta yi gayyata hakan ya sa ta sake sabon ɗauri inda aka mata kwalliya da ɗaurin ɗankwali, haka suka fito ana ta gaisawa da muyane da suke Allah sanya alkairi. Kamar an ce ta waiwaya idanunta suka sauka a kan su Hudu da sukw tahowa, tabbas ta gane su Hudu domin Hudu bai sauya kayana jikinsa ba, sannan sauran abokan ma duk ta gane su tun da da su aka zo ɗazu, wato ta shaida kayan jikinsu duk da cewar daga ɗan nesa ne ta hango su. Na huɗun ne bata gane ba, mai kalar shaddar irin ta jikin ta, wani ɗan gayu ta gani amma da yake ta san Malam Nura bai zo ɗaurin aure da shadda ba ma, shi ya sa bata ma yi tunanin shi ba ne. Ranta ne ya ɓaci domin ta san abokansa ne ya aiko su zo su bata haƙuri a kan yana ya kiranta bata ɗauka, kuma ta san dai zancen gizo ba ya wuce na ƙoƙi, ma,ana duk a kan maganar tarewar ta ce yau, za a kafa mata ƙahon zuƙa, ita kuma ta saka a ranta daidai da zamanin su take, wato sai ta musu tatasss sannan ta faɗa musu ba za ta tare ba sai nan da sati biyu kuma sai idan ya cika sharuɗɗan da za ta gindaya masa, juyawa ma ta yi daga kallon nasu ta ci gaba da gaisawa da mutane don ma kar su ga fuska su yi zaton za su samu sassauci daga gare ta.



Malam Nura ganin an kusa zuwa wajen da sahibar tasa take sai wani bubbuɗawa yake shi ala dole yana son kashe ta da mamakin wankan da ya yi. Sai da suka zo dab da su Hadizar ya mayar da wayarsa aljihu ya sanya hannayensa duka biyu a aljihun rigar ya tsaya daga gefe irin tsayuwar nigogin nan yana son ya mata ba zata don ya san ranta a ɓace yake tun daga batun shaddar nan. Shi kuma yanzu so yake a daidaita ta tare a yau domin ya gama shiryawa yau a matsayin ranar tariyar ta, kuma ranar amarci.

Ko da suka zo su Hudu ne ya yi musu sallama, suka je gaban su Hadiza, shi kuma ta bashi baya don

11 / 15