Goje 3 Hausa Books Complete By Binta Abbale

Author :  Binta Umar Abbale Category :  Read Hausa Novels

Chapter   11 / 13

30K to 33K   out of 37.7K words

kukan
ki ya kare_

*GJSR*

*101&102*
Itace a kusa dashi, Uwale da Hamra'u kuma a baya a tsakaninsu suke hirar da ta shafe su, ita
dai tayi shuru tana dai jinsu, gabadaya tunaninta ya ta'allaka ne gurin ganin yanda za ta koyi
mu'amula da 'yan uwansa, a jikinta takejin kamar akwai abunda zai faru sakamakon zuwanta
garin.
Shi tunaninsa yasha bam-bam da wanda takeyi, domin shi kadai ya san halin damuwar da yake
ciki a halin yanzu sha'awa ce tafi damunsa, gashi yayi wa Uwale alkawari yana ganin da kamar
wuya alkawarin nan ya tabbata domin tare da matarsa zai tafi, saboda samun saukin abinda ke
damunsa.
Daga karshe dai shuru yayi musu ya daina sanya musu baki a hirar sai ya kasance su biyu
kadai suke magana a motar yanayinsu ya nuna d'okin kasancewa da 'yan uwansu.


Daf da za su shiga garin ya kalleta, yaga duk tayi wani iri sai ya mutse fuska take, da alama
akwai abunda ke damunta ta dai yi shuru ne kawai.

Sassauta murya yayi da fadin." Menene."?

Kallonshi tayi da gajiyayyun idanuwanta tace." Zuciyata ce take tashi!.

Yace." Saboda me."? shuru tai masa tana ganin ko ta fada masa dalili bai zama lallai ya yarda
ba."

Yace." Ba zaki magana ba."?

Ta sauke ajiyar zuciya mai sanyi kafin tace." mybe tafiyar mota ne." Ta dan ja tsaki mtssw!
kafin ta cigaba da cewa ."idan ba yau ba din ba, bana tsammanin na ta'ba dogowar tafiya a
mota irin wannan."

Yayi shuru yana nazarin maganarta, kwarai hakan na iya faruwa idan anyi la'akari da irin gidan
da ta fito mostly masu kud'in nan ba sa jurar tafiyar mota 'karamar tafiya sai hau mata jirgi.

Yace."Sannu ai mun shigo garin da ikon Allah."

Ba tace masa komai ba kawai ta jingina kanta jikin kujera tana sauke numfashi sannu a hankali.

Uwale ce ta iya tofa albarkacin bakinta a kan maganar amma Hamra'u ta tafas! ba tace ba, sai
wani dauke kai take tana kumbura fuska.


Tunda suka shiga garin motar ta fara gargada tana ciccijewa sakamakon kwazazzabai da

ramuka! bayan wannan yara da almajirai suka dinga bin motar da gudu suna ihu!!!!!!!


Al'amarin ya daure mata kai mutu'ka! ashe lalacewar 'kauyen har ta kai haka? ko'ina ginin jar
kasa da wasu dirka-dirka bishiyon kuka da tsamiya had'e da mangaro gasu nan dai iri-iri! garin
cike da dabbobi barkatai yaransu da manyansu cikin 'kazanta abun dai sai godiyar Allah.


Uwale sai wangale Baki take tana d'agawa yaran dake bin motar hannu, a tunaninta suna
ganinta motar tintac ce ita take ganinsu amma su basa ganin na ciki, su dai farin cikinsu mota ta
shigo garin.


Can wani fili mai yalwa ya nufa domin gyara parking.....Lokacin gungun! yaransa suka durfafo
gurin suna bushe-bushe karnukan dake biye dasu na haushi gurin ya kacame! 'kura sai tashi
take!

Hankalinta ya tashi ganin haukan da yaran nasa suke! saboda haka yana gyara parking din ta
kalleshi lokacin jikinsa har ya fara tsuma! gumi na karyo masa! tace." Dan Allah kada ka biye
musu ina nufin kada kayi wannnan abun da kake bana so."

Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke ya ciro hankici daga jikinsa gumin fuskarsa ya goge kafin ya
juya gurinsu Uwale lokacin tana ta kici-kicin bude kofar motar.


Ya mika hannu ya bude musu kofar suka fita........Karnukan suna hangoshi a motar sai suka
sake rikicewa! da haushi kokari suke iske in da yake, ta rintse idonta da karfi tace." Kada bari su
shigo ka rufe motar.

Gaggawar rufewa yayi yana kallonta jikinta sai karkarwa yake, 'kwalla ta cika kwarmin idonta,
yana daya daga cikin dalilan da yasa bata kaunar zuwa k'auyen! ta tsani ta bude ido tayi tozali
da k'azaman karnukan da idanuwansu ke cike da kwantsa.

Yace."Wai meye hakane? ki saki jikinki kina tare dani babu abunda za suyi miki."

Ta kalleshi hawayen bakin ciki na zuba tace." Ba zan fita a motar nan ba sai ka sallami wa'innan
'kazaman dasu da karnukansu bana san ganinsu.

Yaji haushin maganarta amma sai ya basar! kawai ya bud'e 'kofar ya fita.....aikuwa karnukan ne
suka dinga tsalle suna rungumeshi! akwai sabo mai tsanani a tsakaninsu. takaici da bakin ciki
ya ishe ta, kullum yana kiran kansa musulumi amma yana tu'ammali da karnuka wanda kowa ya
san hakan haramun ne a musulunci.

Alba ya kwance masa bakin wani kuttu dake cike da tsumi!!! sai kumfa yake!! ya kafa kansa ya
dinga kwankwad'a!! yana wata irin girgiza!

Gurin cika yayi manya da yara duk sun kewayeshi alamu dai sun nuna jama'ar garin suna
alfahari dashi.


Duk bada'kalar da take faruwa tana kallo, duk rokon da tayi masa hakan bai sa ya fasa abinda
yayi niyya ba, kafaffar wu'ka gayawa jini na wuce! ya kar'ba a hannun Alba tana walwali ya
fara dadurawa! a wuyansa! anci sa'a wannan karan bai cire rigarsa ba. ya kai minti goma
yana gurzawa wu'kar! kafin ya kurma! uban ihun! da ya sanya gurin amsawa! ya fara kai kawo
a gurin yana dukan kirjinsa!

Takaici yasa kawai ta sunkuyar da kanta 'kasa bata tsammanin zata iya cigaba da kallonsa yana
wannan halin.

Farar shaddar jikinsa ta rine! tayi jajawur! ta jike da gumiin jikinsa! hatta! da gashin kansa digar
da gumi! yake!

Kawu Ado ne yayi namijin tunkarar gurin da yake! yana kokarin rike hannunsa yana fizgewa! jin
karfi kawai yake yana wani tattaune bakinsa, su kuma yaran sai kara kambaba darajarsa suke
suna 'kara tayar masa da tsumin da yake jikinsa.


Maigari da jama'arsa suka 'karaso gurin domin suna zaune a fada labari ya samesu cewa
*GOJE!* ya shigo garin.

Maigarin ya samu nasarar isa gurin da yake......Kawu Ado ya rufa masa baya. dukkaninsu
*mubaya* (goyon baya) sukayi kafin ya sadadu! Maigari da Kawu Ado hannu na dukan hannu
💪🏻suke masa kirari! *Cau!! Sa'a dai!! Mai maganin wuka da kaho."!!* ire-iren wannan kirarin
suka dinga yi masa kafin su samu kansa! jagab! ji'ke da gumi suka rirrik'eshi domin shiga dashi
cikin gidan.

Cikin uwar dakin Uwale Kawu Ado ya zaunar dashi, kafin ya fita ya sallami yaran nasa da har
yanzu ba su daina bushe-bushe da buga gangani ba, garin duk ya hautsine! sai kace wani
babban basarake ne ya sauka.


Da sauri- sauri yake sauke numfashi makogwaronsa sai suya yake, a maimakon yaji sha'awar
ruwan sanyi amma abun mamaki a lokacin babu abunda yake bukata face hayakin Sigari ko
shisha duk dai wanda ya samu.

Sai da ya dan samu nutsuwa tukkuna ya fito, aikuwa ya tarar tsakar gidan cike da mata 'yan
uwa da kuma abokanar arziki.

Kaf ya dube gurin babu ita babu dalilinta.

Gabansa ya fad'i! ya kalli Uwale da fadin." Ina Zinatu."?

Tace." Umaru ai kai zan tambaya ni da na barka tare da ita a mota."


Ba tare da ya sake wata magana ba ya kama hanyar fita......matan dake tsaitsaye a gurin sai
gaisheshi suke da kyar yake iya amsawa, gabadaya hankalinsa na gurinta.


Tunda ta hango fitowarsa daga gidab ta dauke kai tare da jan tsaki! cikin ranta take ayyana
wasu abubuwa a kansa.

Ya bud'e motar idanuwansu suka had'u! bai ta'ba jin kunyarta ba irin yau!

Yayi saurin janye idonsa yana dawurwura domin ya ma rasa me zai ce mata.

Ganin haka ya sanya kawai ta girgiza kanta ta fara kokarin fitowa daga motar. ya dauki
handbang d'inta ya rike yana gyara mata hijab din dake jikinta.

Cikin gajiya ta fito daga motar tana dudduba gurin.

Ya rufe motar da fadin.'' Muje ko."? Gaba yayi tabi bayansa kamar bata son taka 'kasa.

Handbag din ya mika mata da fadin." Ki shiga zan shigo yanzu."?

Kallonsa tayi na minti biyu kafin ta girgiza kai da fadin." Ni ba zan shiga ni ka d'ai ba."

Bai ce mata komai ba ya koma gurin motar ya bude ya dauko Shishar sa dake cikin kwali! ba ta
gane komeye ba amma tana ta kallonsa gami daso ta hasaso abunda yake cikin kwalin.


Ido ne yayi caaaaa! a kanta yayin da suka shiga gidan......Wa'inda basu santa ba tambaya
kawai suke "Wannan ce matar UMARU."? Uwale na basu amsa daidai da abunda suka
tambaya.

Ita dai kasa tsayuwa tayi kawai tabi bayansa dakin da taga ya shiga.

Hamra'u na dakin sai share-share take.......Yanayin dakin ya nuna nasa ne tun lokacin

samartaka duba da irin tarin kayan farauta da suka rataye a bagon dakin da kuma tarin
buhun-buhun magungunan gargajiya irin wanda yake bayarwa.


'Kura duk ta tashi a dakin sakamakon rashin gyaran da bai samu ba tsayin watannin da suka
wuce.

Taja ta tsaya bakin k'ofar tana mata wani irin kallo, wallahi bata ta'ba ganin mara zuciya irin ta
ba, kullum cikin bautar namijin da babu guarantee akansa.


Ganin yaki mata magana yasa ita ta magantu tace." Kin ga ya isa haka don Allah! mutumin da
ba zama yazo ba meye zaki damu kanki gurin gyara masa daki, ko kin manta yau zai tafi."

A sanyaye Hamra'un ta kalleshi wai ko zaiyi magana, Uffan bece ba shima so yake ta fita ya
samu sararin busa hayak'insa.

Jiki babu kwari tazo za ta wuce da tsintsinya a hannunta, hanya ta matsa mata har yanzu kallon
shashasha take mata, to idan ba haka ba akan me zata dinga wahalar da rayuwarta.


Ta fita daga d'akin ya fito da shishar ya fara tada hayaki!


Ta kalleshi da fadin." Ni ce marainiyar wayonka ko.''?

Ya kalleta tare daso tayi masa karin bayani.

Murmushin takaici tayi kafin tace." Ka b'oye ashararanci da kake a idon duniya saboda gudun
abun magana amma da yake ni ka mayar dani towon tushe baka jin kunyar aikata abu mara
kyau a gabana."


Ya fesar da hayakin dake bakinsa kafin yace." Kwalbar giya ki ka gani a hannuna."?

Tayi shuru tana kallonsa

Yace." Wannan da yake hannuna! bashi da lada ko zunubi! sanya kai ne ga wanda yake da
ra'ayi kuma bana sha sai irin haka ta faru, ko kin ta'ba tsintar karan Sigari a aljihun rigata."?


Ba tace komai ba tana dai ta nazari da tunani a kansa.

Yayi murmushi da fadin." Ko kin manta kalmar da take cewa (Mata sirrin miji) kece sirri na
kuma ina da ta tabbacin cewa duk rintsi duk wuya zaki rufa min asiri a kowane hali, akwai
bambanci sosai a tsakaninki da Hamra'u."


Maganganunsa suka kashe mata jiki, ta dinga kallonsa tana sake jin kaunarsa na ratsa sassan
jikinta.


Da hannu ya nuna mata kusa dashi da fadin." Zo ki zauna kusa dani sanyin idanuwana."

Murmushi tayi kafin ta nufi gurin ta zauna kusa dashi da fadin ." Dubi jikinka yanda ya 'baci!
kayi wani dukun-dukun! sam wannan rayuwar ba ta dace da kai ba."


Ya ajiye abunda ke hannunsa gabadaya ya mayar da hankalinsa kanta, yace." *ZINA* ina so ki
fahimci wani abu, wannan abun fa ya kai matakin da ba za'a iya raba ni dashi ba, ya riga ya
zama jiki da Jinina! duk sanda tsumin ya tashi bana iya sarrafa kaina, tun ina yaro nake shan
magungunan tauri! a cikin dabbobin da Allah ya hallita masu rai kad'an ne ban ci ba. nayi
gwagwarmaya da jinsi mutum da aljanu domin har so sukayi su bude min ido! ni ne ban bada
goyon baya amma duk da hakan wani lokacin idan sun so suna ziyartata muyi hira su tafi salin
alin ba tare da sun cutar dani ba.... babu tabbas akan aljani kuma ba'a yarda dasu amma ni
bana tsammanin cewar zasu cutar dani da duk wanda ya shafe ni, dalili musulmai ne kamar
yanda nake musulmi saboda haka ki kwantar da hankali kisa a ranki cewa ni ne abokin
rayuwarki."


Gabadaya jikinta ya mutu jin abinda yake fada........Dama ta jima tana zarginsa cewa bashi
kadai yake rayuwa ba akwai masu taimaka masa.

Ta rasa wane irin tunani za tayi a kansa.

Yace." Bayan sallar la'asar za mu tafi gida bana tsammanin barin ki a garin nan."

Wani bala'in dadi y rufe ta, amma bata nuna masa ba tace." Saboda me."?

Shu'umin kallo yayi mata kafin yace." Ba zan iya bacci ba yau saboda sha'awar dake damuna
kwana biyu kina fushi dani kin daina kwana a dakina."

Sunkuyar da kanta tayi tana wasa da yatsun hannunta.

Hannu yasa ya daga fuskarta, wanda yayi daidai da shigowar Hamra'u dakin tana sheda masa

ruwan wankan data dora masa yayi zafi."

Hankalinsa gabadaya yana kan matarsa ya amsa da" Okey to na gode kanwata."

A sanyaye ta saki labulan d'akin, zuciyarta kamar ta fashe sakamakon abunda ta gani a
tsakaninsu.



Yana fitowa daga wankan Uwake ke sheda masa cewa Kawunan sa suna son
ganinsa......Yace." Babu damuwa yanzu zai shirya yaje ya samesu.


Ya shiga dakin ya sameta a kwance saman katifarsa sai juye-juye take cikinta ne yake ciwo ga
yunwa na damunta.


Cikin kulawa yace." Zina akwai abunda ke damunki amma idan na tambayeki sai kice babu
komai."


Tana ya mutse fuska tace." Ciki na ne yake ciwo idan ba amai nayi ba to ba zan ji dadi ba.

Girgiza kansa yayi da fadin." Sannu Allah ya sawwake me kike bukata idan na fita na kawo miki
kin san muna da komai na gargajiya."

Tace." Goba da mangaro amma irin wa'inda basu nuna ba."

Yace." Shikkenan."? shuru tayi na minti biyu kafin tace." Meye ma sunan abun."?

'Yar dariya yayi kafin yace." Agwalima kuke ce masa ko."? tace." Yawwa dashi da kuma
Magarya."

Yace." An gama ranki ya dad'e! amma gyad'a marau-marau fa."

Dariya ya bata kafin tace." Ina so." Yace." To insha Allah zan kawo miki, ki kwanta ki huta
yanzu ni zanje gurin. Iyayana suna nema na.".

Tace." To babu damuwa a ce ina gaishesu." Yana kokarin fita ya amsa da zasuji insha Allah."


Yayi wa Uwale sallama lokacin tana kicin tana aikin soye-soye......da yake tana da irin kaji na
hausa wanda take kiwo a can baya, sai ta bar su a hannun Tasallah shine fa tasa aka yanka

mata guda biyar aka gyarasu tsaf ta kawo mata tare da duk abun bukata...




*Kada ki karanta min littafi ba tare da kin biya ba, kada ki saya ki fitar dashi, 'yar uwa kada kiyi
sharing, idan kina bukatar biyan kudin littafin #500 ne......0542382124....Binta umar
gtbabk....Idan kati zaki turo sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/26, 9:55 PM] Matar Malam😊: _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga
wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin
karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin
yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu
cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga
ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da
'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki,
bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya
muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin
ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita
kukanki ya 'kare da ikon Allah._



*103&104*
Su biyu ya same su zaune a cikin rumfar kwanon dake k'ofar gidan Kawu Adon, a nutse ya cire
takalmansa kafin ya hau kan tabarmar ya zauna cikin girmamawa suka gaisa da juna tare da
tambayar bayan rabuwa.........Kawu Haruna yace." Bayan rabuwa sai alkairi Umaru abubuwa da
yawa sun faru masu dadi da marasa dadi sai godiyar Allah dama kuma haka duniyar take yau
da gobe duk na Allah ne."

Yace." K'warai hakane Kawu Amma naji dadin ganinku cikin koshin lafiya babu wata matsala
wannan ne dalilin da yasa hankalina ya kwanta sosai dan idan ba dole ba, babu yanda za'ayi
nayi nesa daku to kana taka Allah na tasa tabbas hukuncin da Allah ya zartar shine dai-dai."

Kawu Ado yace." Umaru mu ai hakan abun alfahari ne a gare mu, domin ka fita zakkah a cikin
mu, nasan yanzu da yawa wa'inda suke zagin ka a baya jikinsu yayi sanyi domin bahaushe
yace (Dan hakin daka raina shike tsone maka ido) kuma Ubangiji na saukar da ikonsa sai dai
kallo, shiyasa idan kaga wani yana aikata kuskure babbah ko yaro ta kafadi alkairi ko kuma kayi
shuru, jama'a da yawa sun kasa gane hakan, sai sanda Allah ya saukar da ikonsa tukkuna,
saboda haka ka daina damuwa wai dan kayi nesa damu hakan ne alkairi a gare mu bakidaya."

Cike da jin dadin maganar yace." Masha Allah Kawu Na gode kwarai da addua da kuma fatan

alkairi Allah ya kara girma."

Suka amsa da ''Ameen." kafin gurin ya dauki shuru na 'yan mintina.

Ya dan gyara zamansa da fadin." Uwale ce ke sheda min cewa kuna nema na."

Gyara zama yayi tare da gyaran murya kafin yace." Mak'asudin kiran akan wannan yarinya ne
Hamra'u!

11 / 13