sa Abbas."
“Haidar ga wanda na maka.” Haidar ya saki murmushi yana kallon Abbas sai ya ce.
“Masha Allah kaman kasan ina so na ƙara maka magana.”
“Ya yi maka?.”
“Eh, Abba tunda Injin miya ne ya kawosa na amince, amma sai nan da wata uku zuwa lokacin mun kammala wannan aikin har result ya fito, amma kafin nan ya fara zuwa dan sanin komai kafin na zo."
“Alhaji dama shima yana so ya kammala karatunsa gashi shirin exam suke yi ma.”
“Ma sha Allah, ai hakan ya yi, da ka kammala kawai ya zo nan.” godiya suka mai sosai.
“Abbana sai na dawo.” Haidar ya faɗa yana raba hannuwansu.
“Da kun isa ka tabbatar ka kira ni.”
“Insha Allah, Abokina zo muyi wata magana mana.” daga haka ya ja hannun Abbas, tare suka jera har gaban wata arniyar mota wanda ya shiga cikin ya ajiye abubuwan hannunsa sannan ya ce.
“Za mu yi magana, dan Allah ka riƙe amana, domin kuwa ni ba wani zama zan dinga yi ba, ina yin wasu ayyukan, amma karka damu zan ki raka, number ya yi?.” ya miƙa mai wayansa yana faɗin.
“Eh Sir, sai na jika, Na gode sosai.” murmushi Haidar ya yi yana faɗin.
“Injin miya zai baka saƙo." Daga haka ya tada motar yana fita.
Murmushi ne kwance a kan fuskarsa ya iso wajensu Alhaji.
“To muje."
“Injin miya ai ƙwayi breakfast, mu shiga ciki." Hmmmm ai ba'a magana kawai, Ogan Abbas da Abbas sai bin ko ina suke yi da kallo, dan gidan ba magana, a parlour suka zauna.
“Maman Safna, a haɗa musu breakfast, wai har kin shirya ne?.” Maman Safna da take sanye da hijab har ƙasa ta faɗaɗa murmushi tana faɗin.
“Eh Abban Haidar, muna so mu dawo da wuri ne."
“Okay, karku daɗe, kuma kuja ma Driver ku ja mai kunne ya bi da ku a hankali.”
“To Abban Haidar."
“Ku bi Flight kawai, zan miki transfer.”
“To muna godiya, daga haka ya yi part ɗin Ummin Haidar, wani harara ta dalla mai, dan kuwa duk buru-uba yau sai sun shiga tsakanin su.
Abinci masu rai da lafiya Zahra mai girki ta haɗa musu, aikam suka ja daɗi, bayan sun gama Alhaji ya basu dubu hamsin ladan aiki, sannan ya biya su kuɗin aiki. Aikam sun mai godiya sosai.
“Abbas sai mun ganka."
“Insha Allah.” a dai-dai lokacin ƴam mata biyu suka fito suna ta ranƙwaɗa, gaishe da Abban Haidar suka yi, sannan har sun ɗaga ƙafa sai Abban Haidar ya ce.
“Ni kaɗai kuka gani?.” da sauri suka gaida sauran, sai dai me da sauri Sumayya ta kuma kallon Abbas tana faɗin.
“A....A...Ab...Abbas.” ba shi kaɗai ba dukkansu suka kalleta, dan yadda ta kira sunan nasa.
“Abbas ni ce fa Sumayya Abu Haidar." (haka sunan su yake har a school, komai Abu Haidar ko Abban Haidar, shi yasa suka tsanar Haidar sosai).
“Bangane ki ba.” Abbas ya faɗa yana mamakin a in da ta sanshi.
“Yanzu school za ni, ban numberka za mu yi magana." Ganin kamar ba ta san Abban Haidar na wajen ba, yasa ya koma ciki, sam bai son ɗaga musu murya dan kanshi yana sarawa in ya yi hakan. Yana wucewa Ogan Abbas shi ya ba ta number sanann suka wuce.
“Ai da ba ka ba ta ba, sam ba ta da ɗa'a."
“A'a fa, kasan ko hakan wani alkairi ne." Suka ci gaba da hira har suka fita a babban haraban gidan.
Tana shiga mota ta rungume Safna tana faɗin.
“Finally na samu number Abbas."
“A Ina kika san shi?."
“Hmmmm a facebook, guy ɗin ya min, ke in kika bibiye page na shi ko, za ki kwasa ilimi, ɗan boko ne sosai, ina yawan ganin videos na shi yawanci friends dinsa ke daura, ke kinji speech, hmmm su 4 ne gaba ɗaya Poly na Kaduna ke ji da su.”
“Okay amma dai ba sonsa kike ba?.”
“Kina wasa ne, ai ni na haukace a soyayyar Abbas."
“Kina ruwa kinsan dai Mom ba za ta yadda ba." Ta figa motar tana wani sakin murmushi.
“Ni dai na gani kuma ya min.” girgiza kai kawai Safna ta yi dan tasan hauka kawai Sumayya ke yi............✍️
> Hmmmmm 🤐 yanzu wasan zai fara kun faji wata sabuwa Sumayya ƙanwar Haidar da son Abbas, gefe guda ga Merry ♥️, hmmm haɗin biza kenan....✍️
FREE PAGE'S ya kusa ƙare wa, ai munyi da waya, akwai point ɗin da nake so ku kai ne..... PRETTYN JAJIRTATTU ce ✍️.
💔 *_HASASHE KO BURI_* 💔
> 📖 A powerful story filled with dreams, struggles, and destiny!
PAGE 2️⃣9️⃣⏩3️⃣0️⃣
*ABUJA*
Su biyu ke tafiya a cikin mota suna hira, a hankali ta faka daga gefe dan ganin wasu mata sun tare motar, Zuby da ke driving ta sauke glass tana kallon mata biyun wanda a ƙalla za su iya haifa su. Bayan sun gaisa ɗaya ta ce.
“Dan Allah Filin Bora muke tambaya." Tana faɗin haka sai Darling ta ɗago ta kalle su.
“Ku shigo can zamu.” ba musu suka shiga cikin motan, dan kuwa ba kowa ke zuwa wajen ba, saboda hanyar babu ƙyau.
“Mama kuma wajen Mai sittin goma za ku?.”
“Ƴar nan eh.” Maman Safna ta faɗa tana jin sanyi a ranta dan yadda ake koɗa wannan malamin.
“Muma can zamu, gaskiya aikinsa ba wasa sai shi akwai tsaɗa.” cewan Zuby
“In da biyan buƙatar ai kuɗi ba matsala bane, munan daga Kano muke, flight muka biyo, to me motar da muka hau shine ya sauke a in da kuka same mu.” faɗin Maman Sumayya.
“Hala kuma an saku a gaba ne?.” Maman Safna ta tambayesu, sai da Darling ta yi murmushi sannan ta ce.
“A'a Mama, mijina zan sa a ƙara mallake min sa, sai ita ƙawata ya janyo hankalin sa wajensa.”
“Na ku da sauƙi, mukam kishiya ce matsalarmu, ta cike mana gida, ga yaronta shima duk sun hana mu jin daɗin gidan. Maganinsu za'a yi mana.” haka suka dinga hira kaman wasu sa'anni.
A wani tsohuwar Fili suka faka sannan suka fito, ba yawaitan gidaje a wajen sai wani ƙarami guda ɗaya. Suna isa jikin wajen suka bi layi dan mata ne a wajen sosai. Ba su jima ma ba Maman Safna suka fara shiga. Sannan bayan sun fito su Darling Suka shiga.
Mutum ne zaune cikin jajayen kaya, sannan fuskarta an shafe ta da farin fenti sai kuma zanen baƙi abu. Mummunan ne sosai, sai washe jajayen haƙoransa yake. Wani abune a hannusa yana jinjigawa sannan ya watsa akan wani ƙyalle. Magana ya fara cikin amon murya da cika kunni.
“Za ki aure Ukasha, kuma za ki juyasa yadda kike so, sai dai ki bi a hankalin domin jininsa na da ƙarfi, amma ki fara sanya wannan ƙwallin, sai kuma wannan garin ki jiƙa ana saura sati ɗaya bikinku kullum ki dinga sha da ruwa, sai dai ki tabbarar ke ce Uwar gida, da kuma ke ya fara mu'amala." Jiki na rawa Sumayya ta amsa wani ƙullin magani da ƙwalli.
“Ke kuma, karki damu mijinki na cikin kariyar mu, ku ta fi, kuje.” Darling ta aje mai uban kuɗi sannan suka fita.
A airport suka sauke su Maman Sumayya, sun musu godiya sosai, Darling harda alƙawarin in ta samu lokaci za taso gidansu tinda ita ma a nan Kano ɗin take.............
_Ashake_
Yayan Ashake bai jima da dawo wa daga aiki ba, Asheke kawai ya samu tana kallo a waya, bayan ta gaidashi ya amsa sannan ya shiga room ɗin sa can ya fito ya zauna sannan ya kalla Ashake da ƙyau ya ce.
“Àbúrò mi níyàwó sọ pé ọ̀la ló máa lọ sílé ìdílé láti dá ọrọ ìgbéyàwó dúró, ní oṣù tó ń bọ́ ni ó fẹ́ kí ìgbéyàwó náà wáyé. (Ƙanwata saurayin nan ya ce gobe zai je family house Dan tsaida maganar aure, a watan gobe yake so auren ya kasance.)"
“Ó dájú níyá. (Shike nan Uncle.)”
“Ṣùgbọ́n ọkùnrin náà ti ní fún ẹ̀ ni? (Amma yaron ya miki ko?)."
“Bẹ́ẹ̀ ni, níyá.(Eh Uncle.).” ta faɗa tan aiyana irin yaɗuwar Ukasha amma ba ya gabanta sam.
“Ó dára, fún mi nǹkan àmì, inú mi ń rẹ̀, níbo ni ìyá àbúrò rẹ lọ? (Yauwa, miƙo min Alama na ci yunwa nake ji, ina Auntynki ta je.).”
“Ó lọ rà àwọn ohun ìjẹun, ní báyìí ló máa wá.(Kayan miya taje siya, yanzu za ta shigo.)” da haka ta kawo mai abinci, a lokcin Maman Amira ta shigo, bayan a ajiye kayan miyan, Ashake ta ɗauki roba ta fita dan su wanke, gobe akwai aikin abinci.
"Surprisingly, it’s only you he loves, or maybe he has plenty money. (Da mamaki ace daga ke sai ke yake so, ko kuma yana da kuɗi ne sosai)”
“Yes o, I hope after marriage he will leave me to start working, because next week our results will be out. (Haka ne, fatan ɗaya bayan auren ya barni na fara aiki, dan next week result din mu zai fito.)”
“Okay, ask him for us, but about love, he just wants marriage, isn’t marriage supposed to be love? (To ki tambaye sa mana, amma ya maganar soyayya, shi aure kawai yake so, dama ana aure ba soyayya ne?)”
“Eh, maybe he wants love after marriage, only he knows. (Eh to maybe she bayan aure yakeson soyayyar, shi ya sani.)”
“Hmmmm, God should grant us good health, then let’s hear what the Alfas will say. (Hmmmm Allah ya nuna mana lafiya, sai ma munji me su Alfa za su ce.)” ta yi murmushi dan tunawa da Alfa, ƙanin mahaifin ta ne shima, yana da faɗa sosai, shima mai dai sam ba ya son hausawa.......
_Abubkar_
Kiran sallan farko ya farka, barcin ne ya ɗauke dat nan take, bayan ya yi alwala ya tafi masjeed, yana dawowa ya ɗan shingiɗa akan sopa, ba wani aiki ya yi ba jiya amma ya gaji sosai. Wayansa ya sake dubawa yana mai tuna ya karanta *Farin cikina* daga nan ya barcin ya ɗauke sa. *Mafarkina* shi ya shiga sannan ya fara karantawa.
( *MAFARKI NA* KIYaruwar ƴanci, rayuwa kaman kowa, ina so na shaƙar iskan ƴan ci, hmmmm sai dai Mahaifiya ta ce mun komai lokaci ne, kuma na haƙura ina nan ina jiran wannan lokacin, da zan zama tamkar tantabara, na yi shawagi kamar kowa.) Nunfashi ha sauke sannan ya shiga na gaba. *Damuwarta*
(Damuwata ɗaya ne tak shine ƙyau, wasu na nema ruwa a jallo, amma Allah bai basu ba, sai dai ni kam Allah ya jarrabeni da ƙyau wanda shine ya yi silar duk halin da nake ci, ƙyawuna ya yi wayan da ya zama min masifa, amma na ɗauka hakan a matsayin ƙaddarata, ina da ƙyau wanda ni kaina ina mamakin kallon kai na a mirrow, Alhamdulillah kawai, shi yasa na zaɓa ɓoye kai na har zuwa ga cikon *Hasashe na*.) Shafin a hanɗe yake dan haka ya dasa.
(Hasashe na, samun mamallakin zuciyata, wanda ya zai zama min gata, da na Mahaifiyata, ya zama min wani bango wanda zan dinga jingina a kodayaushe, ina fatan na Hasashe na ya faru ya tabbata ga duk wanda Allah ya zaɓa min, ina son muyi rayuwa bisa ta farkin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ❤️, ina son na koyar da yarana addini da kai na kafin su shiga makaranta, ina son na koya musu karatu amma kash ba ni da wannan ikon, ban da ikon rere musu karatun Alkur'ani, kai alkur'ani ya yi, sauti mai sanyi ga daɗi sannan ga riba, ni sai dai na yi a zuciya. Hmmmmm Hasashe na Maybe ya zama gaskiya......) Bai san hawaye ya ɗan gangaro daga idon saba sai da ya ji lema, tabbas kanshi ya yi nauyi, ya manta rabon da ya ɗauki alƙurani, da sauri ya miƙe amma me kaf gidan nan babu Alqur'ani, haka a cikin wayansa, download ya yi yana shiga har jikinsa na rawa. Suratul baƙara ya fara shiga bayan ya karanta fatiha, karatu ya fara yana mai kulle idanunsa hawaye na zuba, rero ayoyin kawai yake yi cikin fitar da hukuncin kowani harafi, ji yake tamkar an fara yaye mai wani abu a cikin zuciyarsa, ya jima yana kuka da karatun, take ya ji wani iska na ratsa shi sosai, shuru ya yi yana mai ƙura ma littafin Allah ido take yakai bakinsa ya sumbata.
“Yaushe rabon da na karanta wannan littafin? Me yasa na dena? Ya akai ban samu ko da Alqur'ani ɗaya ba a gidan nan? Me yasa har na wayana babu?.....” kiran da ya shigo wayarsa ne ya tsaida shi, dan Haidar ba ne ba yadda za'a yi ya ɗau wannan kiran. Bayan ya yi sallama a hankali, sannan shi Haidar ɗin ya amsa.
“Sir zamu ta fi, mun jira ko zamu ganka amma shuru, fatan lafiya?.”
“Eh Haidar, kuje kawai, kai na yana ciwo, Allah ya tsare kuma fatan sa'a." Ya faɗa da ƙyar, yana jin shi yana mai addu'a amma bai amsa ba. Sai ya ajiye wayan yana miƙewa sannan ya nufa cikin room ɗin sa, zama ya yi yana mai dafa kansa sai kuma ya miƙe ya fara Safa da marwa. Wani ihu yaji anyi a cikin kansa take ya zube a kan carpet ya suma.......
END.
> Hmmmm kunji wata sabuwa, Matan Abban Haidar sun haɗe da Darling wato Abubakar, sannan ga Zuby Kanuri ita ma, kuma wai duk a wajen *Malam Mai sittin goma* . Hmmmm ko ya ya tafiyar za ta kasance, mu je zuwa dai......
> Yau dai tsab mun karanta littafin *Ameeratulkhair* gaskiya ni kai na zan so sanin wacece ita, su waye suka ruguza komai na rayuwarta?, Su waye suka sa ta fara rayuwar rashin ƴan ci? Waye mahaifinta? Ko farcenta babu mai gani sai mahaifiyarta ashe dai wani lu'ulune a ɓoye....... Tabbas wani ƙyau ɗin masifa ne.
> *Abubakar* yau dai ka kai ƙarshe, sai Ameeratulkhair ta tinama waye *Allah* hmmmm kai dai Darling ta gama da kai wlh, a ce kaf gidan ka babu Alqur'ani, ka yi download ka karanta gashi daga ƙarshe ka faɗi, Suma ka yi ko barci 😓....... Mun dai HASASHE KO BURI✍️
💔 *_HASASHE KO BURI_* 💔
> 📖 A powerful story filled with dreams, struggles, and destiny!
PAGE 3️⃣1️⃣⏩3️⃣2️⃣
*KADUNA*
Su biyar ne a zaune a cikin ɗakinsu, Alhajin dake sanye da babban riga ya kuma yin murmushi sannan ya ce.
“Zuwa jibi zasu wuce, na so ace da ku a ciki, amma ku kammala karatun sai ku bisu, kar ku yi wasa da aikin nan domin sai an biya makuɗan kuɗi ake samu, amma saboda ina son taiamaka ku ne, farashin kaɗan na nema, gashi ana samu fiye da tina.” ya kai maganar yana ɗaukar pure water sannan ya kai bakinsa.
“Alhaji, insha Allah da mun gama zamu yi maka magana, gaskiya muna godiya.” faɗin Shamo sai I.B shima ya ce.
“Haka ne Alhaji, muma muna buƙatar wannan aiki.” sai ya duba wayansa alert ne da 800k ya shigo daga Mymoon.
“Zan biya mana kuɗin jirgin in lokaci ya yi." I.B ya kuma faɗa sai Alhajin ya ce.
“Shike nan.....”
“Gaskiya ni na fasa, saboda na samu wani aikin hannu kuma ya min sosai, dan kuwa nan da two month zan koma aikin a Abuja ƙarƙashin Company H - Halal Nigeria Motors.” Da mamaki suke kalla Abbas, sai ya ɗaga musu kai alaman tabbatarwa.
“Mene? Wai ba za ka U.S ba? Akan me Abbas?."
“Kawai dai Abdul.” yana faɗin haka ya yi waje.
“Aiki ne ai ba dole ba ne, akwai masu so zan musu magana, ku dai shirya.” daga haka Alhajin ya yi waje. Shuru ya ratsa ɗakin.
“Meyasa Abbas yake son tarwatsa mune?." Sai ga Abbas ya shigo.
“Abbas ya wuce su ɗauke ka a mai wanke mota, ni dai gaskiya ban yadda ba da kai zamu.” sai Abbas ya yi murmushi sannan ya dafa kafaɗar Shamo ya ce.
“Karka damu mutumina, muna tare har abada, kawai zan ci gaba da aikin hannuna kawai.” haka suka jima suna bashi baki amma ina ya kafe sosai. Daga haka suka bar maganar.
Haka dai rayuwa ta ɗan fara gangarawa suna shirin exam, Mymoon na ta narka ma I.B kuɗi masu yawa har sun siya filaye huɗu duk da sunansa sannan a cikin ɓakin ta zuba kuɗaɗen kaman yaƙi.
“Mymoon, ina kike kai kuɗi ne, kashe kuɗin ya yi waya." Dad ya faɗa yana kallon Mymoon da ta haɗe rai.
“Dad, bansan ya kake so na yi ba, shike nan na dena ta ɓa komai a ciki shike nan.”
“Ni bance, domin kuwa duk dukiyata na kune ke da Taj......” sai ta miƙe.
“Dad wani Taj ɗin?, Ta ya kuɗin ka ya zama na sa, ohhhh na gane.” daga haka ta bar Dining ɗin, girgiza kai ya yi yana kallon Mom da ke cin arish ya ce.
“Yarinyar nan duk ta sauya, bansan me ya shiga kanta ba sam, kallona take tana mai faɗa min magana.”
“To Ni Dad me zance, ba ka son Ina mata faɗa, ga kuma lokacin yin faɗan ya yi amma ba ka saba ma ta ba." Sai suka yi shuru.
“Hmmm duk me ke kanta zan sauke ma shi, Taj zan kira ya shigo ƙasar nan domin aurensu, in na mata auren sai na ga ƙaryan tsiya.” murmushi Mom ta yi tana faɗin.
“Ban shiga tsakanin ku, zan iya jin kunya nan gaba.” sai shima ya yi murmushi.
*** Dariya ta yi sosai dan jin abin da Abdul ya ce.
“Kai Honey, yanzu dai mubar wannan zancen, nawa ne kuɗin da kake buƙata.”
“Uhmmm 500k ne haka.”
“Shike nan karka damu, zuwa gobe za ka ji saƙon.” sai ta miƙe daga kan gadonta tana kuma cewa.
“Zan yi ma Uncle magana, yanzu dai da mun kammala exam sai tafiya.” hira suka sha sosai sannan ta kashe wayan.
*KANO*
_Haidar_
Yana isa haraban gidan tv na GOODNESS TV, ya riske mutane duk sun shirya, har Bus ɗin ɗaukarsu ta iso. Hatta Ameeratulkhair an ba ta I.d card, daga in da yake ya ke karantar natsuwarta, a takure take sosai dan ta kasa sakin jiki, kamar dai kullum irin wannan shigar ta yi. Sun jima sai Haidar ya kira Sir Abubakar, jin abin da ya ce aikam ya ce.
“Duk mu tafi, C.E.O ba zai shigo da wuri ba.” da mamakin take kallon mutanen dake shiga dan a ƙalla sun kai kusan 15 haka. Sai ta saki ranta dan ta za ci ita da Haidar kawai za su.
A layin na uku ta zauna sannan mota ta hau titi, take Haidar ya dawo kusa da ita yana faɗin.
“Fatan ban takura ki ba?.”